< Первая книга Царств 3 >
1 И отрочищь Самуил бе служа Господеви пред Илием иереем, и глаголгол Господень бе честен в тыя дни, не бе видение посылаемо.
Yaron nan Sama’ila ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli. A waɗannan kwanaki kuwa jin magana daga wurin Ubangiji ba safai ba, babu kuma wahayi da yawa.
2 И бысть в день он, и Илий спаше на месте своем, и очи его начаста тяжце быти, и не можаше зрети:
Wata rana da dare Eli da idanunsa sun kusa makancewa har ba ya iya gani sosai yana kwance a inda ya saba.
3 и прежде неже угасе светилник Божий, и Самуил спаше в церкви Господни, идеже кивот Божий,
Fitilar Allah kuwa tana ci, ba tă mutu ba tukuna, Sama’ila kuma na kwance a haikali na Ubangiji inda akwai akwatin Allah.
4 и воззва Господь: Самуиле, Самуиле. И рече: се, аз.
Sai Ubangiji ya kira Sama’ila. Sama’ila ya amsa ya ce, “Ga ni.”
5 И тече ко Илию и рече: се, аз, яко звал мя еси. И рече (Илий): не звах тебе, возвратися и спи. И возвратися и спа.
Sai ya ruga wajen Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Eli ya ce, “Ɗana ban kira ba, je ka kwanta”. Saboda haka ya tafi ya kwanta.
6 И приложи Господь и воззва еще: Самуиле, Самуиле. И воста Самуил и иде ко Илию вторицею, и рече: се, аз, яко звал мя еси. И рече: не звах тебе, чадо мое, возвратися, спи.
Ubangiji ya sāke kiransa ya ce, “Sama’ila!” Sama’ila ya tashi kuma ya je wurin Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Amma Eli ya ce, “Ban kira ka ba, ɗana koma ka kwanta.”
7 Самуил же в то время еще не познаваше Бога, прежде откровения ему гласа Господня.
Sama’ila dai bai riga ya san Ubangiji ba tukuna. Ba a kuma taɓa bayyana maganar Ubangiji a gare shi ba tukuna ba.
8 И приложи Господь призвати Самуила третицею: и востав, и иде ко Илию и рече: се, аз, яко звал мя еси. И разуме Илий, яко Господь призывает отрочища, и рече: возвратися и спи, чадо:
Ubangiji ya kira Sama’ila sau na uku, Sama’ila kuma ya tashi ya tafi wurin Eli, “Ga ni, gama ka kira ni.” Sai Eli ya gane cewa Ubangiji ne ke kira yaron.
9 и будет аще воззовет тя Зовый, и речеши: глаголи, Господи, яко слышит раб Твой. И иде Самуил, и спа на месте своем.
Saboda haka, Eli ya gaya wa Sama’ila cewa, “Je ka kwanta, in kuma ya kira ka, ka ce masa, ‘Ya Ubangiji ka yi magana gama bawanka yana saurara.’” Sama’ila ya koma ya kwanta a wurin kwanciyarsa.
10 И прииде Господь и ста и воззва его якоже первое и второе: Самуиле, Самуиле. И рече Самуил: глаголи (Господи), яко слышит раб Твой.
Ubangiji kuma ya zo ya tsaya a wurin, yana kira ya ce, “Sama’ila, Sama’ila!” Kamar yadda ya kira a lokutan baya. Sai Sama’ila ya ce, “Yi magana gama bawanka yana saurara.”
11 И рече Господь к Самуилу: се, Аз творю глаголголы Моя во Израили, яко всякому слышащему сия пошумит во обоих ушесех его:
Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Duba ina dab da yin wani abu a Isra’ila da zai sa kunne kowa da yake ji, yă ji tsoro.
12 в день той воздвигну на Илиа вся, елика глаголах на дом его: начну и скончаю:
A ranar zan cika dukan maganar da na yi game da Eli da iyalinsa, daga farko har ƙarshe.
13 и возвестих ему, яко отмщу Аз на доме его до века в неправдах сынов его, о нихже ведяше, яко злословиста Бога сынове его, и не наказа их:
Gama na gaya masa zan hukunta gidansa har abada saboda zunubin da yake sane da shi;’ya’yansa sun wulaƙantar da kansu, shi kuma bai tsawata musu ba.
14 и сего ради кляхся дому Илиину, яко не очистится неправда дому Илиина в кадилах и жертвах его до века.
Saboda haka na rantse a kan gidan Eli, ‘Ba za a taɓa shafe laifin gidan Eli da hadaya ko baiko ba.’”
15 И спа Самуил до утра, и утренева заутра, и отверзе двери храма Господня. Самуил же убояся поведати видения Илию.
Sama’ila kuwa ya kwanta har safe, sa’an nan ya buɗe ƙofofin gidan Ubangiji. Ya ji tsoro yă gaya wa Eli wahayin,
16 И рече Илий к Самуилу: Самуиле чадо. И рече: се, аз.
amma Eli ya kira shi ya ce, “Sama’ila, ɗana.” Sama’ila ya ce, “Ga ni.”
17 И рече (Илий): что глаголгол глаголголанный к тебе? Не скрый убо от мене: сия да сотворит тебе Бог и сия да приложит, аще утаиши от мене слово от всех словес глаголголанных к тебе во ушеса твоя.
Eli ya ce, mene ne ya ce maka? Kada ka ɓoye mini. Allah ya yi da kai har ma fiye in ka ɓoye mini kome da ya ce maka.
18 И поведа Самуил Илию вся словеса, и не утаи от него (ни единаго глаголгола). И рече Илий: Господь Сам, еже благо пред Ним, да сотворит.
Don haka sai Sama’ila ya gaya masa kome bai ɓoye masa kome ba. Sa’an nan Eli ya ce, “Shi ne Ubangiji bari yă yi abin da ya yi kyau a gare shi.”
19 И возвеличен бысть Самуил, и Господь бе с ним, и не паде от всех словес его на земли (ни един глагол).
Ubangiji kuwa yana tare da Sama’ila har girmansa bai kuma bar ko ɗaya daga maganarsa ta kāsa cika ba.
20 И разумеша вси Израилтяне от Дана даже и до Вирсавии, яко верен Самуил Господу во пророцех.
Dukan Isra’ila daga Dan har Beyersheba suka shaida amincin Sama’ila annabi ne na Ubangiji.
21 И приложи Господь явитися в Силоме, яви бо Ся Господь Самуилу: и уверися Самуил пророк быти Господеви во всем Израили, от конца до конца земли. Илий же состареся зело, и сынове его ходяще хождаху, и лукав путь их пред Господем.
Ubangiji kuwa ya dinga bayyana a Shilo, a nan ya bayyana kansa ga Sama’ila ta wurin maganarsa.