< Danilo 6 >
1 Svidje se Dariju te postavi nad carstvom sto i pedeset upravitelja da budu nad svijem carstvom;
Ya gamshi Dariyus ya naɗa muƙaddasai 120 su yi shugabanci a duk fāɗin masarautar,
2 A nad njima tri starješine, od kojih jedan bješe Danilo, kojima æe upravitelji davati raèune da ne bi caru bilo štete.
ya naɗa mutum uku a bisa waɗannan muƙaddasan, Daniyel yana ɗaya daga cikin mutum ukun nan. Sai aka sa muƙaddasan nan a ƙarƙashin waɗannan uku ɗin domin kada sarki ya yi hasarar kome.
3 A taj Danilo nadvišivaše starješine i upravitelje, jer u njemu bješe velik duh i car mišljaše da ga postavi nad svijem carstvom svojim.
To, Daniyel dai ya yi ficce a cikin shugabannin nan uku har da muƙaddasan ma, saboda waɗansu halaye nagari da yake da su, wanda ya sa sarki ya yi shiri ya ɗora shi a kan dukan mulkinsa.
4 Tada starješine i upravitelji gledahu kako bi našli što da zabave Danilu radi carstva; ali ne mogahu naæi zabave ni pogrješke, jer bješe vjeran, i ne nalažaše se u njega pogrješke ni mane.
A kan haka, shugabannin nan uku da muƙaddasan nan suka yi ƙoƙari su sami wani laifi a kan Daniyel a yadda yake tafiyar da aikin shugabancinsa, amma ba su samu ba. Ba su same shi da wani laifin cin hanci ba, domin shi amintacce ne kuma babu wani aibi a kansa ko rashin kula.
5 Tada rekoše oni ljudi: neæemo naæi na toga Danila ništa, ako ne naðemo što na nj radi zakona Boga njegova.
A ƙarshe waɗannan mutane suka ce; “Ba za mu taɓa samun wani laifin da za mu kama Daniyel da shi ba, sai dai ko abin ya shafi dokar Allahnsa.”
6 Tada doðoše starješine i upravitelji k caru, i rekoše mu ovako: Darije care, da si živ dovijeka.
Saboda haka shugabannin nan suka haɗu da muƙaddasan nan suka tafi wurin sarki a ƙungiyance suka ce, “Ya Sarki Dariyus, ranka yă daɗe!
7 Sve starješine u carstvu, poglavari i upravitelji, vijeænici i vojvode dogovoriše se da se postavi carska naredba i oštra zabrana da ko bi se god zamolio za što kome god bogu ili èovjeku za trideset dana osim tebi, care, da se baci u jamu lavovsku.
Shugabannin masarauta, da masu mulki, da muƙaddasai, da mashawarta da gwamnoni duk sun amince cewa sarki yă kafa doka yă kuma yi umarni cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda ya yi addu’a ga wani allah ko mutum, in ba a gare ka ba, ya sarki, jefa shi cikin kogon zakoki.
8 Zato, care, postavi tu zabranu i napiši da se ne može promijeniti, po zakonu Midskom i Persijskom, koji je nepromjenit.
Yanzu, ya sarki, sai ka yi umarni ka kuma yi shi a rubuce saboda kada a canja shi, bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
9 I car Darije napisa knjigu i zabranu.
Sai Sarki Dariyus ya ba da umarnin a rubuce.
10 A Danilo kad dozna da je knjiga napisana, otide svojoj kuæi, gdje bijahu otvoreni prozori u njegovoj sobi prema Jerusalimu, i padaše na koljena svoja tri puta na dan i moljaše se i hvalu davaše Bogu svojemu kao što èinjaše prije.
To, da Daniyel ya ji labarin cewa an fitar da doka, sai ya tafi gidansa a ɗakinsa na sama inda tagogin ɗakin suke duban wajen Urushalima. Sau uku yakan durƙusa yă yi addu’a yana yin godiya ga Allahnsa, kamar yadda ya saba yi.
11 Tada se sabraše oni ljudi, i naðoše Danila gdje se moli i pripada Bogu svojemu.
Sai waɗannan mutane suka tafi a ƙungiyance suka kuma iske Daniyel yana addu’a yana roƙon Allah yă taimake shi.
12 I otidoše te rekoše caru za carsku zabranu: nijesi li napisao zapovijest, da ko bi se god zamolio kome god bogu ili èovjeku za trideset dana, osim tebi, care, da se baci u jamu lavovsku? Car odgovori i reèe: tako je po zakonu Midskom i Persijskom, koji je nepromjenit.
Sai suka tafi wurin sarki suka yi masa magana game da dokar mulkinsa, suka ce, “Ashe, ba ka yi doka cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda aka tarar yana addu’a ga wani allah ko mutum in ba kai ba, ya sarki, za ka jefa shi a cikin ramin zakoki ba?” Sarki ya amsa ya ce, “Dokar tana nan daram bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
13 Tada odgovoriše i rekoše caru: Danilo, koji je izmeðu roblja Judina, ne haje za te, care, ni za zabranu koju si napisao, nego se moli tri puta na dan svojom molitvom.
Sai suka ce wa sarki, “Daniyel ɗin nan, wanda yake ɗaya daga cikin waɗanda aka kwaso daga Yahuda, bai kula da kai ba, ya sarki, balle fa dokar da ka yi. Har yanzu yana addu’a sau uku a rana.”
14 Tada car èuvši to ožalosti se vrlo, i naumi da izbavi Danila, i truðaše se do zahoda sunèanoga da ga izbavi.
Da sarki ya ji haka, sai ya damu sosai, ya ƙudura yă ceci Daniyel, ya yi ta fama har fāɗuwar rana yadda zai yi yă kuɓutar da shi.
15 Tada oni ljudi sabraše se kod cara i rekoše caru: znaj, care, da je zakon u Midijana i Persijana da se nikakva zabrana i naredba, koju postavi car, ne mijenja.
Sai mutanen nan suka je wurin sarki a ƙungiyance suka ce masa, “Ka tuna, ya sarki; cewa bisa ga dokar Medes da Farisa, babu umarni ko dokar da sarki ya yi da za a iya sokewa.”
16 Tada car reèe te dovedoše Danila i baciše ga u jamu lavovsku; i car progovori i reèe Danilu: Bog tvoj, kojemu bez prestanka služiš, neka te izbavi.
Saboda haka sai sarki ya ba da umarni suka kuma kawo Daniyel suka jefa shi cikin ramin zakoki. Sarki ya ce wa Daniyel, “Bari Allahn nan wanda kake bauta masa kullum, yă cece ka!”
17 I donesoše kamen i metnuše jami na vrata, i car ga zapeèati svojim prstenom i prstenom svojih knezova da se ništa ne promijeni za Danila.
Aka kawo dutsen aka rufe bakin ramin, sa’an nan sarki ya hatimce shi da zobensa da kuma zoban manyan mutanensa, don kada wani yă canja yanayin Daniyel.
18 Tada otide car u svoj dvor, i prenoæi ne jedavši niti dopustivši da mu se donese što èim bi se razveselio, i ne može zaspati.
Sa’an nan sarki ya koma fadarsa ya kwana bai ci ba, kuma babu wata liyafar da aka kawo masa. Ya kuma kāsa barci.
19 Potom car usta ujutru rano i otide brže k jami lavovskoj.
Gari yana wayewa, sai sarki ya tashi ya hanzarta zuwa ramin zakoki.
20 I kad doðe k jami, viknu Danila žalosnijem glasom; i progovori car i reèe Danilu: Danilo, slugo Boga živoga, Bog tvoj, kojemu služiš bez prestanka, može li te izbaviti od lavova?
Da ya yi kusa da ramin zakokin, sai ya kira Daniyel da muryar mai cike da damuwa ya ce, “Daniyel bawan Allah mai rai, ko Allahn nan naka wanda kake bauta wa kullum, ya iya cetonka daga zakoki?”
21 Tada Danilo reèe caru: care, da si živ dovijeka!
Sai Daniyel ya amsa ya ce, “Ran sarki, yă daɗe!
22 Bog moj posla anðela svojega i zatvori usta lavovima, te mi ne naudiše; jer se naðoh èist pred njim, a ni tebi, care, ne uèinih zla.
Allahna ya aiko da mala’ikansa, ya kuwa rufe bakunan zakoki. Ba su yi mini rauni ba, gama an same ni marar laifi ne a gabansa. Ban kuwa taɓa yin wani abu marar kyau a gabanka ba, ya sarki.”
23 Tada se car veoma obradova tomu, i zapovjedi da izvade Danila iz jame. I izvadiše Danila iz jame, i ne naðe se rane na njemu, jer vjerova Bogu svojemu.
Sai sarki ya cika da murna ƙwarai, ya kuma yi umarni a ciro Daniyel daga ramin zakoki. Kuma da aka fito da Daniyel daga ramin, ba a sami wani rauni a jikinsa ba, domin ya dogara ga Allahnsa.
24 Potom zapovjedi car, te dovedoše ljude koji bijahu optužili Danila, i baciše u jamu lavovsku njih, djecu njihovu i žene njihove; i još ne doðoše na dno jami, a lavovi ih zgrabiše i sve im kosti potrše.
Sai sarki ya umarta, a kawo mutanen nan da suka yi wa Daniyel maƙarƙashiya, a tura su, da’ya’yansu, da matansu cikin ramin zakoki. Kafin ma su kai ƙurewar ramin, sai zakoki suka hallaka su suka yayyage su, suka yi kaca-kaca da su.
25 Tada car Darije pisa svijem narodima i plemenima i jezicima što življahu u svoj zemlji: mir da vam se umnoži.
Sa’an nan Sarki Dariyus ya rubuta wa dukan mutane, da al’ummai da kuma mutanen dukan harsunan a duk fāɗin ƙasar. “Bari yă yi nasara sosai!
26 Od mene je zapovijest da se u svoj državi carstva mojega svak boji i straši Boga Danilova, jer je on Bog živi, koji ostaje dovijeka, i carstvo se njegovo neæe rasuti, i vlast æe njegova biti do kraja;
“Na fitar da doka cewa a cikin dukan iyakar ƙasar mulkina, dole mutane su ji tsoro su kuma girmama Allah na Daniyel.
27 On izbavlja i spasava, i èini znake i èudesa na nebu i na zemlji, on je izbavio Danila od sile lavovske.
Yakan kuɓutar ya kuma ceci;
28 I taj Danilo bijaše sreæan za carovanja Darijeva i za carovanja Kira Persijanca.
Daniyel kuwa ya bunkasa a lokacin mulkin Dariyus da kuma mulkin Sairus na Farisa.