< Mihej 4 >
1 Ali æe u pošljednja vremena biti utvrðena gora doma Gospodnjega navrh gora i uzvišena iznad humova, i narodi æe se stjecati k njoj.
A kwanakin ƙarshe za a kafa dutsen haikalin Ubangiji yă zama babba a cikin duwatsu. Za a ɗaga shi sama da tuddai, mutane kuma za su riƙa ɗunguma zuwa gare shi.
2 I iæi æe mnogi narodi govoreæi: hodite, da idemo na goru Gospodnju i u dom Boga Jakovljeva, i uèiæe nas svojim putovima, i hodiæemo njegovijem stazama; jer æe iz Siona izaæi zakon i rijeè Gospodnja iz Jerusalima.
Al’ummai da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, don mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Doka za tă fita daga Sihiyona, maganar Ubangiji kuma daga Urushalima.
3 I sudiæe meðu mnogim narodima, i pokaraæe jake narode nadaleko, i oni æe raskovati maèeve svoje na raonike, i koplja svoja na srpove; neæe dizati maèa narod na narod, niti æe se više uèiti ratu.
Zai shari’anta tsakanin mutane yă kuma sulhunta tsakanin manyan al’ummai nesa da kuma kusa. Har su mai da takubansu su zama garemani, māsunsu kuma su zama wuƙaƙen askin itace. Al’umma ba za tă ɗauki takobi gāba da wata al’umma ba, ko a yi horarwa don yaƙi.
4 Nego æe sjedjeti svaki pod svojom vinovom lozom i pod smokvom, i neæe biti nikoga da ih plaši; jer usta Gospoda nad vojskama rekoše.
Kowa zai zauna a tushen kuringar inabinsa da tushen ɓaurensa, kuma ba wanda zai tsoratar da su, gama Ubangiji Maɗaukaki ne ya faɗa.
5 Jer æe svi narodi hoditi svaki u ime boga svojega; a mi æemo hoditi u ime Gospoda Boga svojega uvijek i dovijeka.
Dukan al’ummai za su iya tafiya a cikin sunan allolinsu; mu dai za mu yi tafiya a cikin sunan Ubangiji Allahnmu har abada abadin.
6 U to vrijeme, govori Gospod, sabraæu hrome, i skupiæu odagnane i kojima zlo uèinih.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “zan tattara guragu; zan kuma tara masu zaman bauta, da waɗanda na sa suka damu.
7 I uèiniæu od hromijeh ostatak i od odagnanih silan narod; i Gospod æe carovati nad njima na gori Sionu otsada i dovijeka.
Zan mai da guragu su zama raguwa, waɗanda aka kora, su zama al’umma mai ƙarfi. Ubangiji zai yi mulkinsu a Dutsen Sihiyona daga wannan rana da kuma har abada.
8 I ti, kulo stadu, stijeno kæeri Sionskoj, tebi æe doæi, doæi æe prva vlast, carstvo kæeri Jerusalimske.
Game da ke, ya hasumiyar tsaron garke, Ya mafaka Diyar Sihiyona, za a maido miki da mulkinki na dā, sarauta kuma za tă zo wa Diyar Urushalima.”
9 Zašto vièeš tako jako? nema li cara u tebi? eda li izgiboše tvoji savjetnici, te te obuzeše bolovi kao porodilju?
Don me yanzu kike kuka da ƙarfi, ba ki da sarki ne? Masu shawararki sun hallaka ne, da zafi ya cika ki kamar mace mai naƙuda?
10 Muèi se i vièi, kæeri Sionska, kao porodilja, jer æeš izaæi iz grada i stanovaæeš u polju, i otiæi æeš u Vavilon; ondje æeš se osloboditi, ondje æe te iskupiti Gospod iz ruku neprijatelja tvojih.
Ki yi birgima cikin zafin azaba, ya Diyar Sihiyona, kamar macen da take naƙuda, don yanzu dole ki bar birni ki kafa sansani a filin Allah. Za ki tafi Babilon; a can za a kuɓutar da ki. A can ne Ubangiji zai fanshe ki daga hannun maƙiyanki.
11 A sada se sabraše na te mnogi narodi govoreæi: da se oskvrni, i da se oèi naše nagledaju Siona.
Amma yanzu al’ummai da yawa suna gāba da ke. Suna cewa, “Bari a ƙazantar da ita, bari mu zuba wa Sihiyona ido.”
12 Ali ne znaju misli Gospodnjih, niti razumiju namjere njegove, jer ih je skupio kao snoplje na gumno.
Amma ba su san tunanin Ubangiji ba; ba su fahimci shirinsa ba, shi da ya tattara su kamar dammuna a masussuka.
13 Ustani i vrsi, kæeri Sionska, jer æu ti naèiniti rog gvozden, i kopita æu ti naèiniti mjedena, te æeš satrti mnoge narode, i posvetiæu Gospodu blago njihovo i imanje njihovo Gospodu sve zemlje.
“Ki tashi ki yi sussuka, ya Diyar Sihiyona, gama zan ba ki ƙahonin ƙarfe; zan ba ki kofatan tagulla domin ki ragargaje al’ummai masu yawa.” Za ki ba Ubangiji dukan dukiyarsu da suka tara ta hanyar zamba, wadatarsu kuma ga Ubangiji dukan duniya.