< Матеј 26 >

1 И кад сврши Исус речи ове, рече ученицима својим:
Sa’ad da Yesu ya gama faɗin dukan waɗannan abubuwa, sai ya ce wa almajiransa,
2 Знате да ће до два дана бити пасха, и Сина човечијег предаће да се разапне.
“Kamar yadda kuka sani, Bikin Ƙetarewa sauran kwana biyu, za a kuma ba da Ɗan Mutum don a gicciye shi.”
3 Тада скупише се главари свештенички и књижевници и старешине народне у двор поглавара свештеничког по имену Кајафе;
Sai manyan firistoci da dattawan mutane, suka taru a fadan babban firist, mai suna Kayifas,
4 И световаше се како би Исуса из преваре ухватили и убили.
suka ƙulla shawara su kama Yesu da makirci, su kuma kashe shi.
5 И говораху: Али не о празнику, да се не би народ побунио.
Suka ce, “Amma ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su tā da rikici.”
6 А кад Исус беше у Витанији у кући Симона губавог,
Yayinda Yesu yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu,
7 Приступи к Њему жена са скленицом мира многоценог, и изли на главу Његову кад сеђаше за трпезом.
wata mace ta zo wurinsa da wani ɗan tulun alabasta na turaren mai tsada sosai, wanda ta zuba a kansa a lokacin da yake cin abinci.
8 А кад видеше то ученици Његови, расрдише се говорећи: Зашто се чини таква штета?
Sa’ad da almajiransa suka ga wannan, sai suka yi fushi. Suka ce, “Wannan almubazzaranci fa!
9 Јер се могло ово продати скупо и новци дати сиромасима.
Wannan turare ai, da an sayar da shi da kuɗi mai yawa a ba matalauta kuɗin.”
10 А кад разуме Исус, рече им: Шта сметате жену? Она учини добро дело на мени.
Sane da wannan, Yesu ya ce musu, “Me ya sa kuke damun macen nan? Ta yi mini abu mai kyau ne.
11 Јер сиромахе имате свагда са собом, а мене немате свагда.
Matalauta za su kasance tare da ku kullum, amma ni ba zan kasance tare da ku kullum ba.
12 А она изливши миро ово на тело моје за укоп ме приготови.
Sa’ad da ta zuba turaren nan a jikina, ta shirya ni ne don jana’izata.
13 Заиста вам кажем: где се год успроповеда ово јеванђеље по свему свету, казаће се и то за спомен њен што учини она.
Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bisharan nan a duniya duka, abin da matan nan ta yi, za a riƙa faɗarsa don tunawa da ita.”
14 Тада један од дванаесторице, по имену Јуда Искариотски, отиде ка главарима свештеничким,
Sai ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, wanda ake kira Yahuda Iskariyot, ya je wurin manyan firistoci
15 И рече: Шта ћете ми дати да вам га издам? А они му обрекоше тридесет сребрника.
ya ce, “Me za ku ba ni, in na bashe shi gare ku?” Sai suka ƙirga masa kuɗi azurfa talatin.
16 И отада тражаше згоду да Га изда.
Daga wannan lokaci, Yahuda ya yi ta neman zarafin da zai miƙa shi.
17 А у први дан пресних хлебова приступише ученици к Исусу говорећи: Где ћеш да ти зготовимо пасху да једеш?
A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, sai almajiran suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
18 А Он рече: Идите у град к томе и томе, и кажите му: Учитељ каже: време је моје близу, у тебе ћу да учиним пасху с ученицима својим.
Ya amsa ya ce, “Ku shiga gari wurin wāne, ku ce masa, ‘Malam ya ce, lokacina ya yi kusa. Zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina a gidanka.’”
19 И учинише ученици како им заповеди Исус, и уготовише пасху.
Saboda haka almajiran suka yi yadda Yesu ya umarce su, suka kuwa shirya Bikin Ƙetarewa.
20 А кад би увече, седе за трпезу са дванаесторицом.
Da yamma ta yi, sai Yesu ya zauna don cin abinci tare da Sha Biyun.
21 И кад јеђаху рече им: Заиста вам кажем: један између вас издаће ме.
Yayinda suke cin abinci, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
22 И забринувши се врло почеше сваки говорити Му: Да нисам ја, Господе?
Suka yi baƙin ciki ƙwarai, suka fara ce masa da ɗaya-ɗaya, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
23 А Он одговарајући рече: Који умочи са мном руку у зделу онај ће ме издати.
Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya sa hannunsa a kwano tare da ni ne, zai bashe ni.
24 Син човечији дакле иде као што је писано за Њега; али тешко оном човеку који изда Сина човечијег; боље би му било да се није ни родио онај човек.
Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda aka rubuta game da shi. Amma kaiton mutumin da zai bashe Ɗan Mutum! Da ma ba a haifi mutumin nan ba, da ya fi masa.”
25 А Јуда, издајник Његов, одговарајући рече: Да нисам ја, рави? Рече му: Ти каза.
Sa’an nan Yahuda, wanda zai bashe shi ya ce, “Tabbatacce ba ni ba ne, ko, Rabbi?” Yesu ya amsa ya ce, “I, kai ma ka fada.”
26 И кад јеђаху, узе Исус хлеб и благословивши преломи га, и даваше ученицима, и рече: Узмите, једите; ово је тело моје.
Yayinda suke cikin cin abinci, Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya ya kuma kakkarya, ya ba wa almajiransa yana cewa, “Ku karɓa ku ci; wannan jikina ne.”
27 И узе чашу и давши хвалу даде им говорећи: Пијте из ње сви;
Sa’an nan ya ɗauki kwaf, ya yi godiya, ya kuma ba su, yana cewa, “Ku shassha daga cikinsa, dukanku.
28 Јер је ово крв моја новог завета која ће се пролити за многе ради отпуштења греха.
Wannan jinina ne na sabon alkawari, wanda aka zubar saboda mutane da yawa, don gafarar zunubai.
29 Кажем вам пак да нећу одсад пити од овог рода виноградског до оног дана кад ћу пити с вама новог у царству Оца свог.
Ina gaya muku, ba zan ƙara shan ruwan inabin nan ba har sai ranar da zan sha shi sabo tare da ku a mulkin Ubana.”
30 И отпојавши хвалу изиђоше на гору Маслинску.
Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
31 Тада рече им Исус: Сви ћете се ви саблазнити о мене ову ноћ; јер у писму стоји: Ударићу пастира и овце од стада разбежаће се.
Sai Yesu ya ce musu, “A wannan dare, dukanku za ku ja da baya saboda ni, gama a rubuce yake cewa, “‘Zan bugi makiyayin, tumakin garken kuwa za su fasu.’
32 А по васкрсењу свом ја идем пред вама у Галилеју.
Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
33 А Петар рече Му: Ако се и сви саблазне о тебе ја се нећу никад саблазнити.
Bitrus ya amsa ya ce, “Ko da duka sun ja da baya saboda kai, ba zan taɓa ja da baya ba.”
34 Рече му Исус: Заиста ти кажем: ноћас док петао не запева три пута ћеш ме се одрећи.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya maka, a daren nan, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
35 Рече Њему Петар: Да бих знао и умрети с Тобом нећу Те се одрећи. Тако и сви ученици рекоше.
Bitrus ya furta, “Ko da ma zan mutu ne tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Dukan sauran almajiran ma suka faɗa haka.
36 Тада дође Исус с њима у село које се зове Гетсиманија, и рече ученицима: Седите ту док ја идем тамо да се помолим Богу.
Sa’an nan Yesu ya tafi da almajiransa zuwa wani wurin da ake kira Getsemane, ya ce musu, “Ku zauna nan, in je can in yi addu’a.”
37 И узевши Петра и оба сина Зеведејева забрину се и поче тужити.
Ya ɗauki Bitrus da’ya’ya biyun nan na Zebedi tare da shi, sai ya fara baƙin ciki, ya kuma damu.
38 Тада рече им Исус: Жалосна је душа моја до смрти; почекајте овде, и стражите са мном.
Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har kamar zan mutu. Ku dakata a nan, ku kuma yi tsaro tare da ni.”
39 И отишавши мало паде на лице своје молећи се и говорећи: Оче мој! Ако је могуће да ме мимоиђе чаша ова; али опет не како ја хоћу него како Ти.
Da ya yi gaba kaɗan, sai ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in mai yiwuwa ne, a ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba nufina ba, sai naka.”
40 И дошавши к ученицима нађе их где спавају, и рече Петру: Зар не могосте један час постражити са мном?
Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya tarar suna barci. Ya tambayi Bitrus ya ce, “Ashe, ba za ku iya yin tsaro tare da ni ko na sa’a guda ba?
41 Стражите и молите се Богу да не паднете у напаст; јер је дух срчан, али је тело слабо.
Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
42 Опет по други пут отиде и помоли се говорећи: Оче мој! Ако ме не може чаша ова мимоићи да је не пијем, нека буде воља Твоја.
Ya sāke tafiya sau na biyu, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in ba zai yiwu a ɗauke wannan kwaf ba sai na sha shi, to, bari a aikata nufinka.”
43 И дошавши нађе их опет где спавају; јер им беху очи отежале.
Da ya dawo, har yanzu ya tarar suna barci, domin idanunsu sun yi nauyi da barci.
44 И оставивши их отиде опет и трећи пут те се помоли говорећи оне исте речи.
Saboda haka ya sāke barinsu, ya yi addu’a sau na uku, yana maimaita iri abu guda.
45 Тада дође к ученицима својим и рече им: Једнако спавате и почивате; ево се приближи час, и Син човечији предаје се у руке грешника.
Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya ce musu, “Har yanzu kuna barci kuna hutawa ba? Ga shi, sa’a ta yi kusa, an kuma bashe Ɗan Mutum a hannuwan masu zunubi.
46 Устаните да идемо; ево се приближи издајник мој.
Ku tashi, mu tafi! Ga mai bashe ni nan yana zuwa!”
47 И док Он још тако говораше, гле, Јуда, један од дванаесторице, дође, и с њим људи многи с ножевима и с кољем од главара свештеничких и старешина народних.
Yayinda yana cikin magana, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya iso. Tare da shi kuwa ga taro mai yawa riƙe da takuba da sanduna, manyan firistoci da dattawan mutane ne suka turo su.
48 А издајник Његов даде им знак говорећи: Кога ја целивам онај је; држите га.
To, mai bashe shi ɗin, ya riga ya shirya alama da su, “Wanda na yi masa sumba, shi ne mutumin; ku kama shi.”
49 И одмах приступивши к Исусу рече: Здраво, рави! И целива Га.
Da zuwansa, sai ya miƙe zuwa wurin Yesu ya ce, “Gaisuwa, Rabbi!” Sa’an nan ya yi masa sumba.
50 А Исус рече му: Пријатељу! Шта ћеш ти овде? Тада приступивши дигоше руке на Исуса и ухватише Га.
Yesu ya amsa ya ce, “Aboki, yi abin da ya kawo ka.” Sa’an nan mutanen suka matso, suka kama Yesu suka riƙe shi.
51 И гле, један од оних што беху са Исусом машивши се руком извади нож свој те удари слугу поглавара свештеничког, и одсече му ухо.
Ganin haka, sai ɗaya daga cikin waɗanda suke tare da Yesu, ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya fille masa kunne.
52 Тада рече му Исус: Врати нож свој на место његово; јер сви који се маше за нож од ножа ће изгинути.
Sai Yesu ya ce, masa, “Mai da takobinka kube, gama duk masu zare takobi, a takobi za su mutu.
53 Или мислиш ти да ја не могу сад умолити Оца свог да ми пошаље више од дванаест легеона анђела?
Kuna tsammani ba zan iya kira Ubana, nan take kuwa yă aiko mini fiye da rundunar mala’iku goma sha biyu ba?
54 Али како би се испунило шта стоји у писму да ово треба да буде?
Amma ta yaya za a cika Nassin da ya ce dole haka yă faru?”
55 У тај час рече Исус људима: Као на хајдука изишли сте с ножевима и с кољем да ме ухватите, а сваки дан сам код вас седео учећи у цркви, и не ухватисте ме.
A wannan lokaci sai Yesu ya ce wa taron, “Ina jagoran wani tawaye ne, da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni? Kowace rana ina zama a filin haikali ina koyarwa, ba ku kuwa kama ni ba.
56 А ово све би да се збуду писма пророчка. Тада ученици сви оставише Га, и побегоше.
Amma wannan duka ya faru ne don a cika rubuce-rubucen annabawa.” Sa’an nan dukan almajiran suka yashe shi suka gudu.
57 И они што ухватише Исуса одведоше Га поглавару свештеничком, Кајафи, где се књижевници и старешине сабраше.
Waɗanda suka kama Yesu kuwa suka kai shi wurin Kayifas, babban firist, inda malaman dokoki da dattawa suka taru.
58 А Петар иђаше за Њим издалека до двора поглавара свештеничког и ушавши унутра седе са слугама да види свршетак.
Amma Bitrus ya bi daga nesa, har zuwa cikin filin gidan babban firist. Ya shiga, ya zauna tare da masu gadi, don yă ga ƙarshen abin.
59 А главари свештенички и старешине и сав сабор тражаху лажна сведочанства на Исуса да би Га убили;
Sai manyan firistoci da’yan majalisa duka suka yi ta neman shaidar ƙarya a kan Yesu, don su sami dama su kashe shi.
60 И не нађоше; и премда многи лажни сведоци долазише, не нађоше. Најпосле дођоше два лажна сведока,
Amma ba su sami ko ɗaya ba, ko da yake masu shaidar ƙarya da yawa sun firfito. A ƙarshe, biyu suka zo gaba,
61 И рекоше: Он је казао: Ја могу развалити цркву Божју и за три дана начинити је.
suka furta cewa, “Wannan mutum ya ce, ‘Ina iya rushe haikalin Allah, in sāke gina shi cikin kwana uku.’”
62 И уставши поглавар свештенички рече Му: Зар ништа не одговараш што ови на тебе сведоче?
Sa’an nan babban firist ya miƙe tsaye, ya ce wa Yesu, “Ba ka da wata amsa? Shaidar da mutanen nan suke yi a kanka fa?”
63 А Исус је ћутао. И поглавар свештенички одговарајући рече Му: Заклињем те живим Богом да нам кажеш јеси ли ти Христос син Божји?
Amma Yesu ya yi shiru. Sai babban firist ya ce masa, “Na haɗa ka da Allah mai rai. Faɗa mana in kai ne Kiristi, Ɗan Allah.”
64 Рече му Исус: Ти каза. Али ја вам кажем: одселе ћете видети Сина човечијег где седи с десне стране силе и иде на облацима небеским.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake yadda ka faɗa. Sai dai ina gaya muku duka, nan gaba, za ku ga Ɗan Mutum zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a kan gizagizan sama.”
65 Тада поглавар свештенички раздре хаљине своје говорећи: Хули на Бога; шта нам требају више сведоци? Ево сад чусте хулу његову.
Sa’an nan babban firist ya yage tufafinsa ya ce, “Ya yi saɓo! Don me muke bukatar ƙarin shaidu? Ga shi, yanzu kun dai ji saɓon.
66 Шта мислите? А они одговарајући рекоше: Заслужио је смрт.
Me kuka gani?” Suka amsa, suka ce, “Ya cancanci mutuwa.”
67 Тада пљунуше Му у лице, и ударише Га по лицу, а једни Му даше и приушке
Sai suka tottofa masa miyau a fuskarsa, suka kuma bubbuge shi da hannuwansu. Waɗansu kuma suka mammare shi
68 Говорећи: Прореци нам, Христе, ко те удари?
suka ce, “Yi mana annabci, Kiristi. Wa ya buge ka?”
69 А Петар сеђаше напољу на двору, и приступи к њему једна слушкиња говорећи: и ти си био с Исусом Галилејцем.
To, Bitrus yana nan zaune a filin, sai wata yarinya baiwa, ta zo wurinsa. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu mutumin Galili.”
70 А он се одрече пред свима говорећи: Не знам шта говориш.
Amma ya yi mūsu a gabansu duka. Ya ce, “Ban san abin da kike magana ba.”
71 А кад изиђе к вратима угледа га друга, и рече онима што беху онде: и овај беше са Исусом Назарећанином.
Sa’an nan ya fito zuwa hanyar shiga, inda wata yarinya kuma ta gan shi, ta ce wa mutanen da suke can, “Wannan mutum ma yana tare da Yesu Banazare.”
72 Он опет одрече се клетвом: Не знам тог човека.
Ya sāke mūsu har da rantsuwa, yana cewa, “Ban ma san mutumin nan ba!”
73 А мало потом приступише они што стајаху и рекоше Петру: Ваистину и ти си од њих; јер те и говор твој издаје.
Bayan ɗan lokaci, sai na tsattsaye a wurin, suka hauro wurin Bitrus, suka ce, “Tabbatacce, kai ɗayansu ne, don harshen maganarka, ya tone ka.”
74 Тада се поче клети и преклињати да не зна тог човека. И одмах запева петао.
Sai ya fara la’antar kansa, yana ta rantsuwa yana ce musu, “Ban ma san mutumin nan ba!” Nan da take, sai zakara ya yi cara.
75 И опомену се Петар речи Исусове што му је рекао: Док петао не запева три пута ћеш ме се одрећи. И изашавши напоље плака горко.
Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi cewa, “Kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sani na sau uku.” Sai ya fita waje, ya yi ta kuka.

< Матеј 26 >