< Лука 2 >
1 У то време пак изиђе заповест од ћесара Августа да се препише сав свет.
A waɗancan kwanaki, Kaisar Augustus ya ba da doka cewa ya kamata a yi ƙidaya a dukan masarautar Roma.
2 Ово је био први препис за владања Киринова Сиријом.
(Wannan ce ƙidaya ta fari da aka yi a lokacin da Kwiriniyus yake gwamnar Suriya.)
3 И пођоше сви да се препишу, сваки у свој град.
Sai kowa ya koma garinsa don a rubuta shi.
4 Тада пође и Јосиф из Галилеје, из града Назарета у Јудеју у град Давидов који се зваше Витлејем, јер он беше из дома и племена Давидовог,
Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne.
5 Да се препише с Маријом, испрошеном за њега женом, која беше трудна.
Ya tafi can don a rubuta shi tare da Maryamu, wadda aka yi masa alkawari zai aura, tana kuwa da ciki.
6 И кад онамо беху, дође време да она роди.
Yayinda suke can, sai lokacin haihuwar jaririn ya yi,
7 И роди Сина свог првенца, и пови Га, и метну Га у јасле; јер им не беше места у гостионици.
ta kuwa haifi ɗanta na fari. Ta nannaɗe shi a zane ta kuma kwantar da shi cikin wani kwami, don ba su sami ɗaki a masauƙi ba.
8 И беху пастири у оном крају који чуваху ноћну стажу код стада свог.
Akwai makiyaya masu zama a fili kusa da wurin, suna tsaron garkunan tumakinsu da dare.
9 И гле, анђео Господњи стаде међу њима, и слава Господња обасја их; и уплашише се врло.
Sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, suka kuwa tsorata ƙwarai.
10 И рече им анђео: Не бојте се; јер гле, јављам вам велику радост која ће бити свему народу.
Amma mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Na kawo muku labari mai daɗi na farin ciki mai yawa ne wanda zai zama domin dukan mutane.
11 Јер вам се данас роди спас, који је Христос Господ, у граду Давидовом.
Yau a birnin Dawuda an haifa muku Mai Ceto; shi ne Kiristi Ubangiji.
12 И ето вам знака: Наћи ћете дете повито где лежи у јаслама.
Wannan zai zama alama a gare ku. Za ku tarar da jariri a nannaɗe a zane kwance a kwami.”
13 И уједанпут постаде с анђелом мноштво војника небеских, који хваљаху Бога говорећи:
Ba labari sai ga taron rundunar sama suka bayyana tare da mala’ikan, suna yabon Allah suna cewa,
14 Слава на висини Богу, и на земљи мир, међу људима добра воља.
“Ɗaukaka ga Allah a can cikin sama, a duniya kuma salama ga mutane waɗanda tagomashinsa yake bisansu.”
15 И кад анђели отидоше од њих на небо, пастири говораху један другом: Хајдемо до Витлејема, да видимо то што се тамо догодило шта нам каза Господ.
Da mala’ikun suka bar su, su suka koma sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu je Betlehem mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar mana.”
16 И дођоше брзо, и нађоше Марију и Јосифа и дете где лежи у јаслама.
Sai suka tafi da sauri, suka tarar da Maryamu da Yusuf, da kuma jaririn kwance a kwami.
17 А кад видеше, казаше све што им је казано за то дете.
Sa’ad da suka gan shi, sai suka baza maganar da aka gaya musu game da yaron,
18 И сви који чуше дивише се томе што им казаше пастири.
duk kuwa waɗanda suka ji wannan, suka yi mamaki a kan abin da makiyayan suka faɗa.
19 А Марија чуваше све речи ове и слагаше их у срцу свом.
Amma Maryamu ta riƙe dukan waɗannan abubuwa ta kuma yi ta tunaninsu a zuciyarta.
20 И вратише се пастири славећи и хвалећи Бога за све што чуше и видеше, као што им би казано.
Makiyayan kuwa suka koma, suna ɗaukaka suna kuma yabon Allah saboda dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.
21 И кад се наврши осам дана да Га обрежу, наденуше Му име Исус, као што је анђео рекао док се још није био ни заметнуо у утроби.
A rana ta takwas, da lokaci ya yi da za a yi masa kaciya, sai aka ba shi suna Yesu, sunan da mala’ika ya ba shi kafin a yi cikinsa.
22 И кад дође време да иду на молитву по закону Мојсијевом, донеше Га у Јерусалим да Га метну пред Господа,
Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji
23 (Као што је написано у закону Господњем: Да се свако дете мушко које најпре отвори материцу посвети Господу; )
(yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji”),
24 И да принесу прилог, као што је речено у закону Господњем, две грлице, или два голубића.
don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko’yan tattabarai biyu.”
25 И гле, беше у Јерусалиму човек по имену Симеун, и тај човек беше праведан и побожан, који чекаше утехе Израиљеве, и Дух Свети беше у њему.
To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.
26 И њему беше Свети Дух казао да неће видети смрт док не види Христа Господњег.
An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji.
27 И каза му Дух те дође у цркву; и кад донесоше родитељи дете Исуса да сврше за Њега закон по обичају,
Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci,
28 И он Га узе на руке своје, и хвали Бога и рече:
sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
29 Сад отпушташ с миром слугу свог, Господе, по речи својој;
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari, yanzu ka sallami bawanka lafiya.
30 Јер видеше очи моје спасење Твоје,
Gama idanuna sun ga cetonka,
31 Које си уготовио пред лицем свих народа,
wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
32 Видело, да обасја незнабошце, и славу народа Твог Израиља.
haske don bayyanawa ga Al’ummai da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”
33 И Јосиф и мати Његова чуђаху се томе што се говораше за Њега.
Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi.
34 И благослови их Симеун, и рече Марији, матери Његовој: Гле, Овај лежи да многе обори и подигне у Израиљу, и да буде знак против кога ће се говорити
Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba,
35 (А и теби самој пробошће нож душу), да се открију мисли многих срца.
ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”
36 И беше Ана пророчица, кћи Фануилова, од колена Асировог; она је остарела, а седам је година живела с мужем од девојаштва свог,
Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure,
37 И удова око осамдесет и четири године, која не одлажаше од цркве, и служаше Богу дан и ноћ постом и молитвама.
ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a.
38 И она у тај час дође, и хваљаше Господа и говораше за Њега свима који чекаху спасења у Јерусалиму.
Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.
39 И кад свршише све по закону Господњем, вратише се у Галилеју у град свој Назарет.
Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu.
40 А дете растијаше и јачаше у духу, и пуњаше се премудрости, и благодат Божија беше на Њему.
Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.
41 И родитељи Његови иђаху сваке године у Јерусалим о празнику пасхе.
Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.
42 И кад Му би дванаест година, дођоше они у Јерусалим по обичају празника;
Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.
43 И кад дане проведоше и они се вратише, оста дете Исус у Јерусалиму; и не знаде Јосиф и мати Његова;
Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.
44 Него мислећи да је с друштвом, отидоше дан хода, и стадоше Га тражити по родбини и по знанцима.
Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin’yan’uwansu da abokansu.
45 И не нашавши Га вратише се у Јерусалим да Га траже.
Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.
46 И после три дана нађоше Га у цркви где седи међу учитељима, и слуша их, и пита их,
Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi.
47 И сви који Га слушаху дивљаху се Његовом разуму и одговорима.
Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa.
48 И видевши Га зачудише се, и мати Његова рече Му: Сине! Шта учини нама тако? Ево отац твој и ја са страхом тражисмо те.
Da iyayensa suka gan shi sai suka yi mamaki. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, don me ka yi mana haka? Ni da mahaifinka duk mun damu muna nemanka.”
49 И рече им: Зашто сте ме тражили? Зар не знате да мени треба у оном бити што је Оца мог?
Sai ya ce, “Don me kuke nemana? Ba ku san cewa, dole in kasance a gidan Ubana ba?”
50 И они не разумеше речи што им рече.
Amma ba su fahimci abin da yake faɗin musu ba.
51 И сиђе с њима и дође у Назарет; и беше им послушан. И мати Његова чуваше све речи ове у срцу свом.
Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta.
52 И Исус напредоваше у премудрости и у расту и у милости код Бога и код људи.
Yesu kuwa ya yi girma, ya kuma ƙaru cikin hikima, ya kuma sami tagomashi a wurin Allah da mutane.