< 2 Dnevnika 12 >

1 A kad Rovoam utvrdi carstvo i kad osili, ostavi zakon Gospodnji i sav Izrailj s njim.
Bayan mulkin Rehobowam ya kahu kamar sarki ya kuma yi ƙarfi, shi da dukan Isra’ila suka yi biris da dokar Ubangiji.
2 A pete godine carovanja Rovoamova doðe Sisak car Misirski na Jerusalim, jer zgriješiše Gospodu,
Domin sun yi rashin biyayya ga Ubangiji, saboda haka Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima a shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam.
3 S tisuæu i dvije stotine kola i sa šezdeset tisuæa konjika, i ne bješe broja narodu koji doðe s njim iz Misira, Luvejima, Suhejima i Husejima.
Da kekunan yaƙi dubu ɗaya da ɗari biyu da kuma mahayan dawakai dubu haɗe da mayaƙan Libiyawa, Sukkatawa da kuma Kushawa waɗanda suka wuce ƙidaya suka zo tare da shi daga Masar,
4 I uze tvrde gradove Judine i doðe do Jerusalima.
ya ci biranen katanga na Yahuda har zuwa Urushalima.
5 Tada doðe Semaja prorok k Rovoamu i knezovima Judinijem, koji se bijahu skupili u Jerusalim od Sisaka, i reèe im: ovako veli Gospod: vi ostaviste mene, zato i ja ostavljam vas u ruke Sisaku.
Sai annabi Shemahiya ya zo wurin Rehobowam da kuma wajen shugabannin Yahuda waɗanda suka taru a Urushalima don tsoron Shishak, ya kuma faɗa musu, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Kun yi biris da ni; saboda haka, yanzu na bashe ku ga Shishak.’”
6 Tada se poniziše knezovi Izrailjevi i car i rekoše: pravedan je Gospod.
Shugabannin Isra’ila da sarki suka ƙasƙantar da kansu suka ce, “Ubangiji mai adalci ne.”
7 A kad ih vidje Gospod gdje se poniziše, doðe rijeè Gospodnja Semaji govoreæi: poniziše se, neæu ih potrti, nego æu im sada dati izbavljenje, i neæe se izliti jarost moja na Jerusalim preko Sisaka.
Sa’ad da Ubangiji ya ga sun ƙasƙantar da kansu, sai wannan maganar Ubangiji ta zo wa Shemahiya, “Tun da yake sun ƙasƙantar da kansu, to, ba zan hallaka su ba, amma zan cece su, ba zan kwararo fushina ta hannun Shishak a kan Urushalima ba.
8 Nego æe mu biti sluge da poznadu šta je meni služiti, šta li služiti carstvima zemaljskim.
Duk da haka za su zama bayinsa, don su san bambanci tsakanin yin mini bauta da kuma yin wa sarakunan sauran ƙasashe bauta.”
9 I tako doðe Sisak car Misirski u Jerusalim i uze blago doma Gospodnjega i blago doma careva, sve to uze; uze i štitove zlatne, koje bješe naèinio Solomun;
Da Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima, sai ya kwashi ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan sarki. Ya kwashe kome da kome, har da garkuwoyin zinariyar da Solomon ya yi.
10 I na njihovo mjesto naèini car Rovoam štitove od mjedi, i predade ih starješinama nad stražarima koji èuvahu vrata doma careva.
Sai sarki Rehobowam ya ƙera garkuwoyin tagulla a madadin na zinariya, ya sa su a hannun shugabannin matsara na mashigin gidan sarki.
11 I kad iðaše car u dom Gospodnji dolažahu stražari i nošahu ih, a poslije ih opet ostavljahu u riznicu stražarsku.
Duk sa’ad da sarki ya tafi haikalin Ubangiji, masu tsaron sukan tafi tare da shi, suna riƙe da garkuwoyi, daga baya kuma su mai da su a ɗakin tsaro.
12 Što se dakle ponizi, odvrati se od njega gnjev Gospodnji, i ne zatr ga sasvijem; jer još u Judi bješe dobra.
Gama Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, fushin Ubangiji ya bar shi, ba a kuwa hallaka shi ƙaƙaf ba. Tabbatacce an yi’yan abubuwa masu kyau a Yahuda.
13 I utvrdi se car Rovoam u Jerusalimu, i carova; jer bijaše Rovoamu èetrdeset i jedna godina kad se zacari, i sedamnaest godina carova u Jerusalimu gradu, koji izabra Gospod izmeðu svijeh plemena Izrailjevijeh da ondje namjesti ime svoje. A materi njegovoj bješe ime Nama, Amonka.
Sarki Rehobowam ya kafa kansa daram a Urushalima, ya kuma ci gaba a matsayin sarki. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila wanda zai sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama ce, ita mutuniyar Ammon ce.
14 Ali on èinjaše zlo, jer ne upravi srca svojega da traži Gospoda.
Ya aikata mugunta domin bai sa zuciyarsa ga neman Ubangiji ba.
15 Ali djela Rovoamova prva i pošljednja nijesu li zapisana u knjizi proroka Semaje i vidioca Ida, gdje se kazuju koljena a i ratovi koji bijahu jednako meðu Rovoamom i Jerovoamom?
Game da ayyukan mulkin Rehobowam, daga farko zuwa ƙarshe, ba a rubuce suke a tarihin Shemahiya annabi da Iddo mai gani wanda yake zancen zuriyoyi ba? Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
16 I poèinu Rovoam kod otaca svojih, i bi pogreben u gradu Davidovu; a na njegovo se mjesto zacari Avija sin njegov.
Rehobowam ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Abiya ɗansa kuma ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Dnevnika 12 >