< Книга пророка Иеремии 38 >

1 И слыша Сафаниа сын Нафань и Годолиа сын Пасхоров, и Иоахал сын Селемиин и Фасхор сын Мелхиев словеса, яже Иеремиа глагола ко всем людем, глаголя:
Shefatiya ɗan Mattan, Gedaliya ɗan Fashhur, Yukal ɗan Shelemiya da Fashhur ɗan Malkiya ya ji abin da Irmiya yana faɗa wa dukan mutane sa’ad da ya ce,
2 тако рече Господь: седяй во граде сем умрет мечем и гладом и мором, исходяй же ко Халдеем жив будет, и будет душа его на обретение, и жив будет.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba, amma duk wanda ya je wurin Babiloniyawa zai rayu. Zai tsira da ransa, ya rayu.’
3 Яко тако рече Господь: преданием предастся град сей в руце силы царя Вавилонска, и возмет его.
Kuma ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Tabbatacce za a ba da wannan birni ga sojojin sarkin Babilon, wanda zai ci shi.’”
4 И рекоша царю: да умрет человек той, яко сей разслабляет руце мужей воюющих оставшихся во граде и руки всех людий, глаголя к ним по словесем сим: яко человек сей не проповедает людем сим мира, но токмо злая.
Sai fadawa suka ce wa sarki, “Ya kamata a kashe wannan mutum. Yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran mutane, ta wurin abubuwan da yake faɗa musu. Wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan sai dai wahala.”
5 И рече царь Седекиа: се, той в руках ваших. Понеже не можаше царь противу им.
“Yana a hannuwanku” Sarki Zedekiya ya amsa. “Sarki ba zai iya yin kome ya hana ku ba.”
6 И взяша Иеремию и ввергоша его в ров Мелхиин, сына царева, иже бяше во дворе темничнем: и свесиша его ужами в ров, в рове же не бяше воды, но тина, и бяше в тине Иеремиа.
Saboda haka suka kama Irmiya suka sa a rijiyar da ba ruwa a ciki ta Malkiya, ɗan sarki, wadda take a sansanin matsara. Suka saukar da Irmiya cikin rijiyar da ba ruwa da igiya; babu ruwa a cikinta, sai laka, Irmiya ya nutse cikin laka.
7 И слыша Авдемелех Мурин, и той бяше во дворе цареве, яко ввергоша Иеремию в ров: царь же (в той час) седяше во вратех Вениаминих.
Amma Ebed-Melek mutumin Kush, wani hafsa a fada, ya ji cewa sun sa Irmiya a rijiyar da ba ruwa. Yayinda sarki yana zama a Ƙofar Benyamin,
8 И изыде Авдемелех от дому царева и рече ко царю глаголя:
Ebed-Melek ya fita daga fadar ya ce masa,
9 злосотворил еси, яже сотворил еси, убивая человека сего от лица глада, яко несть хлеба во граде ктому.
“Ranka yă daɗe sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu a duk abin da suka yi wa Irmiya annabi. Sun jefa shi cikin rijiyar da ba ruwa, inda zai mutu da yunwa gama ba sauran wani burodi a birnin.”
10 И повеле царь Авдемелеху, глаголя: поими с собою отсюду тридесять мужей и извлецы Иеремию из рова, да не умрет.
Sai sarki ya umarce Ebed-Melek mutumin Kush, “Ka ɗauko mutane talatin daga nan ku fid da Irmiya annabi daga rijiyar kafin ya mutu.”
11 И поят Авдемелех мужы, и прииде в дом царев подземный, и взя оттуду ветхи порты и ветхия ужы, и вверже я ко Иеремии в ров, и рече к нему:
Saboda haka Ebed-Melek ya ɗauki mutane tare da shi suka shiga ɗaki a ƙarƙashin baitulmali a cikin fada. Ya ɗauko waɗansu tsofaffin tsummoki da tsofaffi riguna daga can ya kuma zurara su da igiya wa Irmiya a cikin rijiyar.
12 положи сия под ужы. И сотвори Иеремиа сице.
Ebed-Melek mutumin Kush ya ce wa Irmiya, “Ka sa waɗannan tsummoki da tsofaffin rigunan a hammatarka, ya zarga igiya.” Irmiya ya yi haka,
13 И извлекоша его ужами и изяша его из рова. И седе Иеремиа во дворе темничнем.
suka kuma ja shi sama da igiya suka fid da shi daga rijiyar. Irmiya kuwa ya zauna a sansanin matsara.
14 И посла царь, и призва к себе Иеремию в дом Аселисиль, иже в дому Господни. И рече ему царь: вопрошаю тя словесе (единаго), и не утай от мене словесе.
Sai Sarki Zedekiya ya aika a kawo Irmiya annabi, ya sa aka kawo shi a ƙofa ta uku ta haikalin Ubangiji. Sai sarki ya ce wa Irmiya, “Zan tambaye ka wani abu, kada ka ɓoye mini wani abu.”
15 И рече Иеремиа царю: аще повем ти, то не смертию ли умориши мя? И аще совещаю ти, то не послушаеши мене.
Irmiya ya ce wa Zedekiya, “In na ba ka amsa, ba za ka kashe ni ba? Ko da na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba.”
16 И клятся ему царь, глаголя: жив Господь, иже сотвори нам душу сию, аще убию тя и аще предам тя в руце человек сих ищущих души твоея (на смерть).
Amma Sarki Zedekiya ya yi wannan rantsuwa a kaɗaice ga Irmiya cewa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya ba mu numfashi, ba zan kashe ka ko in ba da kai ga waɗanda suke neman ranka ba.”
17 И рече ему Иеремиа: тако рече Господь Сил, Бог Израилев: аще изыдый изыдеши к воеводам царя Вавилонска, жива будет душа твоя, и град сей не пожжется огнем, и жив будеши ты и дом твой:
Sa’an nan Irmiya ya ce wa Zedekiya, “Ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon, za a bar ka da rai ba za a kuma ƙone wannan birni ba; da kai da iyalinka za ku rayu.
18 аще же не изыдеши ко князем царя Вавилонска, предастся град сей в руце Халдейсте, и пожгут его огнем, и ты не спасешися от руки их.
Amma in ba ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon ba, za a ba da wannan birni ga Babiloniyawa za su kuma cinna mata wuta; kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba.’”
19 И рече царь Иеремии: аз опасение имам от Иудеев избежавших ко Халдеем, да не предадут мя (Халдее) в руце их, и поругаются ми.
Sarki Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawan da suka tafi wurin Babiloniyawa, gama Babiloniyawa mai yiwuwa su ba da ni gare su su kuma wulaƙanta ni.”
20 И рече Иеремиа: не предадят тебе: послушай убо словесе Господня, еже аз глаголю тебе, и лучше ти будет, и жива будет душа твоя:
Irmiya ya ce, “Ba za su ba da kai ba, ka yi biyayya ga Ubangiji ta wurin yin abin da na faɗa maka. Ta haka zai zama maka da amfani, za ka kuwa rayu.
21 и аще не восхощеши ты изыти, сие слово, еже сказа мне Господь:
Amma in ka ƙi miƙa wuya, ga abin da Ubangiji ya bayyana mini.
22 и се, вся жены, оставшыяся в дому царя Иудина, изведутся ко князем царя Вавилонска: и тыя глаголаху: прельстиша тя и премогоша тя мужие мирницы твои, и ослабиша во поползновениих ногу твою и отвратишася от тебе:
Za a fitar da dukan matan da suka ragu a fadan sarkin Yahuda wa hafsoshin sarkin Babilon. Waɗannan mata za su ce maka, “‘Sun ruɗe ka suka kuma rinjaye ka, waɗannan abokanka. Ƙafafunka sun nutse a cikin laka; abokanka sun yashe ka.’
23 и жены твоя и чада твоя изведут ко Халдеем, и ты не уцелееши, яко рукою царя Вавилонска ят будеши, и град сей пожжется.
“Za a kawo dukan matanka da’ya’yanka wa Babiloniyawa. Kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba amma za su sa sarkin Babilon zai kama ka; za a kuma ƙone wannan birni.”
24 И рече ему царь: человек да не увесть словес сих, и да не умреши ты.
Sai Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan zance, in ba haka ba za ka mutu.
25 И аще услышат князи, яко глаголах с тобою, и приидут к тебе и рекут ти: повеждь нам, что глагола к тебе царь? Не утай от нас, и не убием тебе: и что глагола к тебе царь?
In fadawa suka ji cewa na yi magana da kai, suka kuma zo wurinka suka ce, ‘Faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da kuma abin da sarki ya faɗa maka; kada ka ɓoye mana, in ba haka za mu kashe ka,’
26 И речеши им: повергох аз моление мое пред лицем царевым, яко да не возвратит мене в дом Ионафань, умрети ми тамо.
sai ka ce musu cewa, ‘Na roƙi sarki kada yă mai da ni gidan Yonatan in mutu a can.’”
27 И приидоша вси князи ко Иеремии и вопросиша его. И поведа им по всем словесем сим, яже заповеда ему царь. И умолкнуша, яко несть слышано слово господне.
Dukan fadawa kuwa suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi, ya kuma faɗa musu dukan abin da sarki ya umarce shi ya faɗa. Saboda haka ba su ƙara ce masa kome ba, gama ba wanda ya ji zance da suka yi da sarki.
28 И седяше Иеремиа во дворе темничнем, дондеже взяша Иерусалим.
Irmiya kuwa ya zauna a sansanin masu gadi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi. Ga yadda aka ci Urushalima,

< Книга пророка Иеремии 38 >