< Luki 14 >

1 I dogodi mu se da doðe u subotu u kuæu jednoga kneza farisejskoga da jede hljeb; i oni motrahu na njega.
Wata ranar Asabaci, ya shiga gidan wani daya daga cikin shugabanin Farisawa domin cin abinci, mutane kuwa suna sa masa idanu.
2 I gle, bješe pred njim nekakav èovjek na kome bješe debela bolest.
Sai ga wani a gabansa mai ciwon fara.
3 I odgovarajuæi Isus reèe zakonicima i farisejima govoreæi: je li slobodno u subotu iscjeljivati?
Yesu ya tambaye masanan attaura da Farisawa, “Ya halata a wakar a ranan Asabaci, ko a'a?”
4 A oni oæutješe. I dohvativši ga se iscijeli ga i otpusti.
Amma suka yi shiru. Yesu kuwa ya kama shi, ya warkar da shi, ya kuma sallame shi.
5 I odgovarajuæi reèe im: koji od vas ne bi svojega magarca ili vola da mu padne u bunar odmah izvadio u dan subotni?
Sai yace masu, “Wanene a cikinku in yana da jaki ko takarkari ya fadi a rijiya ran Asabaci, ba zai fitar da shi nan da nan ba?”
6 I ne mogoše mu odgovoriti na to.
Sai suka kasa ba da amsar wadannan abubuwa.
7 A gostima kaza prièu, kad opazi kako izbirahu zaèelja, i reèe im:
Sa'adda Yesu ya lura da yadda wadanda aka gayyato sun zabi mazaunan alfarma, sai ya ba su misali yana ce masu,
8 Kad te ko pozove na svadbu, ne sjedaj u zaèelje, da ne bude meðu gostima ko stariji od tebe;
“Sa'adda wani ya gayyace ka zuwa bikin aure, kada ka zauna a wuri mai daraja, domin yana yiwuwa an gayyaci wani wanda ya fi ka daraja.
9 I da ne bi došao onaj koji je pozvao tebe i njega, i rekao ti: podaj mjesto ovome: i onda æeš sa stidom sjesti na niže mjesto.
Sa'adda wanda ya gayyace ku duka biyu ya zo, zai ce maka, 'Ka ba mutumin nan wurinka,' sa'annan a kunyace za ka koma mazauni mafi kaskanci.
10 Nego kad te ko pozove, došavši sjedi na pošljednje mjesto, da ti reèe kad doðe onaj koji te pozva: prijatelju! pomakni se više; tada æe tebi biti èast pred onima koji sjede s tobom za trpezom.
Amma idan an gayyace ka biki, sai ka je ka zauna a wuri mafi kaskanci, domin idan wanda ya gayyace ka ya zo, yana iya ce maka, 'Aboki, hawo nan mana'. Sannan za ka sami girma kenan a gaban dukan wadanda kuke zaune tare a kan teburi.
11 Jer svaki koji se podiže, poniziæe se; a koji se ponižuje, podignuæe se.
Duk wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, wanda ya kaskantar da kansa, kuma daukaka shi za a yi”.
12 A i onome što ih je pozvao reèe: kad daješ objed ili veèeru, ne zovi prijatelja svojijeh, ni braæe svoje, ni roðaka svojijeh, ni susjeda bogatijeh, da ne bi i oni tebe kad pozvali i vratili ti;
Yesu ya ce wa mutumin da ya gayyace shi, “Idan za ka gayyaci mutum cin abinci ko biki, kada ka gayyaci abokanka, ko 'yan'uwanka, ko danginka, ko makwabtanka masu arziki, kamar yadda suna iya gayyatar ka, sai ya zama an maida maka.
13 Nego kad èiniš gozbu, zovi siromahe, kljaste, hrome, slijepe;
Amma idan za ka kira biki sai ka gayyace matalauta, da nakasassu, da guragu, da makafi,
14 I blago æe ti biti što ti oni ne mogu vratiti; nego æe ti se vratiti o vaskrseniju pravednijeh.
za ka kuwa sami albarka da yake ba su da hanyar saka maka. Gama za a saka maka a ranar tashin masu adalci.”
15 A kad èu to neki od onijeh što sjeðahu s njim za trpezom reèe mu: blago onome koji jede hljeba u carstvu Božijemu!
Da daya daga cikin wadanda ke zama akan teburi da Yesu ya ji wadannan abubuwa, sai ya ce masa, “Albarka ta tabbata ga wanda zai ci abinci a mulkin Allah!”
16 A on mu reèe: jedan èovjek zgotovi veliku veèeru, i pozva mnoge;
Amma Yesu ya ce masa, “Wani mutum ne ya shirya babban biki ya gayyaci mutane da yawa.
17 I kad bi vrijeme veèeri, posla slugu svojega da kaže zvanima: hajdete, jer je veæ sve gotovo.
Da lokacin biki ya yi, sai ya aiki bawansa ya ce wa wadanda aka gayyata, “Ku zo, duk an shirya kome.”
18 I poèeše se izgovarati svi redom; prvi mu reèe: kupih njivu, i valja mi iæi da je vidim; molim te izgovori me.
Sai dukansu, suka fara kawo dalilai. Na farko ya ce masa, 'Na sayi gona, lalle ne in je in gan ta. Ina rokonka ka dauke mani.'
19 I drugi reèe: kupih pet jarmova volova, i idem da ih ogledam; molim te, izgovori me.
Sai wani ya ce, 'Na sayi shanu garma biyar, ina so in gwada su. Ina ronkan ka, ka dauke mani.'
20 I treæi reèe: oženih se, i zato ne mogu doæi.
Wani mutum kuma ya ce, 'Na yi aure, don haka ba zan iya zuwa ba.'
21 I došavši sluga taj kaza ovo gospodaru svome. Tada se rasrdi domaæin i reèe sluzi svome: idi brzo na raskršæa i ulice gradske, i dovedi amo siromahe, i kljaste, i bogaljaste, i slijepe.
Da bawan ya zo ya fadi wa maigidansa wadannan abubuwa, sai maigidan yayi fushi, ya ce wa bawansa, jeka da sauri ka bi cikin titunan birni da kwararo-kwararo, ka kawo gajiyayyu, da nakasassu, da makafi, da guragu.'
22 I reèe sluga: gospodaru, uèinio sam kako si zapovjedio, i još mjesta ima.
Sai bawan ya ce, 'Maigida, abin da ka umarta an gama, amma har yanzu da sauran wuri.”
23 I reèe gospodar sluzi: iziði na putove i meðu ograde, te natjeraj da doðu da mi se napuni kuæa.
Sai maigidan ya ce wa bawan, 'Jeka, ka bi kwararo-kwararo da hanyoyin karkara, ka rinjayi mutane su shigo, don a cika gidana.
24 Jer vam kažem da nijedan od onijeh zvanijeh ljudi neæe okusiti moje veèere. Jer je mnogo zvanijeh, ali je malo izbranijeh.
Gama ina gaya maku, babu ko daya daga cikin mutanen da na gayyata da farko da zai dandana bikina.”
25 Iðaše pak s njim mnoštvo naroda, i obazrevši se reèe im:
Ana nan, taron suna tafiya tare da shi, sai ya juya ya ce masu,
26 Ako ko doðe k meni a ne mrzi na svojega oca, i na mater, i na ženu, i na djecu, i na braæu, i na sestre i na samu dušu svoju, ne može biti moj uèenik.
“Duk mai zuwa wurina amma bai ki mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa, da 'ya'yansa, da 'yan'uwansa maza da mata ba - I, har da ransa ma, ba zai iya zama almajirina ba.
27 I ko ne nosi krsta svojega i za mnom ne ide, ne može biti moj uèenik.
Duk wanda bai dauki gijiyensa ya biyo ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
28 I koji od vas kad hoæe da zida kulu ne sjede najprije i ne proraèuni šta æe ga stati, da vidi ima li da može dovršiti?
Wanene a cikinku wanda yake niyyar gina bene, da ba zai zauna ya yi lissafin abin da zai kashe ba tun da farko, ko yana da ishashen kudi da zai iya kare aikin?
29 Da ne bi, kad postavi temelj i ne uzmože dovršiti, svi koji gledaju stali mu se rugati
Kada ya zama bayan da ya sa harsashin ginin, ya kasa gamawa, har duk wadanda suka gani su fara yi masa ba'a,
30 Govoreæi: ovaj èovjek poèe zidati, i ne može da dovrši.
su rika cewa, ga mutumin nan ya fara gini amma ya kasa gamawa.'
31 Ili koji car kad poðe s vojskom da se pobije s drugijem carem ne sjede najprije i ne drži vijeæu može li s deset hiljada sresti onoga što ide na njega sa dvadeset hiljada?
Ko kuwa wanne sarki ne, in za shi je yaki da wani sarki, da ba zai zauna da farko ya yi shawara ya ga ko shi mai jarumawa dubu goma zai iya karawa da dayan sarkin mai jarumawa dubu ashirin ba?
32 Ako li ne može, a on pošlje poslanike dok je onaj još daleko i moli da se pomire.
In kuwa ba zai iya ba, to tun wancan yana nesa, sai ya aiki wakili ya kuma tambayo sharudan salama.
33 Tako dakle svaki od vas koji se ne odreèe svega što ima ne može biti moj uèenik.
Haka ma, ba wani a cikinku wanda bai rabu da duk abin da ya mallaka ba, da zai iya zama almajirina.”
34 So je dobra, ali ako so obljutavi, èim æe se osoliti?
“Gishiri abu ne mai kyau, amma idan gishiri ya sane, da me za a dadada shi?
35 Niti je potrebna u zemlju ni u gnoj; nego je prospu napolje. Ko ima uši da èuje neka èuje.
Ba shi da wani anfani a kasa, ko ya zama taki. Sai dai a zubar kawai. Duk mai kunnen ji, ya ji.”

< Luki 14 >