< Исход 34 >
1 И рече Господь к Моисею: истеши себе две скрижали каменны, якоже и первыя, и взыди ко Мне на гору: и напишу на скрижалех словеса, яже бяху на скрижалех первых, яже сокрушил еси:
Ubangiji ya ce wa Musa “Sassaƙa alluna biyu kamar na farko, ni kuwa in rubuta kalmomin da suke cikin alluna na farko da ka farfasa.
2 и буди готов заутра, и взыдеши на гору Синайскую и предстанеши Мне тамо на версе горы:
Ka shirya da safe, ka hauro kan Dutsen Sinai. Ka gabatar da kanka a gare ni a can kan dutse.
3 и да никтоже взыдет с тобою, ниже да явится на всей горе: и овцы и говяда да не пасутся близ горы тоя.
Ba wani da zai zo tare da kai, ko a gan shi ko’ina a kan dutsen, kada garkunan tumaki ko na shanu su yi kiwo kusa da dutsen.”
4 И истеса две скрижали каменны, якоже и первыя: и утренневав Моисей заутра, взыде на гору Синайскую, якоже завеща ему Господь: и взя Моисей с собою две скрижали каменныя.
Saboda haka Musa ya sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na fari, sai ya hau Dutsen Sinai da sassafe, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, yana kuma ɗauke da alluna biyu na dutse a hannuwansa.
5 И сниде Господь во облаце, и предста ему тамо Моисей, и призва именем Господним.
Sa’an nan Ubangiji ya sauko a cikin girgije ya tsaya can tare da shi, ya kuma yi shelar sunansa.
6 И мимоиде Господь пред лицем его и воззва: Господь, Господь Бог щедр и милостив, долготерпелив и многомилостив и истинен,
Sai Ubangiji ya wuce a gaban Musa, ya yi shela ya ce, “Ni ne Ubangiji Allah mai tausayi, mai alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna da aminci,
7 и правду храняй, и творяй милость в тысящы, отемляй беззакония и неправды и грехи, и повиннаго не очистит, наводяй грехи отцев на чада, и на чада чад, до третияго и четвертаго рода.
nakan nuna ƙauna wa dubbai, nakan kuma gafarta mugunta, tawaye da zunubi. Amma ba na barin mai laifi, ba tare da na hore shi ba; nakan hukunta’ya’ya da jikoki har tsara ta uku da ta huɗu saboda laifin iyaye.”
8 И потщався Моисей, приник на землю, поклонися Богу
Musa ya yi sauri ya rusuna har ƙasa, ya yi sujada.
9 и рече: аще обретох благодать пред Тобою, да идет Господь мой с нами: людие бо жестоковыйнии суть: и отимеши ты грехи нашя и беззакония наша, и будем Твои.
Ya ce, “Ya Ubangiji, in na sami tagomashi a idanunka, bari Ubangiji yă tafi tare da mu. Ko da yake wannan mutane masu taurinkai ne, ka gafarta muguntanmu da zunubanmu, ka kuma sāke sa mu zama abin gādonka.”
10 И рече Господь к Моисею: се, Аз полагаю тебе завет пред всеми людьми твоими, и сотворю славная, яже не быша по всей земли и во всех языцех: и узрят вси людие, в нихже еси ты, дела Господня, яко чудна суть, яже Аз сотворю тебе:
Sai Ubangiji ya ce, “Ga shi na yi alkawari da kai. A gaban dukan mutanenka zan yi abubuwan banmamakin da ba a taɓa yinsa a cikin wata al’umma a duniya ba. Mutanen da kuke zaune cikinsu za su ga aikin bantsoro, da Ni Ubangiji zan yi muku.
11 внемли ты вся, елика Аз заповедаю тебе: се, Аз изжену пред лицем вашим Аморреа и Хананеа, и Хеттеа и Ферезеа, и Евеа и Гергесеа и Иевусеа:
Ku yi biyayya da umarnin da na ba ka yau. Zan kora muku Amoriyawa, Kan’aniyawa, Hittiyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa.
12 внемли себе, да не когда завещаеши завет седящым на земли, в нюже внидеши, да не будет соблазн в вас:
Ku kula, kada ku yi yarjejjeniya da waɗanda suke zaune a ƙasar da za ku tafi, in ba haka ba, za su zama muku tarko.
13 капища их разорите и кумиры их сокрушите, и дубравы их посецыте, и изваяная богов их сожжите огнем,
Ku rurrushe bagadansu, ku farfashe keɓaɓɓun duwatsunsu, ku sassare ginshiƙan Asheransu.
14 не бо поклонитеся богом иным: ибо Господь Бог ревниво имя, Бог ревнив есть:
Kada ku bauta wa wani allah, gama Ubangiji, wanda sunansa Kishi, Allah ne mai kishi.
15 да не когда завещаеши завет седящым на земли, и соблудят вслед богов их, и пожрут богом их, и призовут тя, и снеси от жертв их:
“Ku kula, kada ku yi yarjejjeniya da mazaunan wannan ƙasa, don kada sa’ad da suke yi wa allolinsu sujada, suna miƙa musu hadaya, su gayyace ku, ku ci hadayar da suka miƙa wa allolinsu.
16 и поймеши от дщерей их сыном твоим, и от дщерей твоих даси сыном их, и соблудят дщери твоя вслед богов их, и сынове твои соблудят вслед богов их:
Kada ku auro wa’ya’yanku maza’yan matansu, waɗanda suke yi wa alloli sujada, har su sa’ya’yanku su bi allolinsu.
17 и богов слияных да не сотвориши себе:
“Kada ku yi alloli na zubi.
18 и праздник опресночный да сохраниши: седмь дний да яси опресноки, якоже заповедах тебе, во время в месяце новых плодов: в месяце бо новых плодов изшел еси от земли Египетския:
“Sai ku yi Bikin Burodi Marar Yisti. Ku kuma ci burodi marar yisti har kwana bakwai, kamar yadda na umarce ku. Ku yi wannan a ƙayyadadden lokacinsa a watan Abib, gama a cikin watan ne kuka fita daga Masar.
19 всяко разверзающее ложесна мужеск Мне пол (да будет), всяко первородное телца и первородное овцы:
“Ɗan fari na kowane mutum zai zama nawa, har da ɗan farin na dabbobi, ko na garken shanu ko na tumaki.
20 и первородное осляте искупиши овцею: аще же не искупиши е, цену да даси его: всякаго первенца от сынов твоих да искупиши, да не явишися предо Мною тощь:
Ku fanshi ɗan farin jaki da na tunkiya, amma in ba ku fanshe shi ba, ku karya wuyansa. Ku fanshi duk’ya’yan farinku maza. “Kada wani yă zo gabana hannu wofi.
21 в шесть дний да делаеши, в седмый же день да почиеши, от сеятвы и жатвы да почиеши,
“Kwana shida za ku yi aiki, amma a rana ta bakwai za ku huta; ko da lokacin noma ne, ko lokacin girbi, sai ku huta.
22 и праздник седмиц да сотвориши ми, начало жатвы пшеницы, и праздник собрания посреде лета:
“Ku kiyaye Bikin Makoni wato, bikin girbin nunan fari na alkama, da Bikin Gama Tattara amfanin gonaki, a ƙarshen shekara.
23 в три времена лета да явится всяк мужеск пол твой пред Господем Богом Израилевым:
Sau uku a shekara, dukan mazanku za su bayyana a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, Allah na Isra’ila.
24 егда бо изжену языки от лица твоего и разширю пределы твоя, никтоже возжелает земли твоея, егда приидеши явитися пред Господем Богом твоим в три времена лета:
Zan kore al’umma daga gabanku, in fadada kan iyakarku, babu wanda zai yi ƙyashin ƙasarku a lokutan nan uku na shekara da kuka haura don ku bayyana a gaban Ubangiji, Allahnku.
25 да не заколеши с квасом крове жертв Моих, и да не прележит до утрия жертва праздника Пасхи:
“Kada ku miƙa mini jinin hadaya tare da wani abin da yana da yisti, kada kuma ku bar kowace hadaya ta Bikin Ƙetarewa ta kwana.
26 первородная жит земли твоея да внесеши в дом Господа Бога твоего: да не свариши агнца во млеце матере его.
“Ku kawo nunan farin amfanin gonarku mafi kyau a gidan Ubangiji, Allahnku. “Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madarar mahaifiyarsa.”
27 И рече Господь к Моисею: напиши себе словеса сия, в словесех бо сих положих тебе завет и Израилю.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka rubuta waɗannan kalmomi, gama bisa ga kalmomin nan, na yi alkawari da kai da kuma Isra’ila.”
28 И бе тамо Моисей пред Господем четыредесять дний и четыредесять нощей: хлеба не яде и воды не пи: и написа (Моисей) на скрижалех словеса сия завета, десять словес.
Musa ya kasance tare da Ubangiji kwana arba’in da dare arba’in, bai ci ba, bai sha ba. Ya kuma rubuta kalmomin alkawari a kan alluna, wato, dokoki goma.
29 Сходящу же Моисею с горы Синайския, и обе скрижали в руку Моисеову: сходящу же ему с горы, и Моисей не ведяше, яко прославися зрак плоти лица его, егда глаголаше с ним.
Sa’ad da Musa ya sauko daga kan Dutsen Sinai tare da alluna biyu na Alkawari a hannuwansa, bai san cewa fuskarsa tana ƙyalli ba saboda zaman da ya yi a gaban Ubangiji.
30 И виде Аарон и вси сынове Израилевы Моисеа, и бяше прославлен зрак плоти лица его: и убояшася приступити к нему.
Da Haruna da dukan Isra’ila suka ga Musa, fuskarsa kuma tana ƙyalli, sai suka ji tsoron zuwa kusa da shi.
31 И воззва их Моисей, и обратишася к нему Аарон и вси князи сонма: и глагола Моисей к ним.
Amma Musa ya kira su, sai Haruna da dukan shugabannin jama’ar suka zo wurinsa, ya kuwa yi musu magana.
32 И по сих приидоша к нему вси сынове Израилевы: и заповеда им вся, елика глагола к нему Господь на горе Синайстей.
Daga baya sai dukan Isra’ilawa suka zo kusa da shi, ya kuma ba su dukan dokokin da Ubangiji ya ba shi a Dutsen Sinai.
33 И егда преста глаголя к ним, возложи на лице свое покров.
Da Musa ya gama magana da su, sai ya lulluɓe fuskarsa.
34 Егда же вхождаше Моисей пред Господа глаголати к Нему, снимаше покров, дондеже исхождаше: и изшед глаголаше ко всем сыном Израилевым, елика заповеда ему Господь.
Amma duk sa’ad da ya je gaban Ubangiji don yă yi magana da shi, sai yă tuɓe lulluɓin har sai ya fito. Kuma duk sa’ad da ya fito yă faɗa wa Isra’ilawa abin da aka umarce shi,
35 И видеша сынове Израилевы лице Моисеово, яко прославися: и возлагаше Моисей покров на лице свое, дондеже внидет глаголати с Ним.
sai su ga fuskarsa tana ƙyalli. Sa’an nan Musa yă sāke lulluɓe fuskarsa, har sai ya shiga don yă yi magana da Ubangiji.