< 1 Peter 2 >
1 Zatorej dajte na stran vso zlobnost in vso zvijačo in hinavščine in nevoščljivosti in vsa hudobna govorjenja,
Saboda haka, ku rabu da kowace ƙeta da dukan ruɗu, munafunci, kishi, da kuma kowace irin ɓata suna.
2 kot novorojeni otročiči si želite pristnega mleka besede, da boste s tem lahko rastli;
Kamar sababbin jarirai, ku yi marmarin madara zalla ta ruhaniya, domin ta wurinta za ku yi girma cikin cetonku,
3 če je tako, ste okusili, da je Gospod milostljiv.
yanzu da kuka ɗanɗana alherin Ubangiji.
4 H kateremu prihajajte kakor k živemu kamnu, zares zavrnjenemu od ljudi, toda od Boga izbranemu in dragocenemu.
Da kuka zo gare shi, rayayyen Dutse, da mutane suka ƙi amma Allah ya zaɓa, kuma mai daraja a gare shi
5 Tudi vi ste kot živi kamni, vgrajeni [v] duhovno hišo, sveto duhovništvo, da darujete duhovne žrtve, po Jezusu Kristusu sprejemljive Bogu.
ku ma, a matsayinku na duwatsu masu rai, ana gina ku ga zama gidan ruhaniya don ku zama tsattsarkar ƙungiyar firistoci, kuna miƙa hadayun ruhaniya, abin karɓa ga Allah ta wurin Yesu Kiristi.
6 Zatorej je tudi vsebovano v pismu: »Glej, na Sionu položim glavni vogalni kamen, izvoljen, dragocen, in kdor veruje vanj, ne bo zbegan.«
Gama a cikin Nassi an ce, “Ga shi, na kafa dutse a Sihiyona, zaɓaɓɓen dutse na kusurwar gini mai daraja, wanda kuma ya dogara gare shi ba zai taɓa kunyata ba.”
7 Vam torej, ki verujete, je dragocen; toda tem, ki so neposlušni, je kamen, ki so ga graditelji zavrnili, ta isti postal glava vogalu
A gare ku da kuka gaskata, wannan dutse mai daraja ne. Amma ga waɗanda ba su gaskata ba, “Dutsen da magina suka ƙi ya zama dutsen kusurwar gini,
8 in kamen spotike in skala pohujšanja, celó tem, ki se spotikajo ob besedo, ki so neposlušni; za kar so bili tudi določeni.
kuma, “Dutse ne da yake sa mutane tuntuɓe kuma fā ne da yake sa su fāɗi.” Sun yi tuntuɓe domin sun ƙi su yi biyayya da saƙon, wanda kuma yake abin da aka ƙaddara musu.
9 Toda vi ste izbran rod, kraljevo duhovništvo, svet narod, posebni ljudje; da naj bi naznanjali hvale tistega, ki vas je iz teme poklical v svojo čudovito svetlobo;
Amma ku zaɓaɓɓu ne, ƙungiyar firistocin babban Sarki, al’umma mai tsarki, jama’a mallakar Allah, domin ku shaida yabon shi wanda ya kira ku daga cikin duhu zuwa haskensa mai banmamaki.
10 ki v preteklem času niste bili ljudstvo, toda sedaj ste Božje ljudstvo; ki niste dosegli usmiljenja, toda sedaj ste usmiljenje dosegli.
Dā ku ba mutane ba ne, amma yanzu ku mutanen Allah ne; Dā ba ku karɓi jinƙai ba, amma yanzu kun karɓi jinƙai.
11 Srčno ljubljeni, rotim vas kot tujce in romarje; vzdržite se pred mesenimi poželenji, ki se bojujejo zoper dušo;
Abokaina ƙaunatattu, ina roƙonku, a matsayin bare da kuma baƙi a duniya, ku rabu da sha’awace-sha’awacen zunubin da suke yaƙi da ranku.
12 imejte svoje vedênje iskreno med pogani, da bodo, medtem ko govorijo proti vam kot hudodelcem, lahko po vaših dobrih delih, ki jih bodo gledali, na dan obiskanja proslavili Boga.
Ku yi irin rayuwa mai kyau a cikin masu bautar gumaka, yadda ko da sun zarge ku da yin laifi, za su iya ganin ayyukanku nagari, su ɗaukaka Allah a ranar da zai ziyarce mu.
13 Zaradi Gospoda se podredite vsaki človeški odredbi; bodisi je to kralj, kot najvišji,
Saboda Ubangiji, ku yi biyayya ga kowace hukumar da aka kafa cikin mutane, ko ga sarki, a matsayi wanda ya fi iko,
14 bodisi voditeljem, kot tistim, ki so po njem poslani za kaznovanje hudodelcev in za hvalo teh, ki delajo dobro.
ko ga gwamnoni, waɗanda ya aika domin su hukunta masu laifi su kuma yabi masu aikata abin da yake daidai.
15 Kajti taka je Božja volja, da boste s počenjanjem dobrega lahko utišali nevednost nespametnih ljudi.
Gama nufin Allah ne cewa ta wurin yin nagarta za ku toshe jahilcin marasa azanci.
16 Kot svobodni, pa svoje svobode ne uporabljajte za ogrinjalo zlonamernosti, temveč kakor Božji služabniki.
Ku yi rayuwa kamar mutanen da aka’yantar, sai dai kada ku yi amfani da’yancinku a matsayin hujjar aikata mugunta; ku yi rayuwa kamar bayin Allah.
17 Spoštujte vse ljudi. Ljubite bratstvo. Bojte se Boga. Spoštujte kralja.
Ku nuna ladabin da ya dace ga kowa. Ku ƙaunaci’yan’uwantakar masu bi, ku ji tsoron Allah, ku girmama sarki.
18 Služabniki, z vsem strahom bodite podrejeni svojim gospodarjem; ne samo dobrim in blagim, temveč tudi osornim.
Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku da matuƙar ladabi, ba kawai ga waɗanda suke da kirki da masu sauƙinkai ba, amma har ga masu zafin rai ma.
19 Kajti vredno hvale je to, če človek, ki krivično trpi zaradi zavedanja pred Bogom, prenaša žalost.
Gama abin yabo ne in mutum ya yi haƙuri cikin zafin wahalar rashin adalci saboda yana sane da Allah.
20 Kajti kakšna čast je to, če boste, ko ste oklofutani zaradi svojih napak, to potrpežljivo prestali? Toda ko delate dobro in zaradi tega trpite, če to potrpežljivo prestanete, je to sprejemljivo pri Bogu.
Amma ina abin taƙama in kuka sha duka saboda kun yi laifi kuka kuma jimre? Sai dai in kuka sha wahala saboda yin nagari kuka kuma jimre, abin yabo ne a gaban Allah.
21 Kajti celó k temu ste bili poklicani, ker je tudi Kristus trpel za nas in nam pustil zgled, da naj bi vi sledili njegovim stopinjam;
Ga wannan ne aka kira ku, domin Kiristi ya sha wahala dominku, ya bar muku gurbin da ya kamata ku bi.
22 ki ni storil greha niti v njegovih ustih ni bilo najti zvijače;
“Bai taɓa yin laifi ba sam, ba a kuma sami ƙarya a bakinsa ba.”
23 ki ni ponovno zasramoval, ko je bil zasramovan; ko je trpel, ni grozil; temveč je sebe izročil njemu, ki sodi pravično;
Sa’ad da suka zazzage shi, bai rama ba; sa’ad da ya sha wahala, bai yi barazana ba. A maimakon haka, ya miƙa kansa ga wanda yake shari’ar adalci.
24 ki je sam, v svojem lastnem telesu, naše grehe ponesel na les, da naj bi mi, mrtvi grehom, lahko živeli v pravičnosti; s čigar udarci z bičem ste bili ozdravljeni.
Shi kansa ya ɗauki zunubanmu a jikinsa a kan itace, domin mu mutu ga zunubai mu kuma rayu ga adalci; ta wurin raunukansa ne kuka sami warkarwa.
25 Kajti bili ste kakor ovce, ki so zašle, toda sedaj ste vrnjeni k Pastirju in duhovnemu Nadzorniku svojih duš.
Gama dā kuna kama da tumakin da suka ɓace, amma yanzu kun dawo ga Makiyayi da kuma Mai lura da rayukanku.