< Psalmi 147 >

1 Hvalite Gospoda, jer je slatko pjevati Boga našega, jer blagome prilikuje hvala.
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2 Gospod zida Jerusalim, sabira rasijane sinove Izrailjeve;
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3 Iscjeljuje one koji su skrušena srca, i lijeèi tuge njihove;
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
4 Izbraja mnoštvo zvijezda, i sve ih zove imenom.
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
5 Velik je Gospod naš i velika je krjepost njegova, i razumu njegovu nema mjere.
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
6 Prihvata smjerne Gospod, a bezbožne ponižava do zemlje.
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
7 Redom pjevajte Gospodu hvalu, udarajte Bogu našemu u gusle.
Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
8 On zastire nebo oblacima, sprema zemlji dažd, èini te raste na gorama trava;
Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
9 Daje stoci piæu njezinu, i vraniæima, koji vièu k njemu.
Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
10 Ne mari za silu konjsku, niti su mu mili kraci èovjeèiji.
Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
11 Mili su Gospodu oni koji ga se boje, koji se uzdaju u milost njegovu.
Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
12 Slavi, Jerusalime, Gospoda; hvali Boga svojega, Sione!
Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
13 Jer on utvrðuje prijevornice vrata tvojih, blagosilja sinove tvoje u tebi.
Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
14 Ograðuje meðe tvoje mirom, nasiæava te jedre pšenice.
Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 Šalje govor svoj na zemlju, brzo teèe rijeè njegova.
Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
16 Daje snijeg kao vunu, sipa inje kao pepeo.
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
17 Baca grad svoj kao zalogaje, pred mrazom njegovijem ko æe ostati?
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
18 Pošlje rijeè svoju, i sve se raskravi; dune duhom svojim, i poteku vode.
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
19 On je javio rijeè svoju Jakovu, naredbe i sudove svoje Izrailju.
Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
20 Ovo nije uèinio nijednome drugom narodu, i sudova njegovijeh oni ne znaju. Aliluja!
Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.

< Psalmi 147 >