< Књига о Јову 12 >
2 Да, ви сте људи, и с вама ће умрети мудрост.
“Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
3 И ја имам срце као и ви, нити сам гори од вас; и у кога нема тога?
Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
4 На подсмех сам пријатељу свом, који кад зове Бога одазове му се; на подсмех је праведни и добри.
“Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
5 Бачен је луч по мишљењу срећног онај који хоће да попузне.
Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
6 Мирне су колибе лупешке, и без страха су који гневе Бога, њима Бог даје све у руке.
Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
7 Запитај стоку, научиће те; или птице небеске, казаће ти.
“Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
8 Или се разговори са земљом, научиће те, и рибе ће ти морске приповедити.
Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
9 Ко не зна од свега тога да је рука Господња то учинила?
Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
10 Коме је у руци душа свега живог и дух сваког тела човечијег.
Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
11 Не распознаје ли ухо речи као што грло куша јело?
Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
12 У старца је мудрост, и у дугом веку разум.
Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
13 У Њега је мудрост и сила, у Њега је савет и разум.
“Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
14 Гле, Он разгради, и не може се опет саградити; затвори човека, и не може се отворити.
Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
15 Гле, устави воде, и пресахну; пусти их, и испреврћу земљу.
Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
16 У Њега је јачина и мудрост, Његов је који је преварен и који вара.
Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
17 Он доводи саветнике у лудило, и судије обезумљује.
Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
18 Он разрешује појас царевима, и опасује бедра њихова.
Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
19 Он доводи кнезове у лудило, и обара јаке.
Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
20 Он узима беседу речитима, и старцима узима разум.
Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
21 Он сипа срамоту на кнезове, и распасује јунаке.
Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
22 Он открива дубоке ствари испод таме, и изводи на видело сен смртни.
Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
23 Он умножава народе и затире их, расипа народе и сабира.
yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
24 Он одузима срце главарима народа земаљских, и заводи их у пустињу где нема пута,
Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
25 Да пипају по мраку без видела, и чини да тумарају као пијани.
Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.