< Marku 2 >

1 I uðe opet u Kapernaum poslije nekoliko dana; i èu se da je u kuæi.
Bayan’yan kwanaki, da Yesu ya sāke shiga Kafarnahum, sai mutane suka ji labarin zuwansa gida.
2 I odmah skupiše se mnogi tako da ne mogahu ni pred vratima da se sprate; i kazivaše im rijeè.
Mutane suka taru da yawa har ma babu wuri, ko a bakin ƙofa ma, sai ya yi musu wa’azin bishara.
3 I doðoše k njemu s uzetijem koga nošaše èetvoro.
Waɗansu mutum huɗu suka zo wajensa ɗauke da wani shanyayye.
4 I ne moguæi približiti se k njemu od naroda otkriše kuæu gdje on bijaše, i prokopavši spustiše odar na kome uzeti ležaše.
Da ba su iya kai shi wurin Yesu ba, saboda taron, sai suka buɗe rufin gidan saman, bisa daidai inda Yesu yake. Bayan da suka huda rami, sai suka saukar da shanyayyen, kwance a kan tabarmarsa.
5 A Isus vidjevši vjeru njihovu reèe uzetome: sinko! opraštaju ti se grijesi tvoji.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Saurayi, an gafarta zunubanka.”
6 A ondje sjeðahu neki od književnika i pomišljahu u srcima svojima:
To, waɗansu malaman dokoki da suke zaune a wurin, suka yi tunani a zuciyarsu, suna cewa,
7 Šta ovaj tako huli na Boga? Ko može opraštati grijehe osim jednoga Boga?
“Me ya sa mutumin nan yake magana haka? Yana saɓo! Wane ne zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
8 I odmah razumjevši Isus duhom svojijem da oni tako pomišljaju u sebi, reèe im: što tako pomišljate u srcima svojijem?
Nan da nan, Yesu ya gane a ruhunsa abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya ce musu, “Me ya sa kuke tunanin waɗannan abubuwa?
9 Što je lakše? reæi uzetome: opraštaju ti se grijesi? ili reæi: ustani i uzmi odar svoj, i hodi?
Wanne ya fi sauƙi, a ce wa shanyayyen, ‘An gafarta zunubanka,’ ko a ce, ‘Tashi, ɗauki tabarmarka ka yi tafiya’?
10 No da znate da vlast ima sin èovjeèij na zemlji opraštati grijehe, reèe uzetome: )
Amma don ku san cewa, Ɗan Mutum yana da iko a duniya yă gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen,
11 Tebi govorim: ustani i uzmi odar svoj, i idi doma.
“Ina ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka, ka tafi gida.”
12 I usta odmah, i uzevši odar iziðe pred svima tako da se svi divljahu i hvaljahu Boga govoreæi: nigda toga vidjeli nijesmo.
Sai ya tashi, ya ɗauki tabarmarsa, ya yi tafiyarsa a gabansu duka. Wannan ya ba wa kowa mamaki, suka kuma ɗaukaka Allah suna cewa, “Ba mu taɓa ganin abu haka ba!”
13 I iziðe opet k moru; i sav narod iðaše k njemu, i uèaše ih.
Yesu ya sāke tafiya bakin tafkin. Taro mai yawa ya zo wurinsa, sai ya fara koya musu.
14 I prolazeæi vidje Leviju Alfejeva gdje sjedi na carini, i reèe mu: hajde za mnom. I ustavši otide za njim.
Yana cikin tafiya, sai ya ga Lawi, ɗan Alfayus zaune a inda ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.” Sai Lawi ya tashi, ya bi shi.
15 I kad sjeðaše Isus za trpezom u kuæi njegovoj, i carinici i grješnici mnogi sjeðahu s njim i s uèenicima njegovijem: jer ih bijaše mnogo koji iðahu za njim.
Yayinda Yesu yake cin abinci a gidan Lawi, sai masu karɓar haraji da “masu zunubi” da yawa, suka zo suka ci tare da shi da almajiransa, gama akwai mutane da yawa da suka bi shi.
16 A književnici i fariseji vidjevši ga gdje jede s carinicima i s grješnicima govorahu uèenicima njegovijem: zašto s carinicima i grješnicima jede i pije?
Da malaman dokoki, waɗanda su ma Farisiyawa ne, suka ga yana ci tare da masu “zunubi” da masu karɓar haraji, sai suka tambayi almajiransa, suka ce, “Me ya sa yake ci tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
17 I èuvši Isus reèe im: ne trebaju zdravi ljekara nego bolesni. Ja nijesam došao da dozovem pravednike no grješnike na pokajanje.
Da jin wannan, Yesu ya ce musu, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya. Ban zo domin in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi.”
18 I bijahu uèenici Jovanovi i farisejski koji pošæahu; i doðoše i rekoše mu: zašto uèenici Jovanovi i farisejski poste a tvoji uèenici ne poste?
To, almajiran Yohanna da na Farisiyawa suna azumi, sai waɗansu mutane suka zo suka tambayi Yesu, suka ce, “Yaya almajiran Yohanna da na Farisiyawa suna azumi, amma almajiranka ba sa yi?”
19 I reèe im Isus: eda li mogu svatovi postiti dok je ženik s njima? Dokle god imaju sa sobom ženika ne mogu postiti.
Yesu ya amsa ya ce, “Yaya abokan ango za su yi azumi, sa’ad da yana tare da su? Ai, ba za su yi ba, muddin yana tare da su.
20 Nego æe doæi dni kad æe se oteti od njih ženik, i tada æe postiti u one dne.
Ai, lokaci yana zuwa da za a ɗauke musu angon. A sa’an nan ne fa za su yi azumi.
21 I niko ne prišiva nove zakrpe na staru haljinu; inaèe æe odadrijeti nova zakrpa od staroga, i gora æe rupa biti.
“Ba mai facin sabon ƙyalle a tsohuwar riga. In ya yi haka, sabon ƙyallen zai yage daga tsohuwar, yagewar kuwa za tă zama da muni.
22 I niko ne ljeva nova vina u mjehove stare; inaèe novo vino prodre mjehove, i vino se prolije, i mjehovi propadnu; nego novo vino u nove mjehove ljevati treba.
Ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a tsofaffin salkuna. In ya yi haka, ruwan inabin zai farfashe salkunan, yă yi hasarar ruwan inabin, salkunan kuma su lalace. A’a, yakan zuba sabon ruwan inabin a sababbin salkuna.”
23 I dogodi mu se da iðaše u subotu kroz usjeve, i uèenici njegovi trgahu putem klasje.
Wata ranar Asabbaci, Yesu yana ratsa gonakin hatsi, sai almajiransa da suke tafiya tare da shi, suka fara kakkarya waɗansu kan hatsi.
24 I fariseji govorahu mu: gledaj, zašto èine u subotu što ne valja?
Farisiyawa suka ce masa, “Duba, me ya sa suke yin abin da doka ta hana a yi, a ranar Asabbaci?”
25 A on reèe im: nijeste li nikad èitali šta uèini David kad mu bi do nevolje i ogladnje s onima što bijahu s njim?
Ya amsa ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi ba, sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa, suna kuma cikin bukata?
26 Kako uðe u Božiju kuæu pred Avijatarom poglavarom sveštenièkijem i hljebove postavljene pojede kojijeh ne bijaše slobodno nikome jesti osim sveštenika, i dade ih onima koji bijahu s njim?
Ya shiga gidan Allah a zamanin Abiyatar babban firist, ya ci keɓaɓɓen burodin nan, ya kuma ba wa abokan tafiyarsa abin da firistoci kaɗai sukan ci bisa ga doka?”
27 I govoraše im: subota je naèinjena èovjeka radi, a nije èovjek subote radi.
Sai ya ce musu, “An yi Asabbaci saboda mutum ne, ba mutum saboda Asabbaci ba.
28 Dakle je gospodar sin èovjeèij i od subote.
Don haka, Ɗan Mutum Ubangiji ne, har ma da na Asabbaci.”

< Marku 2 >