< Бытие 8 >
1 И помяну Бог Ноа, и вся звери, и вся скоты, и вся птицы, и вся гады пресмыкающыяся, елика беху с ним в ковчезе: и наведе Бог дух на землю, и преста вода.
Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
2 И заключишася источницы бездны и хляби небесныя: и удержася дождь от небесе.
Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
3 И вспять пойде вода идущая от земли: и умаляшеся вода по сте пятидесятих днех.
Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
4 И седе ковчег в месяц седмый, в двадесять седмый день месяца, на горах Араратских.
A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
5 Вода же уходящи умаляшеся даже до десятаго месяца: и в десятый месяц, в первый день месяца явишася верси гор.
Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
6 И бысть до четыредесятих днех отверзе Ное оконце ковчега, еже сотвори,
Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
7 и посла врана (видети, аще уступила вода от лица земли): и изшед не возвратися, дондеже изсяче вода от земли.
ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
8 И посла голубицу по нем видети, аще уступила вода от лица земли:
Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
9 и не обретши голубица покоя ногама своима, возвратися к нему в ковчег, яко вода бяше по всему лицу всея земли: и простер руку свою, прият ю и внесе ю к себе в ковчег.
Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
10 И премедлив еще седмь дний, паки посла голубицу из ковчега.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
11 И возвратися к нему голубица к вечеру, и имеяше сучец масличен с листвием во устех своих: и позна Ное, яко уступи вода от лица земли.
Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
12 И премедлив еще седмь дний других, паки посла голубицу, и не приложи возвратитися к нему потом.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
13 И бысть в первое и шестьсотное лето жития Ноева, в первый день перваго месяца, изсяче вода от лица земли: и откры Ное покров ковчега, егоже сотвори, и виде, яко изсяче вода от лица земли.
A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
14 В месяц же вторый, в двадесять седмый день месяца изсше земля.
A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
15 И рече Господь Бог Ноеви, глаголя:
Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
16 изыди из ковчега ты и жена твоя, и сынове твои и жены сынов твоих с тобою:
“Fito daga jirgin, kai da matarka da’ya’yanka maza da matansu.
17 и вся звери, елицы суть с тобою, и всяку плоть от птиц даже до скотов, и всяк гад движущийся по земли изведи с собою: и раститеся и множитеся на земли.
Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
18 И изыде Ное и жена его, и сынове его и жены сынов его с ним,
Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da’ya’yansa maza da matan’ya’yansa,
19 и вси зверие, и вси скоти, и вся птицы и вси гади движущиися по роду своему на земли изыдоша из ковчега.
da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
20 И созда Ное жертвенник Господеви: и взя от всех скотов чистых и от всех птиц чистых и вознесе во всесожжение на жертвенник.
Sai Nuhu ya gina bagaden hadaya ga Ubangiji, ya ɗiba waɗansu dabbobi da tsuntsaye masu tsabta, ya yi hadaya ta ƙonawa da su a kan bagaden.
21 И обоня Господь воню благоухания. И рече Господь Бог размыслив: не приложу ктому прокляти землю за дела человеческая, зане прилежит помышление человеку прилежно на злая от юности его: не приложу убо ктому поразити всякую плоть живущую, якоже сотворих:
Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara la’anta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
22 во вся дни земли сеятва и жатва, зима и зной, лето и весна, день и нощь не престанут.
“Muddin duniya tana nan, lokacin shuki da na girbi, lokacin sanyi da na zafi, lokacin damina da na rani, dare da rana ba za su daina ba.”