< 1 Мојсијева 50 >
1 Тада Јосиф паде на лице оцу свом, и плака над њим целујући га.
Yusuf kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya kuma sumbace shi.
2 И заповеди Јосиф слугама својим лекарима да мирисима помажу оца његовог; и лекари помазаше мирисима Израиља.
Sa’an nan Yusuf ya umarci masu maganin da suke yin masa hidima, su shafe mahaifinsa Isra’ila da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe shi da maganin hana ruɓa.
3 И наврши му се четрдесет дана, јер толико дана треба оним које помажу мирисима; и плакаше за њим Мисирци седамдесет дана.
Suka ɗauki kwana arba’in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi makoki dominsa kwana saba’in.
4 А кад прођоше жалосни дани, рече Јосиф домашњима Фараоновим говорећи: Ако сам нашао милост пред вама, говорите Фараону и реците:
Sa’ad da kwanakin makoki suka wuce, sai Yusuf ya ce wa iyalin gidan Fir’auna, “In na sami tagomashi a idanunku, ku yi magana da Fir’auna domina. Ku faɗa masa,
5 Отац ме је мој заклео говорећи: Ево, ја ћу скоро умрети; у гробу мом, који ископах у земљи хананској, онде ме погреби. Па сада да идем да погребем оца свог, а после ћу опет доћи.
‘Mahaifina ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, “Ina gab da mutuwa, ka binne ni a kabarin da na haƙa wa kaina a ƙasar Kan’ana.” Yanzu fa bari in haura in binne mahaifina, sa’an nan in dawo.’”
6 А Фараон му рече: Иди, погреби оца свог како те је заклео.
Fir’auna ya ce, “Haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya sa ka rantse za ka yi.”
7 И отиде Јосиф да погребе оца свог; и с њим пођоше све слуге Фараонове, старешине од дома његовог и све старешине од земље мисирске.
Saboda haka Yusuf ya haura don yă binne mahaifinsa. Dukan hafsoshin Fir’auna suka yi masa rakiya tare da manyan mutanen gidan Fir’auna, da kuma dukan manyan mutanen Masar
8 И сав дом Јосифов и браћа његова и дом оца његовог; само децу своју и овце своје и говеда своја оставише у земљи гесемској.
da kuma dukan membobin gidan Yusuf, da’yan’uwansa da kuma waɗanda suke na gidan mahaifinsa. Yara kaɗai da garkunansu da kuma shanunsu ne aka bari a Goshen.
9 А пође с њим кола и коњаника толико да беше војска врло велика.
Kekunan yaƙi da mahayan dawakai su ma suka haura tare da shi. Babbar ƙungiya jama’a ce ƙwarai.
10 А кад дођоше на гумно Атадово, које је с оне стране Јордана, плакаше онде много и врло тужно; и Јосиф учини жалост за оцем својим за седам дана.
Sa’ad da suka kai masussukar Atad, kusa da Urdun, sai suka yi kuka da ƙarfi da kuma mai zafi, a can Yusuf ya yi makoki kwana bakwai saboda mahaifinsa.
11 А људи из оне земље, Хананејци, кад видеше плач на гумну Атадовом, рекоше: У великој су жалости Мисирци. Зато прозваше оно место с оне стране Јордана Жалост мисирска.
Sa’ad da Kan’aniyawa waɗanda suke zama a can suka ga makokin a masussukan Atad, sai suka ce, “Masarawa suna bikin makoki na musamman.” Shi ya sa ake kira wannan wurin da yake kusa da Urdun, Abel-Mizrayim.
12 И учинише му синови његови како им беше заповедио.
Haka fa’ya’yan Yaƙub maza suka yi yadda ya umarce su.
13 Однесоше га синови његови у земљу хананску, и погребоше га у пећини на њиви макпелској, коју купи Аврам да има свој гроб у Ефрона Хетејина према Мамрији.
Suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan’ana suka kuma binne shi a kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, ya zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
14 И погребавши оца свог врати се Јосиф у Мисир и браћа његова и сви који беху изашли с њим да погребу оца његовог.
Bayan ya binne mahaifinsa, sai Yusuf ya koma Masar, tare da’yan’uwansa da kuma dukan waɗanda suka tafi tare da shi don binne mahaifinsa.
15 А браћа Јосифова видећи где им отац умре, рекоше: Може бити да се Јосиф срди на нас, па ће нам се осветити за све зло што му учинисмо.
Sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, sai suka ce, “Mai yiwuwa Yusuf yana riƙe da mu a zuciya, wataƙila zai rama dukan abubuwa marasa kyau da muka yi masa?”
16 Зато поручише Јосифу: Отац твој заповеди на самрти и рече:
Saboda haka suka aika wa Yusuf suna cewa, “Mahaifinka ya bar waɗannan umarnai kafin yă rasu.
17 Овако кажите Јосифу: Молим те, опрости браћи својој безакоње и грех, што ти пакостише; сада опрости безакоње слугама Бога оца твог. А Јосиф заплака се кад му то рекоше.
Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
18 После дођоше и браћа његова и падоше пред њим и рекоше: Ево смо слуге твоје.
’Yan’uwansa kuwa suka zo suka fāɗi a gabansa suka ce, “Mu bayinka ne.”
19 А Јосиф им рече: Не бојте се, зар сам ја место Бога?
Amma Yusuf ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Ni Allah ne?
20 Ви сте мислили зло по ме, али је Бог мислио добро, да учини шта се данас збива, да се сачува у животу многи народ.
Kun yi niyya ku yi mini lahani, amma Allah ya nufe wannan ya zama alheri don yă cika abin da yanzu yake faruwa, ceton rayuka masu yawa.
21 Не бојте се дакле; ја ћу хранити вас и вашу децу. Тако их утеши и ослободи.
Saboda haka, kada ku ji tsoro. Zan tanada muku da kuma’ya’yanku.” Ya sāke tabbatar musu, ya kuma yi musu magana ta alheri.
22 Тако живљаше Јосиф у Мисиру с домом оца свог, и поживе сто и десет година.
Yusuf ya zauna a Masar tare da dukan iyalin mahaifinsa. Ya rayu shekara ɗari da goma.
23 И виде Јосиф синове Јефремове до трећег колена; и синови Махира сина Манасијиног родише се и одрастоше на коленима Јосифовим.
Ya kuma ga tsara ta uku ta’ya’yan Efraim. Haka ma’ya’yan Makir ɗan Manasse, an haife su aka sa a gwiwoyin Yusuf.
24 И рече Јосиф браћи својој: Ја ћу скоро умрети; али ће вас зацело Бог походити, и извешће вас из ове земље у земљу за коју се заклео Авраму, Исаку и Јакову.
Sai Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ina gab da mutuwa. Amma tabbatacce Allah zai taimake ku, yă fid da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.”
25 И закле Јосиф синове Израиљеве и рече: Заиста ће вас походити Бог; а ви онда однесите кости моје одавде.
Yusuf kuwa ya sa’ya’yan Isra’ila maza suka yi rantsuwa, ya kuma ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, ku kuma dole ku ɗauki ƙasusuwana, ku haura da su daga wannan wuri.”
26 Потом умре Јосиф, а беше му сто и десет година; и помазавши га мирисима метнуше га у ковчег у Мисиру.
Yusuf kuwa ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Bayan an shafe shi da maganin hana ruɓa, sai aka sa shi a akwatin gawa a Masar.