< Книга пророка Исаии 49 >

1 Послушайте Мене, острови, и внемлите, языцы. Временем многим стояти будет, глаголет Господь: от чрева матере Моея нарече имя Мое,
Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
2 и положи уста Моя яко мечь остр, и под кровом руки Своея скры Мя: положи Мя яко стрелу избранну, и в туле своем скры Мя,
Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
3 и рече Ми: раб Мой еси Ты, Израилю, и в Тебе прославлюся.
Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
4 Аз же рекох: вотще трудихся, всуе и ни во что дах крепость Мою: сего ради суд Мой пред Господем и труд Мой пред Богом Моим.
Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
5 И ныне тако глаголет Господь, создавый Мя от чрева раба Себе, еже собрати Иакова к Нему и Израиля: соберуся и прославлюся пред Господем, и Бог Мой будет Мне крепость.
Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
6 И рече Ми: велие Ти есть, еже назватися Тебе рабом Моим, еже возставити племена Иаковля и разсеяние Израилево обратити: се, дах Тя в завет рода, во свет языком, еже быти Тебе во спасение даже до последних земли.
ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
7 Тако глаголет Господь, Избавивый Тя Бог Израилев: освятите уничижающаго душу Свою, гнушаемаго от язык рабов княжеских: царие узрят Его, и востанут князи и поклонятся Ему Господа ради, яко верен есть Святый Израилев, и избрах Тя.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
8 Тако глаголет Господь: во время приятно послушах Тебе и в день спасения помогох Ти, и сотворих Тя и дах Тя в завет вечный языков, еже устроити землю и наследити наследия пустыни,
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
9 глаголюща сущым во узах: изыдите, и сущым во тме: открыйтеся. На всех путех пастися будут, и на всех стезях пажить их:
don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
10 не взалчут, ниже вжаждут, ниже поразит их зной, ниже солнце, но Милуяй их утешит их и сквозе источники водныя проведет их.
Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
11 И положу всяку гору в путь и всяку стезю в паству им.
Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
12 Се, сии издалеча приидут, сии от севера и от моря, инии же от земли Персския.
Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
13 Радуйтеся, небеса, и веселися, земле, да отрыгнут горы веселие и холми правду, яко помилова Бог люди Своя и смиренныя людий Своих утеши.
Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
14 Рече же Сион: остави мя Господь, и Бог забы мя.
Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
15 Еда забудет жена отроча свое, еже не помиловати изчадия чрева своего? Аще же и забудет сих жена, но Аз не забуду тебе, глаголет Господь.
“Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
16 Се, на руках Моих написах стены твоя, и предо Мною еси присно,
Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
17 и вскоре возградишися, от нихже разорился еси, и опустошившии тя изыдут из тебе.
’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
18 Возведи окрест очи твои и виждь вся, се, собрашася приидоша к тебе, живу Аз, глаголет Господь: яко всеми ими аки в красоту облечешися и обложиши себе ими яко утварию невеста.
Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
19 Понеже пустая твоя и разсыпаная и падшая ныне утеснеют от обитающих, и удалятся от тебе поглощающии тя.
“Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
20 Рекут бо во ушы твои сынове твои, ихже был погубил еси: тесно ми место, сотвори ми место, да вселюся.
’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
21 И речеши в сердцы своем: кто мне породи сих? Аз же безчадна и вдова, сих же кто воспита мне? Аз же остахся едина, сии же мне где быша?
Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
22 Тако глаголет Господь Господь: се, воздвизаю на языки руку Мою и на островы воздвигну знамение Мое, и приведут сыны твоя в лоне и дщери твоя на плещах возмут.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
23 И будут царие кормителие твои, и княгини их кормилицы твоя: до лица земли поклонятся тебе и прах ног твоих оближут, и увеси, яко Аз Господь Бог, и не посрамятся терпящии Мя.
Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
24 Еда возмет кто от исполина корысти? И аще кто пленит неправедне, спасетлися?
Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
25 Зане тако глаголет Господь: аще кто пленит исполина, возмет корысти: вземляй же от крепкаго спасется: Аз же прю твою разсужду и Аз сыны твоя избавлю:
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
26 и оскорбившии тебе снедят плоть свою и испиют яко вино ново кровь свою, и упиются: и увесть всяка плоть, яко Аз Господь Избавивый тя и заступаяй крепость Иаковлю.
Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”

< Книга пророка Исаии 49 >