< 2 Књига Самуилова 15 >

1 А после тога набави себи Авесалом кола и коња и педесет људи, који трчаху пред њим.
Ana nan sai Absalom ya samo wa kansa wata keken yaƙi da dawakai tare da mutum hamsin da za su sha gabansa.
2 И устајаше рано Авесалом, и стајаше крај пута код врата; и ко год имаше парницу и иђаше цару на суд, Авесалом га дозиваше к себи и говораше: Из ког си града? А кад би онај одговорио: Слуга је твој из тог и тог племена Израиљевог,
Absalom yakan tashi da sassafe yă tsaya a gefen hanyar shigar ƙofar birni. Duk sa’ad da wani ya zo da ƙara don a kai gaban sarki yă yi shari’a, Absalom yakan kira shi yă ce, “Daga wane gari ka fito?” Sai mutumin yă amsa yă ce, “Bawanka ya fito a ɗaya daga cikin kabilan Isra’ila.”
3 Тада би му рекао Авесалом: Видиш, твоја је ствар добра и праведна, али те нема ко саслушати код цара.
Sai Absalom yă ce masa, “Ga shi, ƙararka daidai ne, tana kuma da gaskiya, sai dai ba wakilin sarkin da zai ji ka.”
4 Још говораше Авесалом: Кад бих ја био постављен да судим у земљи! Да сваки к мени долази који има посла на суду, ја бих му дао правицу.
Absalom kuwa yakan ƙara da cewa, “Da a ce an naɗa ni alƙali a ƙasar mana! Da duk mai ƙara, ko kuka wanda zai zo wurina, zan in tabbatar an yi masa adalci.”
5 И кад би му ко приступио да му се поклони, он би пружио руку своју, те би га ухватио и пољубио.
Kuma duk sa’ad da wani ya zo wurin Absalom ya rusuna don yă gaishe shi, sai Absalom yă sa hannunsa yă ta da shi, yă kuma rungume shi.
6 Тако чињаше Авесалом са сваким Израиљцем, који долажаше на суд к цару; и Авесалом примамљиваше срца људи Израиљаца.
Absalom ya yi ta yin haka ga dukan Isra’ilawan da suka zo wurin sarki don neman adalci, ta haka kuwa ya saci zukatan mutanen Isra’ila.
7 А кад прође четрдесет година, рече Авесалом цару: Да отидем у Хеврон да извршим завет који сам заветовао Господу.
A ƙarshen shekara huɗu, Absalom ya ce wa sarki, “Bari in tafi Hebron in cika alkawarin da na yi wa Ubangiji.
8 Јер кад сеђах у Гесуру у Сирији, учини завет слуга твој рекавши: Ако ме Господ одведе натраг у Јерусалим, послужићу Господу.
Yayinda bawanka yake zama a Geshur, a Aram, na yi wannan alkawari, na ce, ‘In Ubangiji ya komo da ni Urushalima, zan yi wa Ubangiji sujada a Hebron.’”
9 А цар му рече: Иди с миром. И он се подиже и отиде у Хеврон.
Sarki ya ce, “Ka sauka lafiya.” Sai ya tafi Hebron.
10 И разасла Авесалом по свим племенима Израиљевим уходе поручивши: Кад чујете трубе да затрубе, реците: Зацари се Авесалом у Хеврону.
Sai Absalom ya aiki manzanni a asirce cikin dukan kabilan Isra’ila, ya ce musu su ce, “Da zarar kuka ji an busa ƙaho, sai ku ce, ‘Absalom sarki ne a Hebron.’”
11 А с Авесаломом отиде двеста људи из Јерусалима позваних; али отидоше у простоти својој не знајући ништа.
Mutum ɗari biyu daga Urushalima suka raka Absalom. An gayyace su a matsayin baƙi, suka kuwa tafi cikin rashin sani, ba su san wani abu game da al’amarin ba.
12 А Авесалом посла и по Ахитофела Гилоњанина, саветника Давидовог, да дође из града свог Гилона, кад приношаше жртве. И буна поста јака, и народ се све више стецаше к Авесалому.
Yayinda Absalom yake miƙa hadaya, ya aika a kira Ahitofel mutumin Gilo, mai ba wa Dawuda shawara, yă zo daga Gilo garinsa. Ta haka makircin ya ƙara ƙarfi, masu bin Absalom kuma suka yi ta ƙaruwa.
13 Тада дође гласник к Давиду и рече: Срце Израиљу приста за Авесаломом.
Wani manzo ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Zukatan mutanen Isra’ila sun koma wajen Absalom.”
14 А Давид рече свим слугама својим које беху с њим у Јерусалиму: Устајте, да бежимо; иначе нећемо утећи од Авесалома; брже похитајте, да не похита он и не стигне нас и обори на нас зло, и града не окрене под мач.
Sai Dawuda ya ce wa dukan fadawansa da suke tare da shi a Urushalima, “Ku zo! Mu gudu, in ba haka ba, babu wanda zai tsira daga hannun Absalom. Dole mu bar nan, nan da nan, in ba haka ba zai tashi da sauri yă fāɗa mana, yă kuma hallaka garin da takobi.”
15 А слуге цареве рекоше цару: Шта је год воља цару господару нашем, ево слуга твојих.
Sai fadawan sarki suka ce masa, “Barorinka suna a shirye su yi duk abin da ranka yă daɗe, ya zaɓa.”
16 И отиде цар пешице и сав дом његов; само десет жена иноча остави цар да му чувају кућу.
Sarki ya kama hanya, dukan gidansa kuwa suna biye da shi; amma ya bar ƙwarƙwarai goma su lura da fada.
17 И када отиде цар и сав народ пешице, уставише се на једном месту подалеко.
Ta haka sarki ya kama hanya da dukan mutane suna biye da shi, suka yi sansani a wani wuri mai ɗan nisa da Urushalima.
18 А све слуге његове иђаху уза њ, и сви Херетеји и сви Фелетеји; и сви Гетеји, шест стотина људи, који беху дошли пешке из Гата, иђаху пред царем.
Dukan mutanensa suka wuce gabansa, tare da dukan Keretawa da Feletiyawa; da dukan mutane ɗari shida na Gittiyawan da suka raka shi daga Gat, suka wuce gaban sarki.
19 И рече цар Итају Гетејину: Што и ти идеш с нама? Врати се и остани код цара; јер си странац и опет ћеш отићи у своје место.
Sarki ya ce wa Ittai mutumin Gat, “Don me za ka zo tare da mu? Ka koma ka zauna tare da Sarki Absalom. Kai baƙo ne, ɗan gudun hijira daga garinka.
20 Јуче си дошао, па зар данас да те крећем да се потуцаш с нама? Ја ћу ићи куда могу, а ти се врати и одведи натраг браћу своју. Нека милост и вера буде с тобом.
Jiya-jiya ka zo. Yau kuma in sa ka yi ta yawo tare da mu, ga shi ban ma san inda za ni ba? Koma, ka tafi da’yan’uwanka. Bari alheri da amincin Ubangiji su kasance tare da kai.”
21 А Итај одговори цару и рече: Тако жив да је Господ и тако да је жив цар господар мој, где буде цар господар мој, било на смрт или на живот, онде ће бити и слуга твој.
Amma Ittai ya ce wa sarki, “Muddin Ubangiji yana a raye kuma muddin ranka yă daɗe yana a raye, duk inda ranka yă daɗe sarki zai kasance, ko a yi rai ko a mutu, a can bawanka zai kasance.”
22 Тада рече Давид Итају: А ти ходи. И тако пође Итај Гетејин са свим људима својим и свом децом што беху с њим.
Dawuda ya ce wa Ittai, “Wuce gaba, taka mu je.” Sai Ittai mutumin Gat ya shiga layi tare da dukan mutanensa da iyalan da suke tare da shi.
23 И сва земља плакаше гласно и сав народ прелажаше. И тако цар пређе преко потока Кедрона, и сав народ пређе идући к пустињи.
Dukan ƙauyuka suka yi ta kururuwa yayinda mutanen suke wucewa. Sarki shi ma ya haye ta Kwarin Kidron, mutane kuma suka ci gaba da tafiya zuwa wajen hamada.
24 А гле, и Садок беше онде и сви Левити с њим носећи ковчег завета Божијег; и спустише ковчег Божји, а пође и Авијатар, докле сав народ изиђе из града.
Zadok yana nan tare da su, kuma dukan Lawiyawan da suke tare da shi kuwa suna ɗauke da akwatin alkawarin Allah. Suka sauke akwatin alkawarin Allah, Abiyatar ya miƙa hadaya sai da mutane suka gama fita daga birnin.
25 И рече цар Садоку: Носи ковчег Божји натраг у град; ако нађем милост пред Господом, Он ће ме довести натраг, и даће ми да опет видим Њега и дом Његов.
Sa’an nan sarki ya ce wa Zadok, “Ka komar da akwatin alkawarin Allah cikin birnin. Idan na sami tagomashi a idon Ubangiji, zai dawo da ni, yă kuma sa in sāke gan shi a mazauninsa.
26 Ако ли овако каже: Ниси ми мио; ево ме, нека учини са мном шта му буде воља.
Amma in ya ce, ‘Ina baƙin ciki da kai,’ to, ina a shirye; bari yă yi abin da ya fi masa.”
27 Још рече цар Садоку свештенику: Ниси ли ти виделац? Врати се у град с миром, и Ахимас син твој и Јонатан син Авијатаров, два сина ваша с вама.
Sarki ya kuma ce wa Zadok firist, “Ashe, kai ba mai duba ba ne? Ka koma cikin birnin lafiya, tare da ɗanka Ahimawaz, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar. Kai da Abiyatar ku tafi da’ya’yanku biyu.
28 Видите, ја ћу се забавити у пољу у пустињи докле не дође од вас гласник да ми јави.
Zan kuwa jira a mashigai a hamada, sai na ji daga gare ku.”
29 И тако Садок и Авијатар однесоше ковчег Божји натраг у Јерусалим, и осташе онде.
Saboda haka Zadok da Abiyatar suka ɗauki akwatin alkawarin Allah suka komar da shi Urushalima, suka zauna a can.
30 А Давид иђаше уз гору Маслинску, и идући плакаше, и покривене главе и бос иђаше; тако и сав народ, који беше с њим, сваки покривене главе иђаше, и идући плакаше.
Amma Dawuda ya ci gaba yana hawan Dutsen Zaitun, yana kuka yayinda yake tafiya; kansa a rufe, kuma babu takalma a ƙafafunsa. Dukan mutanen da suke tare da shi suka rufe kawunansu suna ta kuka yayinda suke haurawa.
31 Тада јавише Давиду и рекоше му. Ахитофел је међу онима који се побунише с Авесаломом. А Давид рече: Разбиј намеру Ахитофелову, Господе!
To, an gaya wa Dawuda cewa, “Ahitofel yana cikin waɗanda suka hadasa maƙarƙashiya tare da Absalom.” Saboda haka Dawuda ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji ka mai da shawarar Ahitofel ta zama shiririta.”
32 И кад Давид дође наврх горе, где се хтеде поклонити Богу, гле, срете га Хусај Архијанин раздрте хаљине и главе посуте прахом.
Da Dawuda ya isa ƙwanƙoli, inda mutane sun saba yi wa Allah sujada, Hushai, mutumin Arkitawa kuwa yana can don yă tarye shi, taguwarsa a yage, ga kuma ƙura a kansa.
33 И рече му Давид: Ако пођеш са мном бићеш ми на теготу.
Sai Dawuda ya ce masa, “In ka tafi tare da ni, za ka zama mini kaya.
34 Али да се вратиш у град и кажеш Авесалому: Бићу твој слуга царе! Био сам дуго слуга твом оцу, а сада ћу тако бити теби слуга; разбићеш ми намеру Ахитофелову.
Amma in ka koma birni, ka gaya wa Absalom, ‘Zan zama bawanka, ya sarki; dā ni bawan mahaifinka ne, amma yanzu zan zama bawanka,’ ta haka za ka watsar da shawarar Ahitofel.
35 И свештеници Садок и Авијатар неће ли бити с тобом? Шта год чујеш из куће цареве, докажи Садоку и Авијатару свештеницима.
Ba Zadok da Abiyatar firistocin nan suna nan tare da kai ba? Ka gaya musu duk abin da ka ji a fadan sarki.
36 Ето, онде су с њима два сина њихова, Ахимас Садоков и Јонатан Авијатаров, по њима ми јављајте шта год дочујете.
’Ya’yansu biyu maza, Ahimawaz ɗan Zadok, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar, suna can tare da su. Ka aike su wurina da duk abin da ka ji.”
37 И отиде у град Хусај пријатељ Давидов, и Авесалом дође у Јерусалим.
Saboda haka Hushai abokin Dawuda ya isa Urushalima yayinda Absalom yake shigowa birnin.

< 2 Књига Самуилова 15 >