< 1 Kroniška 14 >
1 Torej kralj Hirám iz Tira je poslal poslance k Davidu in cedrov les z zidarji in tesarji, da mu zgradijo hišo.
To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
2 David je zaznal, da ga je Gospod potrdil za kralja nad Izraelom, kajti njegovo kraljestvo je bilo visoko povzdignjeno zaradi njegovega ljudstva Izraela.
Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
3 David si je v Jeruzalemu vzel več žena in David je zaplodil več sinov in hčera.
A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin’ya’yan maza da mata.
4 Torej to so imena njegovih otrok, ki jih je imel v Jeruzalemu: Šamúa, Šobáb, Natán, Salomon,
Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
5 Jibhár, Elišúa, Elpélet,
Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
7 Elišamá, Beeljadá in Elifálet.
Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
8 Ko so Filistejci slišali, da je bil David maziljen za kralja nad vsem Izraelom, so vsi Filistejci odšli gor, da poiščejo Davida. David pa je slišal o tem in odšel ven zoper njih.
Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
9 Filistejci so prišli in se razporedili po dolini Rafájim.
To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
10 David je poizvedel od Boga, rekoč: »Ali naj grem gor zoper Filistejce? Ali jih boš izročil v mojo roko?« Gospod mu je rekel: »Pojdi gor, kajti izročil jih bom v tvojo roko.«
sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ka tafi, zan ba da su gare ka.”
11 Tako so prišli gor v Báal Peracím in David jih je tam udaril. Potem je David rekel: »Bog je po moji roki pridrl nad moje sovražnike, kakor izbruhnejo vode, « zato so ime tega kraja imenovali Báal Peracím.
Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
12 Ko so tam pustili svoje bogove, je David dal zapoved in sežgali so jih v ognju.
Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
13 Filistejci pa so se ponovno razporedili po dolini.
Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
14 Zato je David ponovno poizvedel od Boga in Bog mu je rekel: »Ne pojdi gor za njimi. Obrni se proč od njih in pridi nadnje nasproti murvinih dreves.
sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
15 Zgodilo se bo, ko boš zaslišal zvok hoje po vrhovih murvinih dreves, da boš tedaj odšel ven na bitko, kajti Bog je šel naprej pred teboj, da udari vojsko Filistejcev.«
Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
16 David je torej storil, kakor mu je Bog zapovedal in udarili so vojsko Filistejcev od Gibeóna, celo do Gazerja.
Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
17 Davidova slava se je razširila po vseh deželah in Gospod je nad vse narode privedel strah pred njim.
Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.