< Лука 14 >

1 И догоди Му се да дође у суботу у кућу једног кнеза фарисејског да једе хлеб; и они мотраху на Њега.
Wata ranar Asabaci, ya shiga gidan wani daya daga cikin shugabanin Farisawa domin cin abinci, mutane kuwa suna sa masa idanu.
2 И гле, беше пред Њим некакав човек на коме беше дебела болест.
Sai ga wani a gabansa mai ciwon fara.
3 И одговарајући Исус рече законицима и фарисејима говорећи: Је ли слободно у суботу исцељивати?
Yesu ya tambaye masanan attaura da Farisawa, “Ya halata a wakar a ranan Asabaci, ko a'a?”
4 А они оћутеше. И дохвативши га се исцели га и отпусти.
Amma suka yi shiru. Yesu kuwa ya kama shi, ya warkar da shi, ya kuma sallame shi.
5 И одговарајући рече им: Који од вас не би свог магарца или вола да му падне у бунар одмах извадио у дан суботни?
Sai yace masu, “Wanene a cikinku in yana da jaki ko takarkari ya fadi a rijiya ran Asabaci, ba zai fitar da shi nan da nan ba?”
6 И не могоше Му одговорити на то.
Sai suka kasa ba da amsar wadannan abubuwa.
7 А гостима каза причу, кад опази како избираху зачеља, и рече им:
Sa'adda Yesu ya lura da yadda wadanda aka gayyato sun zabi mazaunan alfarma, sai ya ba su misali yana ce masu,
8 Кад те ко позове на свадбу, не седај у зачеље, да не буде међу гостима ко старији од тебе;
“Sa'adda wani ya gayyace ka zuwa bikin aure, kada ka zauna a wuri mai daraja, domin yana yiwuwa an gayyaci wani wanda ya fi ka daraja.
9 И да не би дошао онај који је позвао тебе и њега, и рекао ти: Подај место овоме: и онда ћеш са стидом сести на ниже место.
Sa'adda wanda ya gayyace ku duka biyu ya zo, zai ce maka, 'Ka ba mutumin nan wurinka,' sa'annan a kunyace za ka koma mazauni mafi kaskanci.
10 Него кад те ко позове, дошавши седи на последње место, да ти каже кад дође онај који те позва: Пријатељу! Помакни се више; тада ће теби бити част пред онима који седе с тобом за трпезом.
Amma idan an gayyace ka biki, sai ka je ka zauna a wuri mafi kaskanci, domin idan wanda ya gayyace ka ya zo, yana iya ce maka, 'Aboki, hawo nan mana'. Sannan za ka sami girma kenan a gaban dukan wadanda kuke zaune tare a kan teburi.
11 Јер сваки који се подиже, понизиће се; а који се понижује, подигнуће се.
Duk wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, wanda ya kaskantar da kansa, kuma daukaka shi za a yi”.
12 А и ономе што их је позвао рече: Кад дајеш обед или вечеру, не зови пријатеље своје, ни браћу своју, ни рођаке своје, ни суседе богате, да не би и они тебе кад позвали и вратили ти;
Yesu ya ce wa mutumin da ya gayyace shi, “Idan za ka gayyaci mutum cin abinci ko biki, kada ka gayyaci abokanka, ko 'yan'uwanka, ko danginka, ko makwabtanka masu arziki, kamar yadda suna iya gayyatar ka, sai ya zama an maida maka.
13 Него кад чиниш гозбу, зови сиромахе, кљасте, хроме, слепе;
Amma idan za ka kira biki sai ka gayyace matalauta, da nakasassu, da guragu, da makafi,
14 И благо ће ти бити што ти они не могу вратити; него ће ти се вратити о васкрсењу праведних.
za ka kuwa sami albarka da yake ba su da hanyar saka maka. Gama za a saka maka a ranar tashin masu adalci.”
15 А кад чу то неки од оних што сеђаху с Њим за трпезом рече Му: Благо ономе који једе хлеба у царству Божијем!
Da daya daga cikin wadanda ke zama akan teburi da Yesu ya ji wadannan abubuwa, sai ya ce masa, “Albarka ta tabbata ga wanda zai ci abinci a mulkin Allah!”
16 А Он му рече: Један човек зготови велику вечеру, и позва многе;
Amma Yesu ya ce masa, “Wani mutum ne ya shirya babban biki ya gayyaci mutane da yawa.
17 И кад би време вечери, посла слугу свог да каже званима: Хајдете, јер је већ све готово.
Da lokacin biki ya yi, sai ya aiki bawansa ya ce wa wadanda aka gayyata, “Ku zo, duk an shirya kome.”
18 И почеше се изговарати сви редом; први му рече: Купих њиву, и ваља ми ићи да је видим; молим те изговори ме.
Sai dukansu, suka fara kawo dalilai. Na farko ya ce masa, 'Na sayi gona, lalle ne in je in gan ta. Ina rokonka ka dauke mani.'
19 И други рече: Купих пет јармова волова, и идем да их огледам; молим те, изговори ме.
Sai wani ya ce, 'Na sayi shanu garma biyar, ina so in gwada su. Ina ronkan ka, ka dauke mani.'
20 И трећи рече: Ожених се, и зато не могу доћи.
Wani mutum kuma ya ce, 'Na yi aure, don haka ba zan iya zuwa ba.'
21 И дошавши слуга тај каза ово господару свом. Тада се расрди домаћин и рече слузи свом: Иди брзо на раскршћа и улице градске, и доведи амо сиромахе, и кљасте, и богаљасте, и слепе.
Da bawan ya zo ya fadi wa maigidansa wadannan abubuwa, sai maigidan yayi fushi, ya ce wa bawansa, jeka da sauri ka bi cikin titunan birni da kwararo-kwararo, ka kawo gajiyayyu, da nakasassu, da makafi, da guragu.'
22 И рече слуга: Господару, учинио сам како си заповедио, и још места има.
Sai bawan ya ce, 'Maigida, abin da ka umarta an gama, amma har yanzu da sauran wuri.”
23 И рече господар слузи: Изиђи на путеве и међу ограде, те натерај да дођу да ми се напуни кућа.
Sai maigidan ya ce wa bawan, 'Jeka, ka bi kwararo-kwararo da hanyoyin karkara, ka rinjayi mutane su shigo, don a cika gidana.
24 Јер вам кажем да ниједан од оних званих људи неће окусити моје вечере. Јер је много званих, али је мало изабраних.
Gama ina gaya maku, babu ko daya daga cikin mutanen da na gayyata da farko da zai dandana bikina.”
25 Иђаше пак с Њим мноштво народа, и обазревши се рече им:
Ana nan, taron suna tafiya tare da shi, sai ya juya ya ce masu,
26 Ако ко дође к мени, а не мрзи на свог оца, и на матер, и на жену, и на децу, и на браћу, и на сестре и на саму душу своју, не може бити мој ученик.
“Duk mai zuwa wurina amma bai ki mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa, da 'ya'yansa, da 'yan'uwansa maza da mata ba - I, har da ransa ma, ba zai iya zama almajirina ba.
27 И ко не носи крст свој и за мном не иде, не може бити мој ученик.
Duk wanda bai dauki gijiyensa ya biyo ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
28 И који од вас кад хоће да зида кулу не седне најпре и не прорачуна шта ће га стати, да види има ли да може довршити?
Wanene a cikinku wanda yake niyyar gina bene, da ba zai zauna ya yi lissafin abin da zai kashe ba tun da farko, ko yana da ishashen kudi da zai iya kare aikin?
29 Да не би, кад постави темељ и не узможе довршити, сви који гледају стали му се ругати
Kada ya zama bayan da ya sa harsashin ginin, ya kasa gamawa, har duk wadanda suka gani su fara yi masa ba'a,
30 Говорећи: Овај човек поче зидати, и не може да доврши.
su rika cewa, ga mutumin nan ya fara gini amma ya kasa gamawa.'
31 Или који цар кад пође с војском да се побије с другим царем не седне најпре и не држи већу може ли с десет хиљада срести оног што иде на њега са двадесет хиљада?
Ko kuwa wanne sarki ne, in za shi je yaki da wani sarki, da ba zai zauna da farko ya yi shawara ya ga ko shi mai jarumawa dubu goma zai iya karawa da dayan sarkin mai jarumawa dubu ashirin ba?
32 Ако ли не може, а он пошаље посленике док је овај још далеко и моли да се помире.
In kuwa ba zai iya ba, to tun wancan yana nesa, sai ya aiki wakili ya kuma tambayo sharudan salama.
33 Тако дакле сваки од вас који се не одрече свега што има не може бити мој ученик.
Haka ma, ba wani a cikinku wanda bai rabu da duk abin da ya mallaka ba, da zai iya zama almajirina.”
34 Со је добра, али ако со обљутави, чим ће се осолити?
“Gishiri abu ne mai kyau, amma idan gishiri ya sane, da me za a dadada shi?
35 Нити је потребна у земљу ни у гној; него је проспу напоље. Ко има уши да чује нека чује.
Ba shi da wani anfani a kasa, ko ya zama taki. Sai dai a zubar kawai. Duk mai kunnen ji, ya ji.”

< Лука 14 >