< Izlazak 22 >
1 Ko ukrade vola ili ovcu ili kozu, i zakolje ili proda, da vrati pet volova za jednoga vola, a èetiri ovce ili koze za jednu ovcu ili kozu.
“In mutum ya saci saniya ko tunkiya ya yanka, ko ya sayar, zai biya shanu biyar, a maimakon saniyar da ya sata, ko kuma tumaki huɗu, maimakon tunkiyar da ya sata.
2 Ako se lupež uhvati gdje potkopava, te bude ranjen tako da umre, da ne bude kriv za krv onaj koji ga bude ubio;
“In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga yă yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa daga wurin kowa ba;
3 Ali ako se bude sunce rodilo, da je kriv za krv. A lupež sve da naknadi; ako li ne bi imao, onda da se on proda za svoju kraðu.
amma in ya faru bayan wayewar gari, to, za a nemi alhakin jinin ɓarawon a hannun wanda ya bugi ɓarawon. “Ɓarawon da aka kama da abin da ya sata, dole yă yi cikakkiyar ramuwa, amma in ba shi da kome, dole a sayar da shi a biya abin da ya sata.
4 Ako se naðe što je pokrao u njegovoj ruci živo, bio vo ili magarac ili ovca ili koza, da vrati dvostruko.
In an sami dabbar, ko saniya, ko jaki, ko tunkiya da ya sata da rai a hannunsa, dole ɓarawon yă biya taran da za a ci shi, sau biyu na kowane ɗaya.
5 Ko potre njivu ili vinograd pustivši stoku svoju da pase po tuðoj njivi, da naknadi najboljim sa svoje njive i najboljim iz svoga vinograda.
“In mutum ya sa dabbobinsa su yi kiwo a fili ko a gonar inabi, ya kuma bar dabbobinsa suka yi ɓarna a cikin gonar wani, sai a sa mai dabbar yă biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka.
6 Ako izaðe vatra i naiðe na trnje, pa izgori stog ili žito koje još stoji ili njiva, da naknadi onaj koji je zapalio.
“In gobara ta tashi, ta kuma bazu cikin ƙayayyuwa, har ta cinye tarin hatsi, ko hatsin da ke tsaye, ko dukan gonar, dole wanda ya sa wutar, yă biya taran da aka yanka masa saboda ɓarnan da wutar ta yi.
7 Ako ko da bližnjemu svojemu novce ili posuðe na ostavu, pa se ukrade iz kuæe njegove, ako se naðe lupež, da plati dvojinom;
“In mutum ya ba maƙwabcinsa azurfa, ko kaya ajiya, aka kuma sace su daga gidan maƙwabcin, in an kama ɓarawon, sai ɓarawon yă biya abin da ya sata har sau biyu.
8 Ako li se ne naðe lupež, onda gospodar od one kuæe da stane pred sudije da se zakune da nije posegao rukom svojom na stvar bližnjega svojega.
Amma in ba a sami ɓarawon ba, sai wanda aka yi ajiyar a gidansa, yă bayyana a gaban alƙalai a bincika ko yana da hannu a kan kayan maƙwabcinsa.
9 Za svaku stvar za koju bi bila raspra, ili za vola ili za magarca ili za ovcu ili za kozu, ili za haljinu, za svaku stvar izgubljenu, kad ko kaže da je njegova, pred sudije da doðe raspra obojice, pa koga osude sudije, onaj da vrati bližnjemu svojemu dvojinom.
A kowane rikicin cin amana da zai shiga tsakanin mutum biyu, ko a kan bijimi, ko jaki, ko tunkiya, ko riga, kai, ko a kan kowane irin abin da ya ɓata, da ma abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin a gaban alƙalai. Wanda alƙali ya ce shi ne mai laifi, sai yă biya ɗayan taran da za a yanka, har sau biyu.
10 Ako ko da bližnjemu svojemu da èuva magarca ili vola ili ovcu ili kozu ili kako god živinèe, pa ugine ili ohrone, ili ga ko otjera a da niko ne vidi,
“In mutum ya ba da jaki, ko saniya, ko tunkiya, ko kowace dabba wa maƙwabcinsa ajiya, sai abin ya mutu, ko ya ji rauni, ko an ɗauke shi, in ba shaida,
11 Zakletva Gospodnja neka bude izmeðu njih, da nije posegao rukom svojom na stvar bližnjega svojega, i gospodar od stvari neka pristane, a onaj da ne plati.
rantsuwa ce za tă raba tsakaninsu a gaban Ubangiji cewa babu hannunsa a dukiyar maƙwabcinsa. Mai dukiyar kuwa zai yarda da rantsuwar, ba za a bukaci wanda aka bai wa amanar yă biya ba.
12 Ako li mu bude ukradeno, neka plati gospodaru njegovu.
Amma idan satan dabbar ce aka yi, dole wanda aka bai wa ajiyar yă biya mai dabbar taran da aka ci masa.
13 Ako li ga bude rastrgla zvjerka da donese od njega svjedodžbu, i da ne plati što je rastrgnuto.
In naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shaida, ba za a kuwa sa maƙwabcin yă biya abin da naman jeji ya kashe ba.
14 Ako ko uzme u bližnjega svojega živinèe na poslugu, pa ohrone ili ugine, a gospodar mu ne bude kod njega, da plati.
“In mutum ya yi aron dabba daga wurin maƙwabcinsa, sai dabbar ta ji rauni ko ta mutu, yayinda mai shi ba ya nan, dole wanda ya yi aron dabbar yă biya.
15 Ako li gospodar bude kod njega, da ne plati. Ako li bude najmljeno, da plati samo najam.
Amma idan mai dabbar yana a wurin, wanda ya karɓa aron, ba zai biya kome ba. In an yi hayar dabbar ce, to, kuɗin da aka biya na hayar zai zama a madadin rashin.
16 Ko bi prevario djevojku, koja nije zaruèena, te bi spavao s njom, da joj da præiju i uzme je za ženu.
“Idan mutum ya ruɗe budurwa, wadda ba wanda yake nemanta, ya kuma kwanta da ita, dole yă biya kuɗin aurenta, za tă kuma zama matarsa.
17 A ako mu je otac njezin ne bi htio dati, da da novaca koliko ide u præiju djevojci.
In mahaifinta ya ƙi yă ba da ita ga mutumin, dole mutumin yă biya dukiya daidai da abin da akan biya domin budurwai.
18 Vještici ne daj da živi.
“Kada ku bar maiya da rai.
19 Ko bi obležao živinèe, da se pogubi.
“Duk mutumin da ya yi jima’i da dabba dole a kashe shi.
20 Ko žrtvu prinosi bogovima drugim osim jedinoga Gospoda, da se istrijebi kao prokletnik.
“Duk wanda ya yi hadaya ga wani allah ban da Ubangiji, dole a hallaka shi.
21 Došljaku nemoj èiniti krivo niti ga cvijeliti, jer ste bili došljaci u zemlji Misirskoj.
“Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
22 Nemojte cvijeliti udovice i sirote.
“Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.
23 Ako li koju cvijeliš u èem god, i povièe k meni, èuæu viku njezinu,
In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.
24 I zapaliæe se gnjev moj, i pobiæu vas maèem, pa æe vaše žene biti udovice i vaša djeca sirote.
Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye,’ya’yanku kuwa su zama marayu.
25 Kad daš u zajam novaca narodu mojemu, siromahu koji je kod tebe, nemoj mu biti kao kamatnik, ne udarajte na nj kamate.
“In kun ba wa jama’ata matalauta da suke tsakaninku bashin kuɗi, kada ku zama kamar masu ba da rance; kada ku sa yă biya da ruwa.
26 Ako uzmeš u zalogu haljinu bližnjemu svojemu, vrati mu je prije nego sunce zaðe;
In kun ɗauki mayafi maƙwabcinku a matsayin jingina, ku mayar masa kafin fāɗuwar rana,
27 Jer mu je to sve odijelo èim zaklanja tijelo svoje; u èem æe spavati? pa kad povièe k meni, ja æu ga èuti, jer sam milostiv.
domin mayafin ne abin da yake da shi na rufe jikinsa. To, da me zai rufu yă yi barci? Sa’ad da ya yi mini kuka, zan ji, gama ni mai tausayi ne.
28 Nemoj psovati sudija, i starješini naroda svojega ne govori ružno.
“Kada ku yi maganar saɓo ga Allah, ko ku la’anta mai mulkin mutanenku.
29 Od ljetine svoje i od žitkih stvari svojih nemoj se zatezati da prineseš prvine; prvenca izmeðu sinova svojih meni da daš.
“Kada ku jinkirta fitar da zakarku daga rumbunanku, ko harajin kayan da kuka saya. “Dole ku ba ni’ya’yan farinku maza.
30 Tako èini s volom svojim i s ovcom i s kozom; sedam dana neka bude s majkom svojom, a osmoga dana da ga daš meni.
Ku yi haka da shanunku da tumakinku. Bari su kasance da iyayensu mata, har kwana bakwai, amma ku ba ni su a rana ta takwas.
31 Biæete mi sveti ljudi; mesa u polju rastrgnuta ne jedite, bacite ga psima.
“Za ku kasance mutanena masu tsarki. Saboda kada ku ci naman da namun jeji suka kashe; ku jefa wa karnuka.