< 1 Kralji 9 >

1 Pripetilo se je, ko je Salomon dokončal gradnjo Gospodove hiše, kraljeve hiše in vsega, kar je Salomon želel, kar mu je ugajalo storiti,
Sa’ad da Solomon ya gama ginin haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki, ya kuma yi dukan abin da yake so yă yi,
2 da se je Gospod drugič prikazal Salomonu, kakor se mu je prikazal pri Gibeónu.
sai Ubangiji ya bayyana gare shi sau na biyu, kamar yadda ya bayyana masa a Gibeyon.
3 Gospod mu je rekel: »Slišal sem tvojo molitev in tvojo ponižno prošnjo, ki si jo storil pred menoj. Jaz sem posvetil to hišo, ki si jo zgradil, da tja na veke postavim svoje ime in moje oči in moje srce bodo neprestano tam.
Ubangiji ya ce masa, “Na ji addu’arka da kuma roƙon da ka yi a gabana; na tsarkake wannan haikali wanda ka gina, ta wurinsa Sunana zai kasance a can har abada. Idanuna da zuciyata kullum za su kasance a can.
4 Če boš hodil pred menoj, kakor je hodil tvoj oče David, v neokrnjenosti srca in v poštenosti, da storiš glede na vse, kar sem ti zapovedal in da boš ohranjal moje zakone in moje sodbe,
“Kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana da mutunci a zuci da kuma gaskiya, kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka yi dukan abin da na umarta, ka kuma yi biyayya da ƙa’idodina da kuma dokokina,
5 potem bom na veke utrdil prestol tvojega kraljestva nad Izraelom, kakor sem obljubil tvojemu očetu Davidu, rekoč: ›Ne bo ti manjkal mož na Izraelovem prestolu.‹
zan kafa kujerar sarautarka a bisa Isra’ila har abada, kamar yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani a kan kujerar sarautar Isra’ila ba.’
6 Toda če se boste obrnili od sledenja meni, vi ali vaši otroci in ne boste ohranjali mojih zapovedi in mojih zakonov, ki sem jih postavil pred vas, temveč boste šli in služili drugim bogovom in jih oboževali,
“Amma in kai, ko’ya’yanka maza, suka juye daga gare ni, ba ku kuma kiyaye umarnai da ƙa’idodin da na ba ku ba, kuka yi gaba, kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka kuma yi musu sujada,
7 potem bom Izraela odsekal iz dežele, ki sem jim jo dal in to hišo, ki sem jo posvetil za svoje ime, bom vrgel iz svojega pogleda in Izrael bo med vsemi ljudstvi pregovor in tarča posmeha.
sai in yanke mutanen Isra’ila daga ƙasar da na ba su, in kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Isra’ila kuwa za tă zama abin gori da abin dariya a cikin dukan mutane.
8 In ob tej hiši, ki je visoka, bo vsak, kdor gre mimo nje, osupel in bo sikal. Rekli bodo: ›Zakaj je Gospod tako storil tej deželi in tej hiši?‹
Wannan haikali zai zama tarin juji. Duk wanda ya wuce ta hanyan nan kuwa zai ji tausayi, yă kuma yi tsaki yana cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka ga wannan ƙasa da kuma wannan haikali?’
9 Odgovorili bodo: ›Ker so zapustili Gospoda, svojega Boga, ki je njihove očete privedel ven iz egiptovske dežele in so se oprijeli drugih bogov, jih oboževali in jim služili, zato je Gospod nadnje privedel vse to zlo.‹
Mutane za su amsa su ce, ‘Saboda sun yashe Ubangiji Allahnsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna yin musu sujada, suna bauta musu ne, ya sa Ubangiji ya kawo dukan masifan nan a kansu.’”
10 Pripetilo se je ob koncu dvajsetih let, ko je Salomon zgradil dve hiši, Gospodovo hišo in kraljevo hišo,
A ƙarshen shekaru ashirin da Solomon ya ɗauka yana gina haikalin Ubangiji da fadan sarki,
11 ( torej tirski kralj Hirám je Salomona opremil s cedrovim lesom, cipresovim lesom in z zlatom, glede na vso njegovo željo) da je nató kralj Salomon Hirámu dal dvajset mest v galilejski deželi.
sai Sarki Solomon ya ba wa Hiram sarkin Taya garuruwa ashirin a yankin Galili, gama Hiram ya tanada masa da dukan katakai al’ul da na fir, da kuma zinariyar da ya bukaci domin aiki.
12 Hirám je prišel iz Tira, da bi videl mesta, ki mu jih je Salomon dal. Le-ta pa mu niso ugajala.
Amma sa’ad da Hiram ya zo daga Taya don yă ga garuruwan da Solomon ya ba shi, sai bai ji daɗi ba.
13 Rekel je: »Kakšna so ta mesta, ki si mi jih dal, moj brat?« Imenoval jih je dežela Kabúl do tega dne.
Sai ya ce, “Wanda irin garuruwa ke nan ka ba ni, ɗan’uwana?” Saboda haka ya kira su Ƙasar Kabul, sunan da suke da shi har wa yau.
14 Hirám je poslal h kralju sto dvajset talentov zlata.
Hiram kuwa ya aika wa sarki talenti 120 na zinariya.
15 In to je razlog dajatve obveznega dela, ki ga je dvignil kralj Salomon, da zgradi Gospodovo hišo, svojo lastno hišo, Miló, jeruzalemsko obzidje, Hacór, Megído in Gezer.
Ga lissafin ma’aikatan gandun da Sarki Solomon ya ɗauka don ginin haikalin Ubangiji, da fadarsa, da madogaran gini, da katangar Urushalima, da kuma Hazor Megiddo da Gezer.
16 Kajti faraon, egiptovski kralj, je odšel gor, zavzel Gezer, ga požgal z ognjem in umoril Kánaance, ki so prebivali v mestu in ga dal za darilo svoji hčeri, Salomonovi ženi.
(Fir’auna sarkin Masar ya kai wa Gezer hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Ya sa mata wuta, ya kashe Kan’aniyawanta mazaunan wurin, ya kuma ba da ita a matsayin kyautar aure ga’yarsa, matar Solomon.
17 Salomon je zgradil Gezer, spodnji Bet Horón,
Solomon kuwa ya sāke gina Gezer.) Ya gina Bet-Horon ta Kwari,
18 Baalát, Tadmór v divjini, v deželi
da Ba’alat, da Tadmor a hamada, na cikin ƙasarsa.
19 in vsa skladiščna mesta, ki jih je imel Salomon in mesta za njegove bojne vozove in mesta za njegove konjenike in to, kar je Salomon želel, da zgradi v Jeruzalemu, na Libanonu in po vsej deželi svojega gospostva.
Haka kuma ya gina dukan biranen ajiyarsa, da garuruwa domin kekunan yaƙinsa, da garuruwa domin dawakansa. Ya gina duk abin da ya so yă ginawa a Urushalima, da Lebanon, da kuma ko’ina a dukan yankin da ya yi mulki.
20 Na vse ljudstvo, ki je preostalo od Amoréjcev, Hetejcev, Perizéjcev, Hivéjcev in Jebusejcev, ki niso bili od Izraelovih otrok,
Dukan Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa da Yebusiyawan da suka ragu a ƙasar (waɗanda ba Isra’ilawa ba ne),
21 na njihove otroke, ki so za njimi preostali v deželi, ki jih Izraelovi otroci niso mogli popolnoma uničiti, je Salomon naložil dajatev davka prisilnega dela do tega dne.
wato, waɗanda suka ragu a ƙasar, waɗanda Isra’ilawa ba su iya hallakawa ba, su ne Solomon ya ɗauka su zama bayinsa don aikin gandu, kamar yadda yake har wa yau.
22 Toda izmed Izraelovih otrok Salomon ni naredil nobenega sužnja, temveč so bili bojevniki, njegovi služabniki, njegovi princi, njegovi poveljniki, vodje njegovih bojnih voz in njegovi konjeniki.
Amma Solomon bai mai da Isra’ilawa bayi ba; su ne mayaƙansa, shugabannin gwamnatinsa, dogarawansa, shugabannin sojojinsa, da shugabanninsa na kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙinsa.
23 Ti so bili glavni častniki, ki so bili nad Salomonovim delom, petsto petdeset, ki so nadzorovali ljudstvo, ki je opravljalo delo.
Su ne kuma manyan shugabanni masu lura da ayyukan Solomon, su ne shugabanni 550 masu lura da mutanen da suke aiki.
24 Toda faraonova hči je prišla gor iz Davidovega mesta k svoji hiši, ki jo je Salomon zgradil zanjo. Potem je zgradil Miló.
Bayan’yar Fir’auna ta haura daga Birnin Dawuda zuwa fadan da Solomon ya gina mata, sai ya gina madogaran gini.
25 Trikrat na leto je Salomon daroval žgalne daritve in mirovne daritve na oltarju, ki ga je zgradil Gospodu in zažgal je kadilo na oltarju, ki je bil pred Gospodom. Tako je dokončal hišo.
Sau uku a shekara Solomon kan miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama a kan bagaden da ya gina wa Ubangiji, yana ƙone turare a gaban Ubangiji haɗe da su, ta haka ya cika abin da ake bukata na haikali.
26 Kralj Salomon je naredil floto ladij v Ecjón Geberju, ki je poleg Elota, na obali Rdečega morja, v edómski deželi.
Sarki Solomon ya kuma gina jiragen ruwa a Eziyon Geber, wadda take kusa da Elot a Edom, a bakin Jan Teku.
27 Hirám je s Salomonovimi služabniki poslal v floto svoje služabnike, pomorščake, ki so imeli znanje o morju.
Hiram kuwa ya aiki mutanensa, masu tuƙan jirgin ruwa waɗanda suka san teku, don su yi hidima a jerin jiragen ruwa tare da mutanen Solomon.
28 Prišli so do Ofírja in od tam vzeli zlato, štiristo dvajset talentov in to prinesli h kralju Salomonu.
Suka tafi Ofir suka kuma dawo da talenti 420 na zinariya, wanda suka ba wa Sarki Solomon.

< 1 Kralji 9 >