< Psalmi 107 >

1 Hvalite Gospoda, jer je dobar; jer je dovijeka milost njegova.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Tako neka reku koje je izbavio Gospod, koje je izbavio iz ruke neprijateljeve,
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 Skupio ih iz zemalja, od istoka i zapada, od sjevera i mora.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Lutaše po pustinji gdje se ne živi, puta gradu naseljenome ne nahodiše;
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Bjehu gladni i žedni, i duša njihova iznemagaše u njima;
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Ali zavikaše ka Gospodu u tuzi svojoj; i izbavi ih iz nevolje njihove.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 I izvede ih na prav put, koji ide u grad naseljeni.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Neka hvale Gospoda za milost njegovu, i za èudesa njegova radi sinova ljudskih!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Jer siti dušu taštu, i dušu gladnu puni dobra.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Sjedješe u tami i u sjenu smrtnom, okovani u tugu i u gvožðe;
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Jer ne slušaše rijeèi Božijih, i ne mariše za volju višnjega.
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 On poništi srce njihovo stradanjem; spotakoše se, i ne bješe ko da pomože.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Ali zavikaše ka Gospodu u tuzi svojoj, i izbavi ih iz nevolje njihove;
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 Izvede ih iz tame i sjena smrtnoga, i raskide okove njihove.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Neka hvale Gospoda za milost njegovu, i za èudesa njegova radi sinova ljudskih!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Jer razbi vrata mjedena, i prijevornice gvozdene slomi.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Bezumnici stradaše za nevaljale putove svoje, i za nepravde svoje.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Svako se jelo gadilo duši njihovoj, i doðoše do vrata smrtnijeh.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Ali zavikaše ka Gospodu u tuzi svojoj, i izbavi ih iz nevolje njihove.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Posla rijeè svoju i iscijeli ih, i izbavi ih iz groba njihova.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Neka hvale Gospoda za milost njegovu, i za èudesa njegova radi sinova ljudskih!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 I neka prinesu žrtvu za hvalu, i kazuju djela njegova u pjesmama!
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Koji plove po moru na korabljima, i rade na velikim vodama,
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 Oni su vidjeli djela Gospodnja, i èudesa njegova u dubini.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 Kaže, i diže se silan vjetar, i ustaju vali na njemu,
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 Dižu se do nebesa i spuštaju do bezdana: duša se njihova u nevolji razliva;
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Posræu i ljuljaju se kao pijani; sve mudrosti njihove nestaje.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Ali zavikaše ka Gospodu u tuzi svojoj, i izvede ih iz nevolje njihove.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 On obraæa vjetar u tišinu, i vali njihovi umuknu.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Vesele se kad se stišaju, i vodi ih u pristanište koje žele.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Neka hvale Gospoda za milost njegovu, i za èudesa njegova radi sinova ljudskih!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Neka ga uzvišuju na saboru narodnom, na skupštini starješinskoj slave ga!
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 On pretvara rijeke u pustinju, i izvore vodene u suhotu,
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 Rodnu zemlju u slanu pustaru za nevaljalstvo onijeh koji žive na njoj.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 On pretvara pustinju u jezera, i suhu zemlju u izvore vodene,
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 I naseljava onamo gladne. Oni zidaju gradove za življenje;
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 Siju polja, sade vinograde i sabiraju ljetinu.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Blagosilja ih i množe se jako, i stoke im ne umaljuje.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Prije ih bijaše malo, padahu od zla i nevolje, što ih stizaše.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 On sipa sramotu na knezove, i ostavlja ih da lutaju po pustinji gdje nema putova.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 On izvlaèi ubogoga iz nevolje, i plemena množi kao stado.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Dobri vide i raduju se, a svako nevaljalstvo zatiskuje usta svoja.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Ko je mudar, neka zapamti ovo, i neka poznadu milosti Gospodnje.
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Psalmi 107 >