< Књига пророка Језекиља 24 >
1 Потом године девете, десетог месеца, десетог дана, дође ми реч Господња говорећи:
A shekara ta tara, a wata na goma, a rana ta goma, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Сине човечји, запиши име овог дана, овог истог дана; у тај дан дође цар вавилонски на Јерусалим.
“Ɗan mutum, ka rubuta wannan rana, wannan rana, domin sarkin Babilon ya yi ƙawanya wa Urushalima a wannan rana.
3 И кажи причу том дому одметничком, и реци им: Овако вели Господ Господ: пристави лонац, пристави, и налиј у њ воде.
Ka faɗa wa wannan gidan’yan tawaye wani misali ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka sa tukunyar dahuwa; ka sa ta a kan wuta ka kuma zuba ruwa a cikinta.
4 Сложи у њ делове, све добре делове, стегно и плеће, и напуни га најбољих костију.
Ka sa gunduwoyin nama a cikinta dukan gunduwoyi masu kyau, cinya da kafaɗa. Ka cika ta da waɗannan ƙasusuwa mafi kyau;
5 Узми најбоље из стада, и наложи кости испод њега, и узвари добро да се и кости раскувају у њему.
ka kama mafi kyau daga cikin garken. Ka tara itace a ƙarƙashinta saboda ƙasusuwan; ka sa ta tafasa ka kuma dafa ƙasusuwan a cikinta.
6 Јер овако вели Господ Господ: Тешко граду крвничком, лонцу, на коме стоји загорел, с ког неће да сиђе загорел; повади део по део; жреб да се не баци за њ.
“‘Gama wannan shi ne abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini, ga tukunya wadda take da tsatsa, wadda tsatsarta ba za tă fita ba! Ka fitar da shi gunduwa-gunduwa ba tare da jefa ƙuri’a a kansu ba.
7 Јер је крв његова усред њега; на го камен метну је, не проли је на земљу да се покрије прахом.
“‘Gama zubar da jini yana a tsakiyarta, ta zubar da shi a dutsen da yake a fili; ba tă zubar da shi a ƙasa ba, inda ƙura za tă rufe shi.
8 Распаливши гнев да учиним освету, метнућу крв његову на го камен да се не покрије.
Don a zuga hasala a kuma yi sakayya na sa jininta a dutsen da ba a rufe ba, saboda kada a rufe.
9 Зато овако говори Господ Господ: Тешко граду крвничком! И ја ћу наложити велик огањ.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini! Ni ma zan jibge itace da yawa.
10 Нанеси дрва, и распали огањ, нека се страши месо, зачини корењем, и кости нека изгоре.
Ka tula gumagumai ka kuma ƙuna wuta. Ka dafa naman da kyau, kana haɗawa da yaji; ka kuma bar ƙasusuwan su ƙone.
11 Метни га празног на живо угљевље да се угреје и изгори бронза његова и да се стопи у њему нечистота његова и да нестане загорели његове.
Sa’an nan ka sa tukunyan nan da babu kome a kan garwashi sai ta yi zafi har darmarta ta yi ja wur domin dattinta ya narke tsatsarta kuma ta ƙone.
12 Лажима досадио ми је; зато неће изаћи из њега многа загорел његова; у огањ ће загорел његова.
Ta gajiyar da dukan ƙoƙari; ba a fid da tsatsarta nan mai yawa ba, kai, ko a wuta ma.
13 У нечистоти је твојој грдило твоје; јер сам те чистио, али се ти не очисти; нећеш се више чистити од нечистоте своје, докле не намирим гнев свој над тобом.
“‘Yanzu ƙazantarki ita ce lalaci. Domin na yi ƙoƙari in tsabtacce ke amma ba ki tsabtattu daga ƙazantarki ba, ba za ki ƙara yin tsabta ba sai hasalata a kanki ya kwanta.
14 Ја Господ говорих; доћи ће, и извршићу; нећу одустати нити ћу жалити нити ћу се раскајати, по путевима твојим и по делима твојим судиће ти, говори Господ Господ.
“‘Ni Ubangiji na faɗa. Lokaci ya zo da zan aikata. Ba zan janye ba; ba zan ji tausayi ba, ba kuwa zan bari ba. Za a hukunta ki bisa ga hali da ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
15 Опет ми дође реч Господња говорећи:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 Сине човечји, ево ја ћу ти узети жељу очију твојих злом, али не тужи ни плачи, нити суза рони.
“Ɗan mutum, da farat ɗaya ina gab da ɗauke abin da idanunka suke jin daɗin gani. Duk da haka kada ka yi makoki ko ka yi kuka ko ka zub da hawaye.
17 Немој уздисати, не жали како бива за мртвим, метни капу на главу, и обућу своју обуј на ноге, и уста својих немој покрити и хлеба ничијег не једи.
Ka yi nishi shiru; kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka ka kuma sa takalmanka a ƙafa; kada ka rufe sashen fuskarka daga ƙasa ko ka ci abincin da masu kuka sukan ci.”
18 И говорих ујутру народу, а увече ми умре жена; и сутрадан учиних како ми беше заповеђено.
Da gari ya waye, sai na yi magana da mutane, da yamma kuwa matata ta rasu. Kashegari na yi yadda aka umarce ni.
19 И рече ми народ: Хоћеш ли нам казати шта нам је то што радиш?
Sai mutane suka tambaye ni suka ce, “Ba za ka faɗa mana abin da waɗannan abubuwa suke nufi a gare mu ba?”
20 И одговорих им: Дође ми реч Господња говорећи:
Sai na ce musu, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
21 Реци дому Израиљевом: Овако вели Господ Господ: ево, ја ћу оскврнити светињу своју, величанство силе ваше, жељу очију ваших и шта је мило души вашој; и синови ће ваши и кћери ваше које остависте пасти од мача.
faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da ƙazantar da wuri mai tsarkina, kagarar da kuke taƙama, abin da idanunku suke jin daɗin gani, abin faranta zuciyarku.’Ya’yanku maza da mata waɗanda kun bari a baya za su mutu ta wurin takobi.
22 И чинићете како ја чиним: уста нећете покрити и хлеба ничијег нећете јести;
Za ku kuma yi yadda na yi. Ba za ku rufe sashe ƙasa na fuskarku ko ku ci abinci da masu kuka sukan ci ba.
23 И капе ће вам бити на главама и обућа на ногама; нећете тужити ни плакати, него ћете са безакоња својих чилети и уздисаћете један с другим.
Za ku naɗa rawunanku a kai ku sa takalmanku a ƙafafunku. Ba za ku yi kuka ko makoki ba amma za ku lalace saboda zunubanku ku kuma yi ta yin nishi.
24 И Језекиљ ће вам бити знак: чинићете све што он чини; кад то дође, познаћете да сам ја Господ Господ.
Ezekiyel zai zama alama gare ku; za ku yi daidai yadda ya yi. Sa’ad da wannan ya faru, za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’
25 А ти, сине човечји, у онај дан кад им узмем силу њихову, радост славе њихове, жељу очију њихових и за чим тежи душа њихова, синове њихове и кћери њихове,
“Kai kuma ɗan mutum, a ranar da zan ɗauke musu kagararsu, farin cikinsu da darajarsu, abin da idanunsu ke jin daɗin gani, abin da yake faranta musu zuciya, da kuka’ya’yansu maza da mata,
26 У тај дан ко побегне, неће ли доћи к теби да ти донесе глас?
a ranan nan wanda ya tsere zai zo don yă ba ka labari.
27 У тај ће се дан отворити уста твоја према оном ко побегне, и говорићеш и нећеш више бити нем; и бићеш им знак, и они ће познати да сам ја Господ.
A lokacin bakinka zai buɗe, za ka yi magana da shi ba kuwa za ka ƙara yin shiru ba. Ta haka za ka zama alama gare su, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.”