< Книга пророка Исаии 62 >

1 Сиона ради не умолчу и Иерусалима ради не попущу, дондеже изыдет яко свет правда моя, и спасение мое яко светило разжжется.
Saboda Sihiyona ba zan yi shiru ba, saboda Urushalima ba zan huta ba, sai adalcinta ya haskaka kamar hasken safiya, cetonta kuma ya haskaka kamar fitila mai haske.
2 И узрят языцы правду твою, и царие славу твою, и прозовут тя именем новым, имже Господь наименует е.
Al’ummai za su ga adalcinki, sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki; za a kira ki da sabon suna sunan da bakin Ubangiji zai ambata.
3 И будеши венец доброты в руце Господни и диадима царствия в руце Бога твоего:
Za ki zama rawanin daraja a hannun Ubangiji, rawanin sarauta a hannun Allahnki.
4 и не прозовешися ктому оставлен, и земля твоя ктому не наречется пуста: тебе бо прозовется воля Моя, и земля твоя вселенная, яко благоволи Господь в тебе, и земля твоя вкупе населится.
Ba za a ƙara ce da ke Yasasshiya ba, ko a kira ƙasarki Kango. Amma za a ce da ke Hefziba ƙasarki kuma Bewula; gama Ubangiji zai ji daɗinki, ƙasarki kuma za tă yi aure.
5 И якоже живяй юноша с девою, тако поживут сынове твои с тобою: и будет якоже радуется жених о невесте, тако возрадуется Господь о тебе.
Kamar yadda saurayi kan auri yarinya, haka’ya’yanki maza za su aure ki; kamar kuma yadda ango yakan yi farin ciki da amaryarsa, haka Allahnki zai yi farin ciki da ke.
6 И на стенах твоих, Иерусалиме, приставих стражы весь день и всю нощь, иже до конца не премолкнут поминающе Господа.
Na sa matsara a kan katangarki, ya Urushalima; ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Ku da kuke kira bisa sunan Ubangiji, kada ku ba kanku hutu,
7 Несть бо вам подобен: аще исправиши и сотвориши, Иерусалиме, радование на земли.
kuma kada ku ba shi hutu sai ya kafa Urushalima ya kuma mai da ita yabon duniya.
8 Клятся Господь десницею Своею и крепостию мышцы Своея: аще ктому отдам пшеницу твою и пищу твою врагом твоим, и аще ктому испиют вино твое сынове чуждии, о немже трудился еси:
Ubangiji ya rantse da hannunsa na dama ta hannunsa kuma mai iko cewa, “Ba zan ƙara ba da hatsinki ya zama abinci ga abokan gābanki ba, baƙi kuma ba za su ƙara shan ruwan inabin wanda kika sha wahala samu ba;
9 но собирающии снедят я и похвалят Господа, и оымающии испиют я во дворех святых Моих.
amma waɗanda suka girbe shi za su ci shi su kuma yabi Ubangiji, waɗanda kuma suka tattara’ya’yan inabi za su sha shi a filayen wurina mai tsarki.”
10 Идите враты Моими и путь сотворите людем Моим, и камение, еже на пути, размещите: воздвигните знамение на языки.
Ku wuce, ku wuce ƙofofi! Ku shirya hanya saboda mutane. Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku kawar da duwatsu. Ku ɗaga tuta saboda al’ummai.
11 Се бо, Господь слышано сотвори до последних земли: рцыте дщери Сионове: се, Спаситель твой грядет, имеяй с Собою мзду и дело Свое пред лицем Своим.
Ubangiji ya yi shela ga iyakokin duniya cewa, “Faɗa wa Diyar Sihiyona, ‘Ga Mai Cetonki yana zuwa! Ga ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa yana raka shi.’”
12 И прозовет я люди святы, избавлены Господем: ты же прозовешися взыскан град и не оставлен.
Za a ce da shi Tsattsarkar Mutane, Fansassu na Ubangiji; za a kuma ce da ke Wadda Aka Nema Birnin da Ba Za a Ƙara Yashe ta ba.

< Книга пророка Исаии 62 >