< Postanak 15 >

1 Poslije ovijeh stvari doðe Avramu rijeè Gospodnja u utvari govoreæi: ne boj se, Avrame, ja sam ti štit, i plata je tvoja vrlo velika.
Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
2 A Avram reèe: Gospode, Gospode, šta æeš mi dati kad živim bez djece, a na kom æe ostati moja kuæa to je Elijezer ovaj Damaštanin?
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
3 Još reèe Avram: eto meni nijesi dao poroda, pa æe sluga roðen u kuæi mojoj biti moj našljednik.
Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
4 A gle, Gospod mu progovori: neæe taj biti našljednik tvoj, nego koji æe izaæi od tebe taj æe ti biti našljednik.
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
5 Pa ga izvede napolje i reèe mu: pogledaj na nebo i prebroj zvijezde, ako ih možeš prebrojiti. I reèe mu: tako æe biti sjeme tvoje.
Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
6 I povjerova Avram Bogu, a on mu primi to u pravdu.
Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
7 I reèe mu: ja sam Gospod, koji te izvedoh iz Ura Haldejskoga da ti dam zemlju ovu da bude tvoja.
Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
8 A on reèe: Gospode, Gospode, po èemu æu poznati da æe biti moja?
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
9 I reèe mu: prinesi mi junicu od tri godine i kozu od tri godine i ovna od tri godine i grlicu i golupèe.
Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
10 I on uze sve to, i rasijeèe na pole, i metnu sve pole jednu prema drugoj; ali ne rasijeèe ptica.
Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
11 A ptice slijetahu na te mrtve životinje; a Avram ih odgonjaše.
Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
12 A kad sunce bješe na zahodu, uhvati Avrama tvrd san, i gle, strah i mrak velik obuze ga.
Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
13 I Gospod reèe Avramu: znaj zacijelo da æe sjeme tvoje biti došljaci u zemlji tuðoj, pa æe joj služiti, i ona æe ih muèiti èetiri stotine godina.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
14 Ali æu suditi i narodu kojemu æe služiti; a poslije æe oni izaæi s velikim blagom.
Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
15 A ti æeš otiæi k ocima svojim u miru, i biæeš pogreben u dobroj starosti.
Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
16 A oni æe se u èetvrtom koljenu vratiti ovamo; jer grijesima Amorejskim još nije kraj.
A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
17 A kad se sunce smiri i kad se smrèe, gle, peæ se dimljaše, i plamen ognjeni prolažaše izmeðu onijeh dijelova.
Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
18 Taj dan uèini Gospod zavjet s Avramom govoreæi: sjemenu tvojemu dadoh zemlju ovu od vode Misirske do velike vode, vode Efrata,
A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
19 Kenejsku, Kenezejsku i Kedmonejsku,
ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
20 I Hetejsku i Ferezejsku i Rafajsku,
Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
21 I Amorejsku i Hananejsku i Gergesejsku i Jevusejsku.
Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”

< Postanak 15 >