< Књига пророка Исаије 54 >

1 Весели се, нероткињо која не рађаш, запевај и покликни ти, која не трпиш муке од порођаја, јер пуста има више деце него ли она која има мужа, вели Господ.
“Ki rera, ya ke bakararriya, ke da ba ki taɓa haihuwa ba; ki ɓarke da waƙa, ki yi sowa don farin ciki, ke da ba ki taɓa naƙuda ba; domin’ya’yan mace mai kaɗaici sun fi na mai miji yawa,” in ji Ubangiji.
2 Рашири место шатора свог, и завесе стана твог нека се разастру, не брани, продужи ужа своја, коље своје утврди.
“Ki fadada wurin tentinki, ki miƙe labulen tentinki da fāɗi, kada ki janye; ƙara tsawon igiyoyinta, ki kuma ƙara ƙarfin turakunta.
3 Јер ћеш се надесно и налево распространити, и семе ће твоје наследити народе, и пусте ће градове населити.
Gama za ki fadada zuwa dama da hagu; zuriyarki za su kori al’ummai su kuma zauna a kufan biranensu.
4 Не бој се, јер се нећеш осрамотити, и немој се стидети, јер нећеш бити прекорна, него ћеш заборавити срамоту младости своје, и прекора удовиштва свог нећеш се више сећати.
“Kada ki ji tsoro; ba za ki sha kunya ba. Kada ki ji tsoron wulaƙanci, ba za a ƙasƙantar da ke ba. Za ki manta da kunyar ƙuruciyarki ba kuwa za ki tuna da zargin zaman gwauruwarki ba.
5 Јер ти је муж Творац твој, име Му је Господ над војскама, и Избавитељ ти је Светац Израиљев, Бог свој земљи зваће се.
Gama Mahaliccinki shi ne mijinki, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ne Mai Fansarki; ana ce da shi Allahn dukan duniya.
6 Јер као жену остављену и у духу ожалошћену дозва те Господ, и као младу жену пуштену, говори Господ.
Ubangiji zai kira sai ka ce ke mace ce da aka yashe ta tana kuma damuwa a ranta, macen da ta yi aure a ƙuruciya, sai kawai aka ƙi ta,” in ji Allahnki.
7 Замало оставих те, али с великом милошћу прибраћу те.
“Gama a ɗan ƙanƙanen lokaci na rabu da ke, amma da ƙauna mai zurfi zan sāke dawo da ke.
8 У малом гневу сакрих за час лице своје од тебе, али ћу те вечном милошћу помиловати, вели Избавитељ твој Господ.
Cikin fushi mai zafi na ɓoye fuskata daga gare ki na ɗan lokaci, amma da madawwamin alheri zan ji tausayinki,” in ji Ubangiji Mai Fansarki.
9 Јер ми је то као потоп Нојев: јер као што се заклех да потоп Нојев неће више доћи на земљу, тако се заклех да се нећу разгневити на те нити ћу те карати.
“A gare ni wannan ya yi kamar kwanakin Nuhu, sa’ad da na rantse cewa ruwan Nuhu ba za su ƙara rufe duniya ba. Yanzu fa na rantse ba zan yi fushi da ke ba, ba zan ƙara tsawata miki kuma ba.
10 Ако ће се и горе помакнути и хумови се поколебати, опет милост моја неће се одмакнути од тебе, и завет мира мог неће се поколебати, вели Господ, који ти је милостив.
Ko da duwatsu za su girgiza a kuma tumɓuke tuddai, duk da haka madawwamiyar ƙaunata da nake yi miki ba za tă jijjigu ba ba kuwa za a kawar da alkawarin salamata ba,” in ji Ubangiji, wanda ya ji tausayinki.
11 Невољнице, коју ветар размеће, која си без утехе, ево ја ћу наместити камење твоје на мрамору порфирном, и основаћу те на сафирима.
“Ya ke birni mai shan azaba, wadda hadari ya bulale ki ba a kuma ta’azantar da ke ba, zan gina ke da duwatsu turkuwoyis, zan kafa harsashenki da duwatsun saffaya.
12 И начинићу ти прозоре од кристала, и врата од камена рубина, и све међе твоје од драгог камења.
Zan gina hasumiyarki da jan yakutu, ƙofofinki kuma da duwatsu masu haske, dukan katangarki kuma da duwatsu masu daraja.
13 А синови ће твоји сви бити научени од Господа, и обилан мир имаће синови твоји.
Ubangiji zai koya wa dukan’ya’yanki maza, da girma kuma salamar’ya’yanki zai zama.
14 Правдом ћеш се утврдити, далеко ћеш бити од насиља, те се нећеш бојати, и од страхоте, јер ти се неће приближити.
Da adalci za a kafa ke. Zalunci zai yi nesa da ke; ba za ki kasance da wani abin da za ki ji tsoro ba. Za a kawar da duk wani abin banrazana; ba zai yi kusa da ke ba.
15 Гле, биће их који ће се сабирати на те, али неће бити од мене; који се год саберу на те, пашће.
In wani ya far miki, ba daga wurina ba ne; duk wanda ya far miki zai miƙa wuya gare ki.
16 Гле, ја сам створио ковача који распаљује угљевље и вади оруђе за свој посао, ја сам створио и крвника да убија.
“Duba, ni ne wanda na halicci maƙeri wanda yake zuga garwashi ya zama harshen wuta ya kuma ƙera makamin da ya dace da aikinsa. Ni ne kuma na halicci mai hallakarwa ya yi ɓarna;
17 Никакво оружје начињено против тебе неће бити срећно, и сваки језик који се подигне на те на суду сапрећеш. То је наследство слуга Господњих и правда њихова од мене, вели Господ.
ba makamin da aka ƙera don yă cuce ki da zai yi nasara, za ki kuma mayar da magana ga duk wanda ya zarge ki. Wannan ne gādon bayin Ubangiji, kuma wannan ita ce nasararsu daga gare ni,” in ji Ubangiji.

< Књига пророка Исаије 54 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark