< Књига пророка Исаије 40 >
1 Тешите, тешите народ мој, говори Бог ваш.
Ta’aziyya, ku ta’azantu mutanena, in ji Allahnku.
2 Говорите Јерусалиму љубазно, и јављајте му да се навршио рок његов, да му се безакоње опростило, јер је примио из руке Господње двојином за све грехе своје.
Yi magana mai kwantar da rai ga Urushalima, ku kuma furta mata cewa aiki mai zafinta ya isa, cewa an fanshi zunubinta, cewa ta karɓi daga hannun Ubangiji ninki biyu saboda dukan zunubanta.
3 Глас је некога који виче: Приправите у пустињи пут Господњи, поравните у пустоши стазу Богу нашем.
Muryar wani tana kira cewa, “A cikin hamada ku shirya hanya saboda Ubangiji; ku miƙe manyan hanyoyi domin Allahnmu a cikin jeji.
4 Све долине нека се повисе, и све горе и брегови нека се слегну, и што је криво нека буде право, и неравна места нека буду равна.
Za a cike kowane kwari, a baje kowane dutse da kowane tudu; za a mayar da karkatattun wurare su zama sumul, munanan wurare kuma su zama da kyau.
5 И јавиће се слава Господња, и свако ће тело видети; јер уста Господња говорише.
Za a kuma bayyana ɗaukakar Ubangiji, dukan mutane kuwa za su gan ta. Gama Ubangiji da kansa ne ya yi magana.”
6 Глас говори: Вичи. И рече: Шта да вичем? Да је свако тело трава и све добро његово као цвет пољски.
Muryar tana cewa, “Ka yi shela.” Na kuwa ce, “Me zan yi shelar?” “Dukan mutane kamar ciyawa suke, kuma dukan ɗaukakarsu kamar furannin jeji ne.
7 Суши се трава, цвет опада кад дух Господњи дуне на њ; доиста је народ трава.
Ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, domin Ubangiji ya hura iska a kansu. Tabbatacce mutane ciyawa ne.
8 Суши се трава, цвет опада; али реч Бога нашег остаје довека.
Hakika ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, amma maganar Allahnmu tana nan daram har abada.”
9 Изађи на високу гору, Сионе, који јављаш добре гласове; подигни силно глас свој, Јерусалиме, који јављаш добре гласове; подигни, не бој се. Кажи градовима Јудиним: Ево Бога вашег.
Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Sihiyona, ka haura a bisa dutse. Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Urushalima, ka tā da muryarka ka yi ihu, ka ɗaga ta, kada ka ji tsoro; faɗa wa garuruwan Yahuda, “Ga Allahnku!”
10 Ево, Господ Бог иде на јаког, и мишица ће Његова овладати њим; ево плата је његова код Њега и дело његово пред Њим.
Duba, Ubangiji Mai Iko Duka yana zuwa da iko, hannunsa kuma yana yin mulki dominsa. Duba, ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa kuma na rakiyarsa.
11 Као пастир пашће стадо своје; у наручје своје сабраће јагањце, и у недрима ће их носити, а дојилице ће водити полако.
Yakan lura da garkensa kamar makiyayi. Yakan tattara tumaki wuri ɗaya yă riƙe su kurkusa da ƙirjinsa; a hankali kuma yakan bi da masu ba da mama.
12 Ко је измерио воду грстима својим и небеса премерио пеђу? Ко је мером измерио прах земаљски, и горе измерио на мерила и брегове на потег?
Wane ne ya auna ruwaye a tafin hannunsa, ko kuwa ya gwada tsawon sammai da fāɗin tafin hannunsa? Wane ne ya riƙe ƙurar ƙasa a kwando, ko kuwa ya auna nauyin duwatsu a magwaji, tuddai kuma a ma’auni?
13 Ко је управљао Духом Господњим? Или Му био саветник и научио Га?
Wane ne ya fahimci zuciyarUbangiji, ko kuwa ya koya masa a matsayin mashawarcinsa?
14 С ким се договарао и ко Га је уразумио и научио путу суда, и научио Га знању и показао Му пут разума?
Wane ne Ubangiji ya nemi shawararsa don yă ganar da shi, wane ne kuma ya koya masa hanyar da ta dace? Wane ne ya koya masa sani ko ya nuna masa hanyar fahimta?
15 Гле, народи су као кап из ведра, и као прашка на мерилима броје се; гле, премешта острва као прашак.
Tabbatacce al’ummai suna kama da ɗigon ruwa a cikin bokiti an ɗauke su a matsayin ƙura a kan magwaji; yakan auna tsibirai sai ka ce ƙura mai laushi.
16 Ни Ливан не би био доста за огањ, и животиње његове не би биле доста за жртву паљеницу.
Itatuwan Lebanon ba su isa a yi wutar bagade da su ba, balle dabbobinsa su isa yin hadayun ƙonawa.
17 Сви су народи као ништа пред Њим, мање неголи ништа и таштина вреде Му.
A gabansa dukan al’ummai ba kome ba ne; ya ɗauke su ba a bakin kome ba kuma banza ne kurum.
18 С ким ћете дакле изједначити Бога? И какву ћете Му прилику наћи?
To, ga wane ne za ka kwatanta Allah? Wace siffa za ka kwatanta shi da ita?
19 Уметник лије лик, и златар га позлаћује, и верижице сребрне лије.
Gunki dai, maƙeri kan yi zubinsa, maƙerin zinariya kuma yă ƙera shi da zinariya yă kuma sarrafa masa sarƙoƙin azurfa.
20 А ко је сиромах, те нема шта принети, бира дрво које не труне, и тражи вештог уметника да начини резан лик, који се не помиче.
Mutumin da talauci ya sha kansa da ba zai iya miƙa irin hadayar nan ba kan zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba. Yakan nemi gwanin sassaƙa don yă sassaƙa masa gunkin da ba zai fāɗi ba.
21 Не знате ли? Не чујете ли? Не казује ли вам се од искона? Не разумете ли од темеља земаљских?
Ba ku sani ba? Ba ku taɓa ji ba? Ba a faɗa muku daga farko ba? Ba ku fahimta ba tun kafawar duniya?
22 Он седи над кругом земаљским, и њени су Му становници као скакавци; Он је разастро небеса као платно и разапео их као шатор за стан.
Yana zaune a kursiyi a bisa iyakar duniya, kuma mutanenta suna kama da fāra. Ya miƙa sammai kamar rumfa, ya kuma shimfiɗa su kamar tentin da za a zauna a ciki.
23 Он обраћа кнезове у ништа, судије земаљске чини да су као таштина.
Yakan mai da sarakuna ba kome ba yă mai da masu mulkin wannan duniya wofi.
24 Као да нису посађени ни посејани, и као да им се стабло није укоренило у земљи, чим дуне на њих, посахну, и вихор као плеву разнесе их.
Ba da jimawa ba bayan an shuka su, ba da jimawa ba bayan an dasa su, ba da jimawa ba bayan sun yi saiwa a ƙasa, sai yă hura musu iska su yanƙwane, guguwa kuma ta kwashe su kamar yayi.
25 С ким ћете ме дакле изједначити да бих био као он? вели Свети.
“Ga wa za ku kwatanta ni? Ko kuwa wa yake daidai da ni?” In ji Mai Tsarkin nan.
26 Подигните горе очи своје и видите; ко је то створио? Ко изводи војску свега тога на број и зове свако по имену, и велике ради силе Његове и јаке моћи не изостаје ниједно?
Ku ɗaga idanunku ku duba sammai. Wane ne ya halicce dukan waɗannan? Wane ne ya fitar da rundunar taurari ɗaya-ɗaya, yana kiransu, kowanne da sunansa. Saboda ikonsa mai girma da kuma ƙarfinsa mai girma, babu ko ɗayansu da ya ɓace.
27 Зашто говориш, Јакове, и кажеш, Израиљу: Сакривен је пут мој од Господа, и ствар моја не излази пред Бога мог?
Ya Yaƙub, ya Isra’ila, me ya sa kake ce kana kuma gunaguni cewa, “Hanyata tana a ɓoye daga Ubangiji; Allah bai kula da abin da yake damuna ba”?
28 Не знаш ли? Ниси ли чуо да Бог вечни Господ, који је створио крајеве земаљске, не сустаје нити се утруђује? Разуму Његовом нема мере.
Ba ku sani ba? Ba ku ji ba? Ubangiji madawwamin Allah ne, Mahaliccin iyakokin duniya. Ba zai taɓa gaji ko yă kasala ba, kuma fahimtarsa ya wuce gaban ganewar mutum.
29 Он даје снагу уморном, и нејаком умножава крепост.
Yakan ba da ƙarfi ga waɗanda suka gaji yă kuma ƙara ƙarfi ga marasa ƙarfi.
30 Деца се море и сустају, и младићи падају;
Ko matasa ma kan gaji su kuma kasala, samari kuma kan yi tuntuɓe su fāɗi;
31 Али који се надају Господу, добијају нову снагу, подижу се на крилима као орлови, трче и не сустају, ходе и не море се.
amma waɗanda suka dogara ga Ubangiji za su sabunta ƙarfinsu. Za su yi firiya da fikafikai kamar gaggafa; za su kuma yi gudu ba kuwa za su gaji ba, za su yi tafiya ba kuwa za su kasala ba.