< Книга пророка Иезекииля 22 >
1 И бысть слово Господне ко мне глаголя:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 и ты, сыне человечь, аще судити будеши граду кровей, и яви ему вся беззакония его,
“Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
3 и речеши: сия глаголет Адонаи Господь: о, граде проливаяй кровь среде себе, еже приити времени его, и творяй кумиры на себе, еже осквернитися самому:
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
4 в крови их, юже излиял еси, согрешил еси, и в кумирех твоих, яже творил, осквернился еси, и сократил еси дни твоя, и привед время лет твоих: сего ради дах тя на укоризну языком и на поругание всем странам,
kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
5 близ тебе и далече от тебе сущым, и поругаются тебе и возопиют на тя: о, нечистый, пресловутый и мног во беззакониих!
Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
6 Се, старейшины дому Израилева, кийждо ко своим ужикам смесишася в тебе, яко да пролиют кровь:
“‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
7 отцу и матери злословяху в тебе и ко пришелцу обращахуся неправдами в тебе: сироту и вдовицу преобидяху в тебе:
A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
8 и святая Моя уничижаху и субботы Моя оскверняху в тебе:
Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
9 мужие разбойницы беша в тебе, яко да пролиют в тебе кровь, и на горах ядяху в тебе и скверны творяху в тебе:
A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
10 стыд отчий открыша в тебе, и в нечистоте седящую обругаша в тебе:
A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
11 кийждо на жену подруга своего беззаконноваша, и кийждо невестку свою оскверняше в нечестии, и кийждо сестру свою, дщерь отца своего, обругаваше в тебе:
A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
12 мзды взимаху в тебе, яко да пролиют кровь, лихву и избыток взимаху в тебе: и скончал еси скончание злобы твоея яже в насилии, Мене же забыл еси, глаголет Адонаи Господь.
A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 Се убо, ударю рукою Моею о руку Мою на та, яже совершил еси и яже сотворил еси, и на крови твоя бывшыя посреде тебе:
“‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
14 аще устоит сердце твое, и аще преодолеют руце твои во днех, в няже Аз творю в тебе? Аз Господь глаголах, и сотворю.
Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
15 И разсыплю тя во языцех и разсею тя в странах, и оскудеет нечистота твоя из тебе,
Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
16 и владети буду тобою пред очима языков, и познаеши, яко Аз Господь.
Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
17 И бысть слово Господне ко мне глаголя:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 сыне человечь, се, быша Мне дом Израилев смешани вси с медию и железом, и со оловом чистым и со свинцем, среде пещи сребро смешено суть.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
19 Сего ради рцы: сия глаголет Адонаи Господь: понеже бысте вси во смешение едино, сего ради, се, Аз прииму вас во средину Иерусалима:
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
20 якоже приемлется сребро и медь, и железо и свинец и олово чистое во средину пещи, еже дунути на ня огню, да слиются, тако прииму вас во гневе Моем и в ярости Моей, и соберу и слию вас,
Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
21 и дуну на вы во огни гнева Моего, и слияни будете среде его:
Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
22 якоже сливается сребро среде пещи, тако слиетеся посреде его и познаете, яко Аз Господь излиях ярость Мою на вас.
Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
23 И бысть слово Господне ко мне глаголя:
Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
24 сыне человечь, рцы ему: ты еси земля неодождимая, ниже дождь бысть на тя в день ярости.
“Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
25 Егоже старейшины среде его, яко львы рыкающе, восхищающе восхищения, душы изядающе насилием, богатство и честь приемлюще, и вдовицы твоя умножишася посреде тебе:
Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
26 и жерцы его отвергошася закона Моего и оскверниша святая Моя: между святым и сквернавым не разлучаху, и между нечистым и чистым не разделяху, и от суббот Моих покрываху очи свои, и оскверняху Мя посреде себе:
Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
27 князи его среде его яко волцы восхищающе похищения, еже пролияти кровь и погубити душы, яко да лихоимством лихоимствуют:
Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
28 и пророцы его помазующии их падут, видящии суетная, волхвующии ложная, глаголюще: сия глаголет Адонаи Господь: а Господь не глагола.
Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
29 Людий земли утесняюще неправдою и восхищающе восхищения, нища и убога насильствующе и со пришелцем не живуще судом.
Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
30 И исках от них мужа живуща право и стояща цело пред лицем Моим во время гнева Моего, еже бы не до конца погубити его, и не обретох.
“Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
31 И излиях нань ярость Мою во огни гнева Моего, еже скончати я: пути их на главы их дах, глаголет Адонаи Господь.
Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”