< Псалтирь 106 >
1 Исповедайтеся Господеви, яко благ, яко в век милость Его.
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Кто возглаголет силы Господни, слышаны сотворит вся хвалы Его?
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 Блажени хранящии суд и творящии правду во всякое время.
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 Помяни нас, Господи, во благоволении людий Твоих, посети нас спасением Твоим,
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 видети во благости избранныя Твоя, возвеселитися в веселии языка Твоего, хвалитися с достоянием Твоим.
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 Согрешихом со отцы нашими, беззаконновахом, неправдовахом:
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 отцы наши во Египте не разумеша чудес Твоих, ни помянуша множества милости Твоея: и преогорчиша восходяще в Чермное море.
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 И спасе их имене Своего ради, сказати силу Свою:
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 и запрети Чермному морю, и изсяче: и настави я в бездне яко в пустыни.
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 И спасе я из руки ненавидящих и избави я из руки врагов.
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 Покры вода стужающыя им: ни един от них избысть.
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 И вероваша словеси Его и воспеша хвалу Его.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 Ускориша, забыша дела Его, не стерпеша совета Его:
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 и похотеша желанию в пустыни и искусиша Бога в безводней.
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 И даде им прошение их, посла сытость в душы их.
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 И прогневаша Моисеа в стану, Аарона святаго Господня.
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 Отверзеся земля и пожре Дафана и покры на сонмищи Авирона:
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 и разжжеся огнь в сонме их, пламень попали грешники.
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 И сотвориша телца в Хориве и поклонишася истуканному:
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 и измениша славу Его в подобие телца ядущаго траву.
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21 И забыша Бога спасающаго их, сотворшаго велия во Египте,
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 чудеса в земли Хамове, страшная в мори Чермнем.
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 И рече потребити их, аще не бы Моисей избранный Его стал в сокрушении пред Ним, возвратити ярость Его, да не погубит их.
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24 И уничижиша землю желанную, не яша веры словеси Его:
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 и поропташа в селениих своих, не услышаша гласа Господня.
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 И воздвиже руку Свою на ня, низложити я в пустыни,
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 и низложити семя их во языцех, и расточити я в страны.
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 И причастишася Веельфегору и снедоша жертвы мертвых:
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 и раздражиша Его в начинаниих своих, и умножися в них падение.
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 И ста Финеес и умилостиви, и преста сечь:
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 и вменися ему в правду, в род и род до века.
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 И прогневаша Его на воде Пререкания, и озлоблен бысть Моисей их ради:
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 яко преогорчиша дух его и разнствова устнама своима.
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 Не потребиша языки, яже рече Господь им.
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 И смесишася во языцех и навыкоша делом их:
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36 и поработаша истуканным их, и бысть им в соблазн.
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37 И пожроша сыны своя и дщери своя бесовом,
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 и пролияша кровь неповинную, кровь сынов своих и дщерей, яже пожроша истуканным Ханаанским: и убиена бысть земля их кровьми
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 и осквернися в делех их: и соблудиша в начинаниих своих.
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 И разгневася яростию Господь на люди Своя и омерзи достояние Свое:
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 и предаде я в руки врагов, и обладаша ими ненавидящии их.
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 И стужиша им врази их: и смиришася под руками их.
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 Множицею избави я: тии же преогорчиша Его советом своим, и смиришася в беззакониих своих.
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 И виде Господь, внегда скорбети им, внегда услышаше моление их:
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 и помяну завет Свой, и раскаяся по множеству милости Своея:
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 и даде я в щедроты пред всеми пленившими я.
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 Спаси ны, Господи, Боже наш, и собери ны от язык, исповедатися имени Твоему святому, хвалитися во хвале Твоей.
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 Благословен Господь Бог Израилев от века и до века. И рекут вси людие: буди, буди.
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.