< 1 Мојсијева 21 >
1 И Господ походи Сару, као што беше рекао и учини Господ Сари као што беше казао.
Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
2 Јер затрудне и роди Сара Авраму сина у старости његовој у исто време кад каза Господ.
Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
3 И Аврам надеде име сину који му се роди, ког му роди Сара, Исак.
Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
4 И обреза Аврам сина свог Исака кад би од осам дана, као што му заповеди Бог.
Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
5 А Авраму беше сто година кад му се роди син Исак.
Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
6 А Сара рече: Бог ми учини смех; ко год чује, смејаће ми се.
Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
7 И рече: Ко би рекао Авраму да ће Сара дојити децу? Ипак му родих сина у старости његовој.
Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
8 А кад дете дорасте да се одбије од сисе, учини Аврам велику гозбу онај дан кад одбише Исака од сисе.
Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
9 И Сара виде сина Агаре Мисирке, која га роди Авраму, где се подсмева;
Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
10 Па рече Авраму: Отерај ову робињу са сином њеним, јер син ове робиње неће бити наследник с мојим сином, с Исаком.
sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
11 А то Авраму би врло криво ради сина његовог.
Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
12 Али Бог рече Авраму: Немој да ти је криво ради детета и ради робиње твоје. Шта ти је год казала Сара, послушај; јер ће ти се у Исаку семе прозвати.
Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
13 Али ћу и од сина робињиног учинити народ, јер је твоје семе.
Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
14 И Аврам устав ујутру рано, узе хлеба и мешину воде, и даде Агари метнувши јој на леђа, и дете, и отпусти је. А она отишавши луташе по пустињи вирсавској.
Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
15 А кад неста воде у мешини, она баци дете под једно дрво,
Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
16 Па отиде колико се може стрелом добацити, и седе према њему; јер говораше: Да не гледам како ће умрети дете. И седећи према њему стаде гласно плакати.
Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
17 А Бог чу глас детињи, и анђео Божји викну с неба Агару, и рече јој: Шта ти је Агаро? Не бој се, јер Бог чу глас детињи оданде где је.
Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
18 Устани, дигни дете и узми га у наручје; јер ћу од њега учинити велик народ.
Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
19 И Бог јој отвори очи, те угледа студенац; и отишавши напуни мешину воде, и напоји дете.
Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
20 И Бог беше с дететом, те одрасте, и живеше у пустињи и поста стрелац.
Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
21 А живеше у пустињи Фарану. И мати га ожени из земље мисирске.
Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
22 У то време рече Авимелех и Фихол војвода његов Авраму говорећи: Бог је с тобом у свему што радиш.
A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
23 Закуни ми се сада Богом да нећеш преварити мене ни сина мог ни унука мог него да ћеш добро онако како сам ја теби чинио и ти чинити мени и земљи у којој си дошљак.
Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
24 А Аврам рече: Хоћу се заклети.
Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
25 Али Аврам прекори Авимелеха за студенац, који узеше на силу слуге Авимелехове.
Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
26 А Авимелех рече: Не знам ко је то учинио; нити ми ти каза, нити чух до данас.
Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
27 Тада Аврам узе оваца и говеда, и даде Авимелеху, и ухвати веру међу собом.
Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
28 А Аврам одлучи седам јагањаца из стада.
Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
29 А Авимелех рече Авраму: Шта ће оно седам јагањаца што си одлучио?
sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
30 А он одговори: Да примиш из моје руке оно седам јагањаца, да ми буде сведочанство да сам ја ископао овај студенац.
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
31 Отуда се прозва оно место Вирсавеја, јер се онде заклеше обојица.
Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
32 Тако ухватише веру на Вирсавеји. Тада се диже Авимелех и Фихол војвода његов, и вратише се у земљу филистејску.
Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
33 А Аврам посади луг на Вирсавеји, и онде призва име Господа Бога Вечног.
Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
34 И Аврам живеше као дошљак у земљи филистејској много времена.
Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.