< Књига пророка Исаије 28 >
1 Тешко гиздавом венцу пијаница Јефремових, увелом цвету красног накита њиховог, који су уврх родног дола, пијани од вина!
Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
2 Гле, у Господа има неко јак и силан као пљусак од града, као олуја која све ломи, као поплава силне воде, кад навали, обориће све на земљу руком.
Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
3 Ногама ће се изгазити гиздави венац, пијанице Јефремове.
Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
4 И увели цвет красног накита њиховог, што је уврх родног дола, биће као воће узрело пре лета, које чим ко види, узме у руку и поједе.
Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
5 У оно ће време Господ над војскама бити славна круна и дичан венац остатку народа свог,
A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
6 И дух суда ономе који седи да суди, и сила онима који узбијају бој до врата.
Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
7 Али се и они заносе од вина, и посрћу од силовитог пића: свештеник и пророк заносе се од силовитог пића, освојило их је вино, посрћу од силовитог пића, заносе се у пророковању, спотичу се у суђењу.
Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
8 Јер су сви столови пуни бљувотине и нечистоће, нема места чистог.
Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
9 Кога ће учити мудрости, и кога ће упутити да разуме науку? Децу, којој се не даје више млеко, која су одбијена од сисе?
“Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
10 Јер заповест по заповест, заповест по заповест, правило по правило, правило по правило, овде мало, онде мало даваше се.
Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
11 Зато ће неразумљивом беседом и туђим језиком говорити том народу;
To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
12 Јер им рече: Ово је починак, оставите уморног да почине; ово је одмор; али не хтеше послушати.
waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
13 И биће им реч Господња, заповест по заповест, заповест по заповест, правило по правило, правило по правило, мало овде, мало онде, да иду и падају наузнако и разбију се, и да се заплету у замке и ухвате.
Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
14 Зато слушајте реч Господњу, људи подсмевачи, који владате народом што је у Јерусалиму.
Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
15 Што рекосте: Ухватисмо веру са смрћу, и уговорисмо с гробом; кад зађе бич као поводањ, неће нас дохватити, јер од лажи начинисмо себи уточиште, и за превару заклонисмо се; (Sheol )
Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol )
16 Зато овако вели Господ Господ: Ево, ја мећем у Сиону камен, камен изабран, камен од угла, скупоцен, темељ тврд; ко верује неће се плашити.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
17 И извршићу суд по правилу и правду по мерилима; и град ће потрти лажно уточиште и вода ће потопити заклон.
Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
18 И вера ваша са смрћу уништиће се, и уговор ваш с гробом неће остати, а кад зађе бич као поводањ, потлачиће вас. (Sheol )
Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol )
19 Чим зађе, однеће вас, јер ће залазити свако јутро, дању и ноћу, и кад се чује вика, биће сам страх.
A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
20 Јер ће одар бити кратак да се човек не може пружити, и покривач узак да се не може умотати.
wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
21 Јер ће Господ устати као на гори Ферасиму, разгневиће се као у долу гаваонском, да учини дело своје, необично дело своје, да сврши посао свој, необичан посао свој.
Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
22 Немојте се дакле више подсмевати да не постану јачи окови ваши, јер чух од Господа Господа над војскама погибао одређену свој земљи.
Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
23 Слушајте, и чујте глас мој, пазите и чујте беседу моју.
Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
24 Оре ли орач сваки дан да посеје? Или бразди и повлачи њиву своју?
Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
25 Кад поравни одозго, не сеје ли грахор и ким? И не меће ли пшеницу на најбоље место, и јечам на згодно место, и крупник на његово место?
Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
26 И Бог га његов учи и упућује како ће радити.
Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
27 Јер се грахор не врше браном, нити се точак колски обрће по киму, него се цепом млати грахор и ким прутом.
Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
28 Пшеница се врше, али неће једнако врећи нити ће је сатрти точком колским на зупцима раздробити.
Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
29 И то долази од Господа над војскама, који је диван у савету, велик у мудрости.
Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.