< Jeremija 28 >

1 A iste godine, u poèetku carovanja Sedekije cara Judina, èetvrte godine, petoga mjeseca, reèe mi Ananija sin Azorov, prorok iz Gavaona, u domu Gospodnjem pred sveštenicima i svijem narodom govoreæi:
A wata na biyar na wannan shekara, shekara ta huɗu, a farkon sarautar Zedekiya sarkin Yahuda, sai annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibeyon, ya zo wurina a gidan Ubangiji a gaban firistoci da kuma dukan mutane,
2 Ovako veli Gospod nad vojskama Bog Izrailjev: slomih jaram cara Vavilonskoga.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Zan karya karkiyar sarkin Babilon.
3 Do dvije godine ja æu vratiti na ovo mjesto sve sudove doma Gospodnjega, koje uze Navuhodonosor car Vavilonski odavde i odnese u Vavilon.
Cikin shekaru biyu zan komo da dukan kayayyakin gidan Ubangiji da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe daga wannan wuri ya kai Babilon.
4 I Jehoniju sina Joakimova cara Judina i sve roblje Judino što otide u Vavilon, ja æu dovesti opet na ovo mjesto, govori Gospod, jer æu slomiti jaram cara Vavilonskoga.
Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da kuma dukan sauran masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suka tafi Babilon,’ in ji Ubangiji, ‘gama zan karya karkiyar sarkin Babilon.’”
5 Tada reèe Jeremija prorok Ananiji proroku pred sveštenicima i pred svijem narodom, koji stajaše u domu Gospodnjem,
Sai annabi Irmiya ya amsa wa annabi Hananiya a gaban firistoci da kuma dukan mutane waɗanda suke tsaye a gidan Ubangiji.
6 Reèe Jeremija prorok: amin, da Gospod uèini tako, da Gospod ispuni tvoje rijeèi što si prorokovao da bi vratio sudove doma Gospodnjega i sve roblje iz Vavilona na ovo mjesto.
Ya ce, “Amin! Ubangiji yă sa yă zama haka! Ubangiji yă cika maganar da ka yi annabci ta wurin komo da kayayyakin gidan Ubangiji da kuma dukan masu zaman bauta zuwa wannan wuri daga Babilon.
7 Ali èuj ovu rijeè koju æu ja kazati pred tobom i pred svijem narodom:
Duk da haka, ka saurari abin da zan faɗa a kunnenka da kuma a kunnen duka mutane,
8 Proroci koji su bili prije mene i prije tebe od starine, oni prorokovaše mnogim zemljama i velikim carstvima rat i nevolju i pomor.
Daga farko fari annabawan da suka riga ka da ni sun yi annabcin yaƙi, masifa da annoba a kan ƙasashe masu yawa da kuma manyan mulkoki.
9 Prorok koji prorièe mir, kad se zbude rijeè toga proroka, onda se poznaje taj prorok da ga je zaista poslao Gospod.
Amma annabin da ya yi annabcin salama shi za a ɗauka a matsayin wanda Ubangiji ya aika in har abin da ya furta ya zama gaskiya.”
10 Tada Ananija prorok skide jaram s vrata Jeremiji proroku i slomi ga.
Sai annabi Hananiya ya cire karkiya daga wuyar annabi Irmiya ya karya ta,
11 I reèe Ananija pred svijem narodom govoreæi: ovako veli Gospod: ovako æu slomiti jaram Navuhodonosora cara Vavilonskoga do dvije godine s vrata svijeh naroda. I otide prorok Jeremija svojim putem.
ya ce a gaban dukan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘A haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar sarkin Babilon daga wuyan dukan al’ummai a cikin shekaru biyu.’” Da wannan, annabi Irmiya ya yi tafiyarsa.
12 Ali doðe rijeè Gospodnja Jeremiji, pošto slomi Ananija prorok jaram s vrata Jeremiji proroku, i reèe:
Ba a daɗe ba bayan annabi Hananiya ya karya karkiya daga wuyan annabi Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
13 Idi i kaži Ananiji i reci: ovako veli Gospod: slomio si jaram drveni, ali naèini mjesto njega gvozden jaram.
“Je ka faɗa wa Hananiya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka karya karkiyar katako, amma a wurinsa za ka sami karkiyar ƙarfe.
14 Jer ovako veli Gospod nad vojskama Bog Izrailjev: gvozden æu jaram metnuti na vrat svijem tijem narodima da služe Navuhodonosoru caru Vavilonskom, i služiæe mu, dao sam mu i zvijerje poljsko.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa zan sa karkiyar ƙarfe a wuyan dukan waɗannan al’ummai don in sa su bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon, za su kuwa bauta masa. Zan ma sa shi ya mallaki namun jeji.’”
15 Potom reèe Jeremija prorok Ananiji proroku: èuj, Ananija; nije te poslao Gospod, a ti si uèinio da se narod ovaj pouzda u laž.
Sa’an nan annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka saurara, Hananiya! Ubangiji bai aike ka ba, duk da haka ka lallashe wannan al’umma su dogara ga ƙarya.
16 Zato ovako veli Gospod: evo, ja æu te skinuti sa zemlje, ove godine ti æeš umrijeti; jer si kazivao odmet od Gospoda.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Ina shirin kawar da kai daga fuskar duniya. A wannan shekara za ka mutu, domin ka yi wa’azin tawaye a kan Ubangiji.’”
17 I umrije prorok Ananija te godine sedmoga mjeseca.
A wata na bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.

< Jeremija 28 >