< Luki 1 >
1 Buduæi da mnogi poèeše opisivati dogaðaje koji se ispuniše meðu nama,
Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
2 Kao što nam predaše koji isprva sami vidješe i sluge rijeèi biše:
kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
3 Namislih i ja, ispitavši sve od poèetka, po redu pisati tebi, èestiti Teofile,
Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
4 Da poznaš temelj onijeh rijeèi kojima si se nauèio.
Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
5 U vrijeme Iroda cara Judejskoga bijaše neki sveštenik od reda Avijna, po imenu Zarija, i žena njegova od plemena Aronova, po imenu Jelisaveta.
A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
6 A bijahu oboje pravedni pred Bogom, i življahu u svemu po zapovijestima i uredbama Gospodnjijem bez mane.
Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
7 I ne imadijahu djece; jer Jelisaveta bješe nerotkinja, i bijahu oboje veæ stari.
Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8 I dogodi se, kad on služaše po svome redu pred Bogom,
Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
9 Da po obièaju sveštenstva doðe na njega da iziðe u crkvu Gospodnju da kadi.
Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
10 I sve mnoštvo naroda bijaše napolju i moljaše se Bogu u vrijeme kaðenja.
Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11 A njemu se pokaza anðeo Gospodnji koji stajaše s desne strane oltara kadionoga.
A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12 I kad ga vidje Zarija uplaši se i strah napade na nj.
Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13 A anðeo reèe mu: ne boj se, Zarija; jer je uslišena tvoja molitva: i žena tvoja Jelisaveta rodiæe ti sina, i nadjeni mu ime Jovan.
Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14 I biæe tebi radost i veselje, i mnogi æe se obradovati njegovu roðenju.
Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15 Jer æe biti veliki pred Bogom, i neæe piti vina i sikera; i napuniæe se Duha svetoga još u utrobi matere svoje;
Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16 I mnoge æe sinove Izrailjeve obratiti ka Gospodu Bogu njihovome;
Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17 I on æe naprijed doæi pred njim u duhu i sili Ilijnoj da obrati srca otaca k djeci, i nevjernike k mudrosti pravednika, i da pripravi Gospodu narod gotov.
Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18 I reèe Zarija anðelu: po èemu æu ja to poznati? jer sam ja star i žena je moja vremenita.
Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19 I odgovarajuæi anðeo reèe mu: ja sam Gavrilo što stojim pred Bogom, i poslan sam da govorim s tobom i da ti javim ovu radost.
Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
20 I evo, onijemiæeš i neæeš moæi govoriti do onoga dana dok se to ne zbude; jer nijesi vjerovao mojim rijeèima koje æe se zbiti u svoje vrijeme.
Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
21 I narod èekaše Zariju, i èuðahu se što se zabavi u crkvi.
Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
22 A izišavši ne mogaše da im govori; i razumješe da mu se nešto utvorilo u crkvi; i on namigivaše im; i osta nijem.
Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
23 I kad se navršiše dani njegove službe otide kuæi svojoj.
Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24 A poslije ovijeh dana zatrudnje Jelisaveta žena njegova, i krijaše se pet mjeseci govoreæi:
Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
25 Tako mi uèini Gospod u dane ove u koje pogleda na me da me izbavi od ukora meðu ljudima.
“Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
26 A u šesti mjesec posla Bog anðela Gavrila u grad Galilejski po imenu Nazaret
A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
27 K djevojci isprošenoj za muža, po imenu Josifa iz doma Davidova; i djevojci bješe ime Marija.
zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
28 I ušavši k njoj anðeo reèe: raduj se, blagodatna! Gospod je s tobom, blagoslovena si ti meðu ženama.
Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
29 A ona vidjevši ga poplaši se od rijeèi njegove i pomisli: kakav bi ovo bio pozdrav?
Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30 I reèe joj anðeo: ne boj se, Marija! Jer si našla milost u Boga.
Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
31 I evo zatrudnjeæeš, i rodiæeš sina, i nadjeni mu ime Isus.
Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
32 On æe biti veliki, i nazvaæe se sin najvišega, i daæe mu Gospod Bog prijesto Davida oca njegova;
Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
33 I carovaæe u domu Jakovljevu vavijek, i carstvu njegovom neæe biti kraja. (aiōn )
Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn )
34 A Marija reèe anðelu: kako æe to biti kad ja ne znam za muža?
Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35 I odgovarajuæi anðeo reèe joj: duh sveti doæi æe na tebe, i sila najvišega osjeniæe te; zato i ono što æe se roditi biæe sveto, i nazvaæe se sin Božij.
Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36 I evo Jelisaveta tvoja tetka, i ona zatrudnje sinom u starosti svojoj, i ovo je šesti mjesec njojzi, koju zovu nerotkinjom.
Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37 Jer u Boga sve je moguæe što reèe.
Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38 A Marija reèe: evo sluškinje Gospodnje; neka mi bude po rijeèi tvojoj. I anðeo otide od nje.
Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39 A Marija ustavši onijeh dana otide brzo u gornju zemlju u grad Judin.
Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40 I uðe u kuæu Zarijinu, i pozdravi se s Jelisavetom.
Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41 I kad Jelisaveta èu èestitanje Marijino, zaigra dijete u utrobi njezinoj, i Jelisaveta se napuni Duha svetoga,
Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42 I povika zdravo i reèe: blagoslovena si ti meðu ženama, i blagosloven je plod utrobe tvoje.
Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43 I otkud meni ovo da doðe mati Gospoda mojega k meni?
Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44 Jer gle, kad doðe glas èestitanja tvojega u uši moje, zaigra dijete radosno u utrobi mojoj.
Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45 I blago onoj koja vjerova; jer æe se izvršiti što joj kaza Gospod.
Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46 I reèe Marija: velièa duša moja Gospoda;
Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47 I obradova se duh moj Bogu spasu mojemu,
kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48 Što pogleda na poniženje sluškinje svoje; jer gle, otsad æe me zvati blaženom svi naraštaji;
Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49 Što mi uèini velièinu silni, i sveto ime njegovo;
Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 I milost je njegova od koljena na koljeno onima koji ga se boje.
Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 Pokaza silu rukom svojom; razasu ponosite u mislima srca njihova.
Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 Zbaci silne s prijestola, i podiže ponižene.
Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 Gladne napuni blaga, i bogate otpusti prazne.
Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 Primi Izrailja slugu svojega da se opomene milosti;
Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 Kao što govori ocima našijem, Avraamu i sjemenu njegovu dovijeka. (aiōn )
(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn )
56 Marija pak sjedi s njom oko tri mjeseca, i vrati se kuæi svojoj.
Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 A Jelisaveti doðe vrijeme da rodi, i rodi sina.
Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 I èuše njezini susjedi i rodbina da je Gospod pokazao veliku milost svoju na njoj, i radovahu se s njom.
Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 I u osmi dan doðoše da obrežu dijete, i šæadijahu da mu nadjenu ime oca njegova, Zarija.
Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 I odgovarajuæi mati njegova reèe: ne, nego da bude Jovan.
amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 I rekoše joj: nikoga nema u rodbini tvojoj da mu je tako ime.
Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 I namigivahu ocu njegovu kako bi on htio da mu nadjenu ime.
Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 I zaiskavši dašèicu, napisa govoreæi: Jovan mu je ime. I zaèudiše se svi.
Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 I odmah mu se otvoriše usta i jezik njegov, i govoraše hvaleæi Boga.
Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 I uðe strah u sve susjede njihove; i po svoj gornjoj Judeji razglasi se ovaj sav dogaðaj.
Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 I svi koji èuše metnuše u srce svoje govoreæi: šta æe biti iz ovoga djeteta? I ruka Gospodnja bješe s njim.
Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 I Zarija otac njegov napuni se Duha svetoga, i prorokova govoreæi:
Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 Blagosloven Gospod Bog Jakovljev što pohodi i izbavi narod svoj,
“Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 I podiže nam rog spasenija u domu Davida sluge svojega,
Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 Kao što govori ustima svetijeh proroka svojijeh od vijeka (aiōn )
kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn )
71 Da æe nas izbaviti od našijeh neprijatelja i iz ruku sviju koji mrze na nas;
Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 Uèiniti milost ocima našijem, i opomenuti se svetoga zavjeta svojega,
Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 Kletve kojom se kleo Avraamu ocu našemu da æe nam dati
rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
74 Da se izbavimo iz ruku neprijatelja svojijeh, i da mu služimo bez straha,
Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
75 I u svetosti i u pravdi pred njim dok smo god živi.
a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76 I ti, dijete, nazvaæeš se prorok najvišega; jer æeš iæi naprijed pred licem Gospodnjijem da mu pripraviš put;
I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
77 Da daš razum spasenija narodu njegovu za oproštenje grijeha njihovijeh,
domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78 Po dubokoj milosti Boga našega, po kojoj nas je pohodio istok s visine;
Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
79 Da obasjaš one koji sjede u tami i u sjenu smrtnome; da uputiš noge naše na put mira.
domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80 A dijete rastijaše i jaèaše duhom, i bijaše u pustinji dotle dok se ne pokaza Izrailju.
Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.