< Псалми 107 >

1 Хвалите Господа, јер је добар; јер је довека милост Његова.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Тако нека кажу које је избавио Господ, које је избавио из руке непријатељеве,
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 Скупио их из земаља, од истока и запада, од севера и мора.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Луташе по пустињи где се не живи, пута граду насељеном не находише;
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Беху гладни и жедни, и душа њихова изнемагаше у њима;
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Али завикаше ка Господу у тузи својој; и избави их из невоље њихове.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 И изведе их на прав пут, који иде у град насељени.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Нека хвале Господа за милост Његову, и за чудеса Његова ради синова људских!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Јер сити душу ташту, и душу гладну пуни добра.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Седеше у тами и у сену смртном, оковани у тугу и у гвожђе;
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Јер не слушаше речи Божијих, и не марише за вољу Вишњег.
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Он поништи срце њихово страдањем; спотакоше се, и не беше кога да помогне.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Али завикаше ка Господу у тузи својој, и избави их из невоље њихове;
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 Изведе их из таме и сена смртног, и раскиде окове њихове.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Нека хвале Господа за милост Његову, и за чудеса Његова ради синова људских!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Јер разби врата бронзана, и преворнице гвоздене сломи.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Безумници страдаше за неваљале путеве своје, и за неправде своје.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Свако се јело гадило души њиховој, и дођоше до врата смртних.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Али завикаше ка Господу у тузи својој, и избави их из невоље њихове.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Посла реч своју и исцели их, и избави их из гроба њиховог.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Нека хвале Господа за милост Његову, и за чудеса Његова ради синова људских!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 И нека принесу жртву за хвалу, и казују дела Његова у песмама!
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Који плове по мору на корабљима, и раде на великим водама,
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 Они су видели дела Господња, и чудеса Његова у дубини.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 Каже, и диже се силан ветар, и устају вали на њему,
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 Дижу се до небеса и спуштају до бездана: душа се њихова у невољи разлива;
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Посрћу и љуљају се као пијани; све мудрости њихове нестаје.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Али завикаше ка Господу у тузи својој, и изведе их из невоље њихове.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 Он обраћа ветар у тишину, и вали њихови умукну.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Веселе се кад се стишају, и води их у пристаниште које желе.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Нека хвале Господа за милост Његову, и за чудеса Његова ради синова људских!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Нека Га узвишују на сабору народном, на скупштини старешинској славе Га!
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Он претвара реке у пустињу, и изворе водене у сухоту,
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 Родну земљу у слану пустару за неваљалство оних који живе на њој.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Он претвара пустињу у језера, и суву земљу у изворе водене,
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 И насељава онамо гладне. Они зидају градове за живљење;
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 Сеју поља, саде винограде и сабирају летину.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Благосиља их и множе се јако, и стоке им не умањује.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Пре их беше мало, падаху од зла и невоље, што их стизаше.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 Он сипа срамоту на кнезове, и оставља их да лутају по пустињи где нема путева.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Он извлачи убогога из невоље, и племена множи као стадо.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Добри виде и радују се, а свако неваљалство затискује уста своја.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Ко је мудар, нека запамти ово, и нека познају милости Господње.
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Псалми 107 >