< Књига пророка Јоила 1 >
1 Реч Господња која дође Јоилу сину Фатуиловом.
Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
2 Чујте, старци; слушајте, сви становници земаљски; је ли овако шта било за вашег времена или за времена ваших отаца?
Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
3 Приповедајте то синовима својим, и синови ваши својим синовима, и њихови синови потоњем колену.
Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
4 Шта оста иза гусенице изједе скакавац, и шта оста иза скакавца изједе хрушт, и шта оста иза хрушта изједе црв.
Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
5 Отрезните се, пијанице, и плачите; и ридајте сви који пијете вино, за новим вином, јер се оте из уста ваших.
Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
6 Јер дође на земљу моју силан народ и небројен; зуби су му као у лава и кутњаци као у лавице.
Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
7 Потре винову лозу моју, и смокве моје покида, сасвим их огули и побаца, те им се гране беле.
Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
8 Ридај као младица опасана кострећу за мужем младости своје.
Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
9 Неста дара и налива из дома Господњег; туже свештеници, слуге Господње.
Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
10 Опусте поље, тужи земља; јер је потрвено жито, усахло вино, нестало уља.
Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
11 Стидите се ратари, ридајте виноградари, пшенице ради и јечма ради, јер пропаде жетва на њиви;
Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
12 Лоза посахну и смоква увену; шипак и палма и јабука и сва дрвета пољска посахнуше, јер неста радости између синова људских.
Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
13 Опашите се и плачите свештеници; ридајте који служите олтару, дођите, ноћујте у кострети, слуге Бога мог; јер се уноси у дом Бога вашег дар и налив.
Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
14 Наредите пост, огласите празник, скупите старешине, све становнике земаљске, у дом Господа Бога свог, и вапите ка Господу:
Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
15 Јаох дана! Јер је близу дан Господњи, и доћи ће као погибао од Свемогућег.
Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
16 Није ли нестало хране испред очију наших, радости и весеља из дома Бога нашег?
Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
17 Семе иструхну под грудама својим, пусте су житнице, разваљене спреме, јер посахну жито.
Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
18 Како уздише стока! Како су се смела говеда! Јер немају паше; и овце гину.
Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
19 К Теби, Господе, вичем, јер огањ сажеже паше у пустињи, и пламен попали сва дрвета у пољу.
A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
20 И зверје пољско погледа за тобом, јер усахнуше потоци водени и огањ сажеже паше у пустињи.
Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.