< Jobho 22 >
1 Ipapo Erifazi muTemani akapindura akati:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 “Ko, munhu angabatsira Mwari here? Kunyange munhu akachenjera angamubatsira here?
“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
3 Wamasimba Ose angawana mufaro weiko dai iwe wakarurama? Aibatsirwa neiko dai nzira dzako dzaiva dzakarurama?
Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
4 “Imhaka yokumunamata kwako here zvaanokutsiura uyewo achikupa mhosva?
“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
5 Zvakaipa zvako hazvina kukura here? Handiti zvivi zvako hazviperi?
Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
6 Wakakumbira rubatso kuhama dzako pasina; wakatorera vanhu nguo dzavo, uchivasiya vasina kupfeka.
Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
7 Wakanyima mvura vakaneta uye wakanyima vane nzara zvokudya,
Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
8 kunyange wakanga uri munhu ane simba, ane minda yake, uri munhu anokudzwa, agere pairi.
Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
9 Wakadzinga chirikadzi dzisina chinhu uye wakavhuna simba renherera.
Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
10 Ndokusaka misungo yakakukomberedza, ndokusaka njodzi ichikuvhundutsa,
Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
11 ndokusaka kuine rima usingakwanisi kuona, uye mafashamu emvura achikufukidza.
An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
12 “Ko, Mwari haazi kumusoro kwokudenga here? Tarira kukwirira kwakaita nyeredzi dzokumusoro-soro!
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
13 Asi imi munoti, ‘Mwari anoziveiko? Ko, anotonga murima rakadai here?
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
14 Makore matema anomufukidza, saka haationi paanofamba-famba padenderedzwa ramatenga.’
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
15 Ko, iwe ucharambira munzira yakare iya yakatsikwa navanhu vakaipa here?
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
16 Ivo vakabvutwa nguva yavo isati yasvika, hwaro hwavo hwakakukurwa namafashamu.
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
17 Vakati kuna Mwari, ‘Tisiyei takadaro! Wamasimba Ose angaiteiko kwatiri?’
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
18 Sezvo ari iye akazadza dzimba dzavo nezvinhu zvakanaka, ndinomira kure namano avakaipa.
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
19 “Vakarurama vanoona kuparadzwa kwavo vagofara, vasina mhaka vanovaseka vachiti,
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
20 ‘Zvirokwazvo vadzivisi vedu vaparadzwa, uye moto unopedza pfuma yavo.’
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
21 “Zviise pasi paMwari ugova norugare naye, nenzira iyi kubudirira kuchasvika kwauri.
“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
22 Gamuchira kurayira kunobva mumuromo make uye uchengete mashoko ake mumwoyo.
Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
23 Kana ukadzokera kuna Wamasimba Ose, uchadzoredzerwa: Kana ukabvisa zvakaipa uchizviisa kure netende rako,
In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
24 uye ukaisa goridhe rako paguruva, iro goridhe rako rokuOfiri kumatombo okunzizi,
Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
25 ipapo Wamasimba Ose achava goridhe rako, iyo sirivha yako yakanyatsosanangurwa.
sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
26 Zvirokwazvo ipapo uchawana mufaro muna Wamasimba Ose, uye uchasimudzira chiso chako kuna Mwari.
Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
27 Uchanyengetera kwaari, uye achakunzwa, uye iwe uchazadzisa zvawakapika.
Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
28 Zvaunotaura sechirevo zvichaitika, uye chiedza chichavhenekera panzira dzako.
Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
29 Vanhu pavanodzikiswa iwe ukati, ‘Vasimudzei!’ ipapo vakaderedzwa vachaponeswa.
Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
30 Achadzikinura kunyange uyo ane mhosva, acharwirwa kubudikidza nokuchena kwamaoko ako.”
Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”