< Книга пророка Исаии 11 >

1 И изыдет жезл из корене Иессеова, и цвет от корене его взыдет:
Toho zai fito daga kututturen Yesse; daga saiwarsa Reshe zai ba da’ya’ya.
2 и почиет на нем Дух Божий, дух премудрости и разума, дух совета и крепости, дух ведения и благочестия:
Ruhun Ubangiji zai kasance a kansa, Ruhun hikima da na fahimta, Ruhun shawara da na iko, Ruhun sani da na tsoron Ubangiji,
3 исполнит его дух страха Божия: не по славе судити имать, ниже по глаголанию обличит,
zai kuwa ji daɗin tsoron Ubangiji. Ba zai yi hukunci ta wurin abin da ya gani da idanunsa ba, ba zai kuwa yanke shawara ta wurin abin da ya ji da kunnuwansa ba;
4 но судит правдою смиренному суд и обличит правостию смиренныя земли, и поразит землю словом уст Своих и духом устен убиет нечестиваго:
amma da adalci zai yi wa masu bukata shari’a, da gaskiya zai yanke shawarwari saboda matalautan duniya. Kamar sanda zai bugi duniya da maganar bakinsa; da numfashin leɓunansa zai yanke mugaye.
5 и будет препоясан правдою о чреслех Своих и истиною обвит по ребрам Своим:
Adalci ne zai zama abin ɗamararsa aminci kuma igiyar da zai ɗaura kewaye da gindinsa.
6 и пастися будут вкупе волк с агнцем, и рысь почиет со козлищем, и телец и юнец и лев вкупе пастися будут, и отроча мало поведет я:
Kyarkeci zai zauna tare da ɗan rago damisa za tă kwanta tare da akuya, ɗan maraƙi da zaki da ɗan saniya za su yi kiwo tare; ɗan yaro ne zai lura da su.
7 и вол и медведь вкупе пастися будут, и вкупе дети их будут, и лев аки вол ясти будет плевы:
Saniya da beyar za su yi kiwo tare, ƙananansu za su kwanta tare, zaki kuma zai ci ciyawa kamar saniya.
8 и отроча младо на пещеры аспидов и на ложе изчадий аспидских руку возложит:
Jariri zai yi wasa kurkusa da ramin gamsheƙa, ɗan yaro kuma zai sa hannunsa a ramin maciji mai mugun dafi.
9 и не сотворят зла, ни возмогут погубити ни когоже на горе святей Моей: яко наполнися вся земля ведения Господня, аки вода многа покры море.
Ba za su yi lahani ko su hallaka wani a dutsena mai tsarki ba, gama duniya za tă cika da sanin Ubangiji kamar yadda ruwaye suka rufe teku.
10 И будет в день оный корень Иессеов, и востаяй владети языки, на того языцы уповати будут: и будет покой его честь.
A wannan rana Saiwar Yesse zai miƙe kamar tuta don mutanenta; al’ummai za su tattaru wurinsa, wurin hutunsa kuma zai zama mai daraja.
11 И будет в день оный, приложит Господь показати руку Свою, еже возревновати по останку прочему людий, иже аще останет от Ассириов и от Египта, и Вавилона и от Ефиопии, и от Еламитов и от Востоков солнца, и от Аравии и от островов морских.
A wannan rana Ubangiji zai miƙa hannunsa sau na biyu don yă maido da raguwar da ta rage na mutanensa daga Assuriya, daga Masar ta Ƙasa, daga Masar ta Bisa, daga Kush, daga Elam, daga Babiloniya, daga Hamat da kuma daga tsibiran teku.
12 И воздвигнет знамение в языки, и соберет погибшыя Израилевы, и расточенныя Иудины соберет от четырех крил земли.
Zai tā da tuta saboda al’ummai yă kuma tattara masu zaman bauta na Isra’ila; zai tattara mutanen Yahuda da suke a warwatse kusurwoyi huɗu na duniya.
13 И отимется ревность Ефремова, и врази Иудины погибнут: Ефрем не возревнует Иуде, и Иуда не оскорбит Ефрема.
Kishin Efraim zai ɓace, za a kuma kau da abokan gāban Yahuda; Efraim ba zai yi kishin Yahuda ba, haka ma Yahuda ba zai yi gāba da Efraim ba.
14 И полетят в кораблех иноплеменничих, море купно пленят, и сущих от Восток солнца, и Идумею: и на Моава первее руки возложат, сынове же Аммони первии покорятся.
Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma; tare za su washe mutane wajen gabas. Za su ɗibiya hannuwa a kan Edom da Mowab, Ammonawa kuma za su yi musu biyayya.
15 И опустошит Господь море Египетское и возложит руку Свою на реку духом пресильным: и поразит на седмь дебрий, якоже преходити ю во обувении:
Ubangiji zai busar da bakin tekun Masar; da iska mai zafi zai share hannunsa a bisa Kogin Yuferites Zai rarraba shi yă zama ƙanana rafuffuka bakwai saboda mutane su iya hayewa da ƙafa.
16 и будет прошествие людем Моим оставшым во Египте, и будет Израилю, якоже в день, егда изыде от земли Египетския.
Za a yi babbar hanya saboda raguwa mutanensa da ta rage daga Assuriya, kamar yadda ta kasance wa Isra’ila sa’ad da suka fito daga Masar.

< Книга пророка Исаии 11 >