< Isus Navin 17 >

1 I dopade dio plemenu Manasijinu, a on bješe prvenac Josifov; Mahiru prvencu Manasijinu ocu Galadovu, jer bješe èovjek junak, zato mu dopade Galad i Vasan;
Wannan shi ne gādon da aka ba wa kabilar Manasse, a matsayin ɗan farin Yusuf. Manasse yana da ɗan farin mai suna Makir. Makir shi ne mahaifin mutanen Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan gama Makiriyawa jarumai ne ƙwarai.
2 Dobiše dio i ostali sinovi Manasijini po porodicama svojim, sinovi Avijezerovi, i sinovi Helekovi, i sinovi Azrilovi, i sinovi Sihemovi, i sinovi Eferovi, i sinovi Semidini. To su sinovi Manasije sina Josifova; ljudi po porodicama svojim.
Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manasse rabon gādonsu bisa ga iyalansu, wato, Abiyezer, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer da Shemida. Waɗannan su ne’ya’yan Manasse, maza, ɗan Yusuf bisa ga iyalansu.
3 A Salpad sin Efera sina Galada sina Mahira sina Manasijina nije imao sinova nego kæeri; i ovo su imena kæerima njegovijem: Mala i Nuja, Egla, Melha i Tersa.
Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse ba shi da’ya’ya maza, sai dai mata. Ga sunayensu, Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.
4 I one doðoše pred Eleazara sveštenika i pred Isusa sina Navina i pred knezove, i rekoše: Gospod je zapovjedio Mojsiju da nam se dade našljedstvo meðu braæom našom. I dade im Isus po zapovijesti Gospodnjoj našljedstvo meðu braæom oca njihova.
Suka je wurin Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin, suka ce musu, “Ubangiji ya umarci Musa cewa yă ba mu gādonmu tare da’yan’uwanmu maza.” Saboda haka Yoshuwa ya ba su gādo tare da’yan’uwan mahaifinsu maza bisa ga umarnin Ubangiji.
5 I dopade Manasiji deset dijelova, osim zemlje Galadske i Vasanske, koje su s onu stranu Jordana.
Dalilin ke nan Manasse ya sami kashi goma ban da ƙasar Gileyad da Bashan a gabashin Urdun,
6 Jer kæeri Manasijine dobiše našljedstvo meðu sinovima njegovijem, a zemlja Galadska dopade drugim sinovima Manasijinim.
domin’ya’ya mata na kabilar Manasse sun sami gādo tare da’ya’ya maza. Aka ba wa sauran mutanen kabilar Manasse ƙasar Gileyad.
7 A meða Manasijina bješe od Asira k Mihmeti, koja je prema Sihemu, potom ide ta meða nadesno k stanovnicima En-Tafujskim.
Iyakar ƙasar Manasse ta tashi daga Asher zuwa Mikmetat a gabashin Shekem. Iyakar kuma ta miƙe har zuwa kudu wadda ta ƙunshi mutanen da suke zaune a En Taffuwa.
8 A Manasijina je zemlja Tafujska, ali Tafuja na meði Manasijinoj pripada sinovima Jefremovijem.
(Manasse ne yake da ƙasar Taffuwa, amma garin Taffuwa kansa, a kan iyakar Manasse ta mutanen Efraim ce.)
9 Odatle slazi meða na potok Kanu, s južne strane toga potoka; i gradovi su Jefremovi meðu gradovima Manasijinim; a meða je Manasijina sa sjeverne strane potoka i izlazi na more.
Sa’an nan iyakar ta ci gaba ta yi kudu zuwa Rafin Kana. Akwai garuruwan da suke kudancin rafin, waɗanda suke Efraim, ko da yake suna cikin yankin Manasse. Iyakar Manasse ta miƙe zuwa arewa ta bi gefen rafin ta kuma ƙarasa a Bahar Rum.
10 S juga je Jefremovo, a sa sjevera Manasijino, a more im je meða; i s Asirom granièe na sjeveru a s Isaharom na istoku.
Ƙasar a wajen kudu ta Efraim ce, ta wajen arewa kuma ta Manasse ce. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Asher yana wajen arewa, Issakar kuma a wajen gabas.
11 Jer je Manasijino u plemenu Isaharovu i Asirovu: Vet-San sa selima svojim, i Ivleam sa selima svojim, i Dorani sa selima svojim, i En-Dorani sa selima svojim, i Tanašani sa selima svojim, i Megiðani sa selima svojim; ta tri kraja.
A yanki tsakanin Issakar da Asher, Manasse yana da waɗannan wurare, Bet-Sheyan, Ibileyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan En Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta’anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta (Na uku cikin jerin shi ne Nafot).
12 Ali sinovi Manasijini ne mogoše izagnati Hananeja iz tijeh gradova, nego Hananeji stadoše živjeti u toj zemlji.
Duk da haka mutanen Manasse ba su iya mallakar garuruwan nan ba, domin Kan’aniyawa sun nace da zama a wannan yanki.
13 Ali kad ojaèaše sinovi Izrailjevi, udariše danak na Hananeje, ali ih ne izagnaše.
Da Isra’ilawa suka yi ƙarfi, sai suka sa Kan’aniyawa suka zama masu yin musu aiki, amma ba su iya korarsu duka ba.
14 A sinovi Josifovi rekoše Isusu govoreæi: zašto si nam dao u našljedstvo jedan dio i jedno uže, kad je nas množina i Gospod nas je blagoslovio dovde?
Mutanen Yusuf kuwa suka ce wa Yoshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo ɗaya kawai? Ga shi muna da yawa kuma Ubangiji ya albarkace mu sosai.”
15 A Isus im reèe: kad vas je množina, idite u šumu, i ondje okrèite sebi u zemlji Ferezejskoj i Rafajskoj, ako vam je tijesna gora Jefremova.
Yoshuwa ya ce musu, “In kuna da yawa sosai, in kuma ƙasar kan tudu ta Efraim ba ta ishe ku ba, sai ku je cikin jeji, ku nema wa kanku ƙasa a ƙasar Ferizziyawa da Refahiyawa.”
16 A sinovi Josifovi rekoše: neæe nam biti dosta ova gora; a svi Hananeji koji žive u dolini imaju gvozdena kola; i oni koji su u Vet-Sanu i u selima njegovijem i oni koji su u dolini Jezraelskoj.
Mutanen Yusuf suka amsa suka ce, “Ƙasar kan tudu ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan’aniyawan da suke zama a filin, da waɗanda suke Bet-Sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke Kwarin Yezireyel, duk suna da keken yaƙin ƙarfe.”
17 A Isus reèe domu Josifovu, Jefremu i Manasiji, govoreæi: velik si narod i silan si, neæeš imati jednoga dijela.
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Yusuf, wa Efraim da Manasse, “Kuna da yawa, kuna kuma da ƙarfi sosai. Ba wuri ɗaya kaɗai za ku samu gādo ba,
18 Nego gora neka bude tvoja; ako je šuma, isijeci je, pak æeš imati meðe njezine; jer æeš izagnati Hananeje, ako i imaju gvozdena kola, ako i jesu jaki.
amma har da ƙasar kan tudu ma, ko da yake jeji ne, ku je ku gyara shi, duk yă zama naku. Ko da yake Kan’aniyawa suna da kekunan yaƙi na ƙarfe, suna kuma da ƙarfi, duk da haka za ku kore su.”

< Isus Navin 17 >