< 3 Мојсијева 24 >
1 Још рече Господ Мојсију говорећи:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Заповеди синовима Израиљевим нека ти донесу уље маслиново чисто, цеђено, за видело, да жишци горе вазда.
“Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
3 Пред завесом сведочанства у шатору од састанка Арон ће их намештати да горе од вечера до јутра пред Господом вазда законом вечним од колена до колена.
Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
4 На свећњак чисти намештаће жишке пред Господом вазда.
Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
5 И узми белог брашна, и испеци дванаест колача, сваки колач да буде од две десетине ефе.
“Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
6 И постави их у два реда, по шест у један ред, на чистом столу пред Господом.
A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
7 И на сваки ред метни када чистог, да буде за сваки хлеб спомен, жртва огњена Господу.
Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
8 Сваке суботе нека их поставља свештеник пред Господом вазда узимајући од синова Израиљевих законом вечним.
Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
9 И биће Аронови и синова његових, који ће јести на месту светом, јер им је светиња над светињама од огњених жртава Господњих законом вечним.
Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
10 А изађе син једне Израиљке, коме је отац био Мисирац, међу синове Израиљеве, и свади се у логору син жене Израиљке с неким Израиљцем.
To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
11 И псујући син жене Израиљке похули на име Божије, те га доведоше к Мојсију; а мати му беше по имену Саломита, кћи Давријина, од племена Дановог.
Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
12 И метнуше га у затвор докле им се каже шта ће чинити с њим по речи Господњој.
Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
13 А Господ рече Мојсију говорећи:
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
14 Изведи тог псовача напоље из логора, и нека сви који су чули метну руке своје на главу његову, и нека га сав народ заспе камењем.
“Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
15 А синовима Израиљевим кажи и реци: Ко би год похулио Бога свог, носиће грех свој.
Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
16 Ко би ружио име Господње, да се погуби, сав народ да га заспе камењем; и дошљак и домородац који би ружио име Господње, да се погуби.
duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
17 И ко убије човека, да се погуби.
“‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
18 А ко убије живинче, нека врати друго, живинче за живинче.
Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
19 И ко рани ближњег свог, како учини тако да му буде:
Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
20 Улом за улом, око за око, зуб за зуб; како оштети тело човеку, онако да му се учини.
karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
21 Ко убије живинче, да врати друго; али ко убије човека, да се погуби.
Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
22 Закон да вам је један, дошљаку да буде као и рођеном у земљи. Јер сам ја Господ Бог ваш.
Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
23 И Мојсије каза синовима Израиљевим, а они изведоше псовача напоље из логора, и засуше га камењем; и учинише синови Израиљеви како Господ заповеди Мојсију.
Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.