< Dela apostolska 5 >
1 A jedan èovjek, po imenu Ananija, sa ženom svojom Sapfirom prodade njivu,
To wani mutum mai suna Ananiyas tare da matarsa Saffiratu, shi ma ya sayar da wata mallakarsa.
2 I sakri od novaca sa znanjem i žene svoje, i donesavši jedan dijel metnu apostolima pred noge.
Da cikakken sanin matarsa ya ajiye sashi daga cikin kuɗin don kansa, ya kuma kawo sauran ya ajiye a sawun manzanni.
3 A Petar reèe: Ananija! zašto napuni sotona srce tvoje da slažeš Duhu svetome i sakriješ od novaca što uze za njivu?
Sai Bitrus ya ce, “Ananiyas, ta yaya Shaiɗan ya cika zuciyarka haka da ka yi wa Ruhu Mai Tsarki ƙarya ka kuma ajiye wa kanka sauran kuɗin da ka karɓa na filin?
4 Kad je bila u tebe ne bješe li tvoja? I kad je prodade ne bješe li u tvojoj vlasti? Zašto si dakle takovu stvar metnuo u srce svoje? Ljudima nijesi slagao nego Bogu.
Ba naka ba ne kafin ka sayar da shi? Bayan da ka sayar da shi kuma, kuɗin ba naka ba ne? Me ya sa ka yi tunanin yin irin wannan abu? Ba mutum ne ka yi wa ƙarya ba, Allah ne ka yi masa.”
5 A kad èu Ananija rijeèi ove, pade i izdahnu; i uðe veliki strah u sve koji slušahu ovo.
Da Ananiyas ya ji wannan, sai ya fāɗi ya mutu. Sai babban tsoro kuwa ya kama duk waɗanda suka ji abin da ya faru.
6 A momci ušavši uzeše ga i iznesoše te zakopaše.
Sai samari suka zo gaba, suka naɗe gawarsa, suka fitar da shi suka je suka binne.
7 A kad proðe oko tri sahata, uðe i žena njegova ne znajuæi šta je bilo.
Bayan kusan awa uku, sai matarsa ta shigo, ba da sanin abin da ya faru ba.
8 A Petar joj odgovori: kaži mi jeste li za toliko dali njivu? A ona reèe: da, za toliko.
Bitrus ya tambaye ta ya ce, “Gaya mini, kuɗin da yake da Ananiyas kuka sayar da filin ke nan?” Ta ce, “I, haka ne muka sayar.”
9 A Petar joj reèe: zašto se dogovoriste da iskušate Duha Gospodnjega? Gle, noge onijeh koji tvoga muža zakopaše pred vratima su, i iznijeæe te.
Bitrus ya ce mata, “Ta yaya kuka yarda ku gwada Ruhun Ubangiji? Duba! Sawun mutanen da suka binne mijinki suna bakin ƙofa, za su kuwa ɗauke ki zuwa waje ke ma.”
10 I odmah padnu pred nogama njegovijem i izdahnu. A momci ušavši naðoše je mrtvu i iznesoše je i zakopaše kod muža njezina.
Nan take ta fāɗi a ƙafafunsa ta mutu. Sai samarin suka shigo ciki, suka kuwa same ta matacciya, suka ɗauke ta suka kai ta waje suka binne ta kusa da mijinta.
11 I uðe veliki strah u svu crkvu i u sve koji èuše ovo.
Babban tsoro ya kama dukan ikkilisiya da kuma duk wanda ya ji game da abubuwan nan.
12 A rukama apostolskima uèiniše se mnogi znaci i èudesa meðu ljudima; i bijahu svi jednodušno u trijemu Solomunovu.
Manzannin suka yi ayyukan da alamu masu banmamaki masu yawa a cikin mutanen. Dukan masu bi kuwa sukan taru a Shirayin Solomon.
13 A od ostalijeh niko ne smijaše pristupiti k njima; nego ih hvaljaše narod.
Ba wanda ya yi karambanin shiga cikinsu, duk da haka mutane suna girmama su ƙwarai.
14 A sve više pristajahu oni koji vjerovahu Gospoda, mnoštvo ljudi i žena,
Duk da haka, maza da matan da suke gaskata ga Ubangiji sai ƙaruwa suke, suka kuma ƙaru a yawa.
15 Tako da i po ulicama iznošahu bolesnike i metahu na posteljama i na nosilima, da bi kad proðe Petar barem sjenka njegova osjenila koga od njih.
A sakamakon haka, mutane suka kawo marasa lafiya a tituna suka kwantar da su a kan gadaje da tabarmai domin aƙalla inuwar Bitrus za tă bi kan waɗansunsu yayinda yake wucewa.
16 A dolažahu mnogi i iz okolnijeh gradova u Jerusalim, i donošahu bolesnike i koje muèahu neèisti duhovi; i svi ozdravljahu.
Jama’a ma suka tattaru daga garuruwa kewaye da Urushalima suna kawo marasa lafiyarsu da kuma waɗanda mugayen ruhohi suke damun su, dukansu kuwa suka warke.
17 Ali ustade poglavar sveštenièki i svi koji bijahu s njim, od jeresi sadukejske, i napuniše se zavisti,
Sai babban firist da dukan abokan aikinsa, waɗanda suke na ƙungiyar Sadukiyawa suka cika da kishi.
18 I digoše ruke svoje na apostole, i metnuše ih u opšti zatvor.
Suka kama manzannin suka sa su a kurkukun da ake sa kowa da kowa.
19 A anðeo Gospodnji otvori noæu vrata tamnièka, i izvedavši ih reèe:
Amma da dare wani mala’ikan Ubangiji ya buɗe ƙofofin kurkukun ya fitar da su.
20 Idite i stanite u crkvi te govorite narodu sve rijeèi ovoga života.
Ya ce, “Ku je ku tsaya a filin haikali ku sanar wa mutane cikakken saƙon wannan sabon rai.”
21 A kad oni èuše, uðoše ujutru u crkvu, i uèahu. A kad doðe poglavar sveštenièki i koji bijahu s njim, sazvaše sabor i sve starješine od sinova Izrailjevijeh, i poslaše u tamnicu da ih dovedu.
Da gari ya waye, sai suka shiga filin haikali, yadda aka faɗa musu, suka kuwa fara koyar da mutane. Sa’ad da babban firist da abokan aikinsa suka iso, sai suka kira Majalisa gaba ɗaya dukan dattawan Isra’ila, suka kuma aika kurkuku a zo da manzannin.
22 A kad sluge otidoše, ne naðoše ih u tamnici; onda se vratiše i javiše im
Amma da dogarawan suka iso kurkukun, ba su same su a can ba. Saboda haka suka dawo suka ba da labari, suka ce,
23 Govoreæi: tamnicu naðosmo zakljuèanu sa svakom tvrðom i èuvare gdje stoje pred vratima; ali kad otvorismo, unutra nijednoga ne naðosmo.
“Mun iske kurkukun a kulle sosai, da masu gadi suna tsaye a bakin ƙofofin; amma da muka buɗe su, sai muka tarar ba kowa a ciki.”
24 A kad èuše ove rijeèi poglavar sveštenièki i vojvoda crkveni i ostali glavari sveštenièki, ne mogahu im se naèuditi šta bi to sad bilo.
Da jin wannan labari, sai shugaban masu gadin haikali da manyan firistocin suka ruɗe, suna tunanin abin da wannan al’amari zai zama.
25 A neko doðe i javi im govoreæi: eno oni ljudi što ih baciste u tamnicu, stoje u crkvi i uèe narod.
Sai wani ya zo ya ce, “Ga shi! Mutanen da kuka sa a kurkuku suna tsaye a filin haikali suna koya wa mutane.”
26 Tada otide vojvoda s momcima i dovede ih ne na silu: jer se bojahu naroda da ih ne pobije kamenjem.
Da wannan, shugaban ya tafi tare da dogarawansa suka kawo manzannin. Sun kawo su amma fa ba ƙarfi da yaji ba, don suna tsoro kada mutane su jajjefe su da duwatsu.
27 A kad ih dovedoše, postaviše ih pred sabor, i zapita ih poglavar sveštenièki govoreæi:
Da suka kawo manzannin, sai suka sa su suka bayyana a gaban Majalisar don babban firist ya tuhume su.
28 Ne zaprijetismo li vam oštro da ne uèite u ovo ime? i gle, napuniste Jerusalim svojom naukom, i hoæete da bacite na nas krv ovoga èovjeka.
Ya ce, “Mun kwaɓe ku da gaske kada ku ƙara koyarwa cikin wannan suna, duk da haka kun cika Urushalima da koyarwarku, har ma kuna so ku ɗora mana laifin jinin mutumin nan.”
29 A Petar i apostoli odgovarajuæi rekoše: veæma se treba Bogu pokoravati negoli ljudima.
Bitrus da sauran manzannin suka amsa suka ce, “Dole ne mu yi wa Allah biyayya a maimakon mutane!
30 Bog otaca našijeh podiže Isusa, kojega vi ubiste objesivši na drvo.
Allahn kakanninmu ya tā da Yesu daga matattu, wanda kuka kashe ta wurin ratayewa a bisan itace.
31 Ovoga Bog desnicom svojom uzvisi za poglavara i spasa, da da Izrailju pokajanje i oproštenje grijeha.
Allah ya ɗaukaka shi zuwa hannun damansa a matsayin Yerima da Mai Ceto don yă kawo tuba da gafarar zunubai ga Isra’ila.
32 I mi smo njegovi svjedoci ovijeh rijeèi i Duh sveti kojega Bog dade onima koji se njemu pokoravaju.
Mu shaidu ne ga waɗannan abubuwa, haka kuma Ruhu Mai Tsarki, wanda Allah ya ba wa waɗanda suke yin masa biyayya.”
33 A kad oni èuše vrlo se rasrdiše, i mišljahu da ih pobiju.
Da suka ji haka, sai suka yi fushi suka so su kashe su.
34 Ali onda ustade u skupštini jedan farisej, po imenu Gamaliilo, zakonik, poštovan od svega naroda, i zapovjedi da apostoli malo iziðu napolje,
Amma wani Bafarisiyen da ake kira Gamaliyel, wani malamin doka, wanda dukan mutane ke girmamawa, ya miƙe tsaye a Majalisar ya umarta a fitar da mutanen waje na ɗan lokaci.
35 Pa reèe njima: ljudi Izrailjci! gledajte dobro za ove ljude šta æete èiniti;
Sa’an nan ya yi musu jawabi ya ce, “Mutanen Isra’ila, ku yi kula da kyau da abin da kuke niyyar yi wa mutanen nan.
36 Jer prije ovijeh dana usta Tevda, govoreæi da je on nešto, za kojijem pristade ljudi na broj oko èetiri stotine; on bi ubijen, i svi koji ga slušahu raziðoše se i propadoše.
Kwanan baya, Teyudas ya ɓullo, yana cewa wai shi wani mutum ne, kuma wajen mutane ɗari huɗu suka bi shi. Aka kuwa kashe shi, dukan masu binsa kuwa suka watse, kome ya wargaje.
37 Potom usta Juda Galilejac, u dane prijepisa, i odvuèe dosta ljudi za sobom; i on pogibe, i svi koji ga slušahu razasuše se.
Bayansa, Yahuda mutumin Galili ya ɓullo a kwanakin ƙidaya, ya jagoranci mutane cikin tawaye. Shi ma aka kashe shi, dukan mabiyansa kuma aka watsar da su.
38 I sad vam kažem: proðite se ovijeh ljudi i ostavite ih; jer ako bude od ljudi ovaj savjet ili ovo djelo, pokvariæe se.
Saboda haka, a wannan batu na yanzu, ina ba ku shawara. Ku ƙyale mutanen nan! Ku bar su su tafi! Gama in manufarsu ko ayyukansu na mutum ne, ai, zai rushe.
39 Ako li je od Boga, ne možete ga pokvariti, da se kako ne naðete kao bogoborci.
Amma in daga Allah ne, ba za ku iya hana waɗannan mutane ba, za ku dai sami kanku kuna gāba da Allah ne.”
40 Onda ga poslušaše, i dozvavši apostole izbiše ih, i zaprijetiše im da ne govore u ime Isusovo, i otpustiše ih.
Jawabinsa ya rinjaye su. Suka kira manzannin suka sa aka yi musu bulala. Sa’an nan suka kwaɓe su kada su ƙara magana a cikin sunan Yesu, suka kuma bar su suka tafi.
41 A oni onda otidoše od sabora radujuæi se što se udostojiše primiti sramotu za ime Gospoda Isusa.
Manzannin suka bar Majalisar, suna farin ciki domin an ga sun cancanta a kunyata su saboda Sunan nan.
42 A svaki dan u crkvi i po kuæama ne prestajahu uèiti i propovijedati jevanðelje o Isusu Hristu.
Kowace rana, a filin haikali da kuma gida-gida, ba su fasa koyarwa da kuma shelar labari mai daɗi cewa Yesu shi ne Kiristi ba.