< 1 Samuelova 17 >
1 Tada Filisteji skupiše vojsku svoju da vojuju, i skupiše se u Sokotu Judinu, i stadoše u oko izmeðu Sokota i Azike na meði Damimskoj.
To, fa, Filistiyawa suka tattara mayaƙansu suka haɗu a Soko cikin Yahuda domin yaƙi. Suka yi sansani a Efes-Dammim, tsakanin Soko da Azeka.
2 A Saul i Izrailjci skupiše se i stadoše u oko u dolini Ili, i uvrstaše se prema Filistejima.
Shawulu da Isra’ilawa suka taru suka yi sansani a Kwarin Ela suka ja dāgā don su yi yaƙi da Filistiyawa.
3 I Filisteji stajahu na brdu odonuda a Izrailjci stajahu na brdu odovuda, a meðu njima bješe dolina.
Filistiyawa suka zauna a tudu guda, Isra’ilawa kuma suka zauna a ɗaya tudun. Kwari yana a tsakaninsu.
4 I izide iz okola Filistejskoga jedan zatoènik po imenu Golijat iz Gata, visok šest lakata i ped.
Wani jarumin da ake kira Goliyat wanda ya fito daga Gat, ya fita daga sansanin Filistiyawa. Tsawonsa ya fi ƙafa tara.
5 I na glavi mu bješe kapa od mjedi, i oklop ploèast na njemu od mjedi; i bijaše oklop težak pet tisuæa sikala.
Ya sa hular kwanon da aka yi da tagulla, da rigar ƙarfe mai sulke, nauyin rigar ya kai shekel dubu biyar.
6 I nogavice od mjedi bjehu mu na nogu, i štit od mjedi na ramenima.
A ƙafafunsa kuwa ya sa ƙarafar tagulla, rataye a bayansa kuma māshi ne na tagulla.
7 A kopljaèa od koplja mu bješe kao vratilo, a gvožða u koplju mu bješe šest stotina sikala; i koji mu oružje nošaše iðaše pred njim.
Ƙotar kibiyarsa kuwa kamar sandar saƙar igiya take, ƙarfen kibiyar kuma nauyinsa ya kai shekel ɗari shida. Mai riƙe masa garkuwa yana tafe a gabansa.
8 On stavši vikaše vojsku Izrailjsku, i govoraše im: što ste izašli uvrstavši se? nijesam li ja Filistejin a vi sluge Saulove? izberite jednoga izmeðu sebe, pa neka izaðe k meni.
Goliyat ya tsaya ya tā da murya wa hafsoshin Isra’ila ya ce, “Me ya sa kuka fito kuna layi don yaƙi? Ni ba Bafilistin ba ne? Ku kuma ba bayin Shawulu ba ne? Ku zaɓi waninku yă zo nan.
9 Ako me nadjaèa i pogubi me, mi æemo vam biti sluge; ako li ja njega nadjaèam i pogubim ga, onda æete vi biti nama sluge, i služiæete nam.
In zai iya yin faɗa har yă kashe ni, to, za mu zama bayinku. Amma in na fi ƙarfinsa na kashe shi, to, sai ku zama bayinmu, ku kuma yi mana bauta.”
10 Još govoraše Filistejin: ja osramotih danas vojsku Izrailjsku; dajte mi èovjeka da se bijemo.
Sai Bafilistin ya ce, “A wannan rana, na kalubalanci sojojin Isra’ila, ku ba ni mutum ɗaya mu yi faɗa.”
11 A kad Saul i sav Izrailj èu šta reèe Filistejin, prepadoše se i uplašiše se vrlo.
Da jin maganganun Bafilistin, sai Shawulu da dukan Isra’ila suka damu suka kuma ji tsoro.
12 A bijaše David sin jednoga Efraæanina, iz Vitlejema Judina, kojemu ime bješe Jesej, koji imaše osam sinova i bijaše u vrijeme Saulovo star i vremenit meðu ljudima.
To, Dawuda dai ɗan wani mutumin Efratawa ne mai suna Yesse, shi mutumin Betlehem ne a cikin Yahudiya. Yesse yana da yara maza takwas, a zamanin Shawulu kuwa, Yesse ya riga ya tsufa.
13 I tri najstarija sina Jesejeva otidoše za Saulom na vojsku; a imena trojici sinova njegovijeh koji otidoše na vojsku bijahu prvencu Elijav a drugome Avinadav a treæemu Sama.
Manyan’ya’yansa maza uku, sun bi Shawulu wajen yaƙi. Ɗansa na fari shi ne Eliyab, na biyu shi ne Abinadab, na uku kuwa shi ne Shamma.
14 A David bijaše najmlaði. I ona tri najstarija otidoše za Saulom.
Dawuda shi ne ɗan autansu. Manyan’yan mazan nan uku suka bi Shawulu.
15 A David otide od Saula i vrati se u Vitlejem da pase ovce oca svojega.
Amma Dawuda yakan tafi sansanin Shawulu lokaci-lokaci yă kuma koma Betlehem don yă yi kiwon tumakin mahaifinsa.
16 A Filistejin izlažaše jutrom i veèerom, i staja èetrdeset dana.
Kwana arba’in cif, Bafilistin nan ya yi ta fitowa kowane safe da kuma kowace yamma.
17 A Jesej reèe Davidu sinu svojemu: uzmi sada za braæu svoju efu ovoga prženoga žita i ovijeh deset hljebova, i odnesi brže u oko braæi svojoj.
Yesse ya ce wa ɗansa Dawuda, “Ka ɗauki wannan gasasshen hatsi da waɗannan curin burodi goma, ka kai wa’yan’uwanka a sansani da sauri.
18 A ovijeh deset mladijeh siraca odnesi tisuæniku, i vidi braæu svoju kako su, i donesi od njih znak.
Ka haɗa da waɗannan cuku guda goma, ka kai wa komandan rundunarsu. Ka ga lafiyar’yan’uwanka, ka kawo mini labari daga wurinsu.
19 A Saul i oni i sav Izrailj bijahu u dolini Ili ratujuæi s Filistejima.
Suna tare da Shawulu da kuma dukan mutanen Isra’ila a Kwarin Ela, suna can suna yaƙi da Filistiyawa.”
20 I tako David usta rano i ostavi ovce na èuvaru; pa uze i otide kako mu zapovjedi Jesej; i doðe na mjesto gdje bješe oko, i vojska izlažaše da se vrsta za boj, i podizaše ubojnu viku.
Kashegari da sassafe, Dawuda ya tashi ya bar tumakinsa wa wani yă lura da su, sai ya ɗauki kayansa, ya kama hanya kamar yadda Yesse ya umarce shi. Ya isa sansanin daidai sa’ad da rundunar tana fitowa zuwa bakin dāgā, suna kirarin yaƙi.
21 I stajaše vojska Izrailjska i Filistejska jedna prema drugoj.
Isra’ila da Filistiyawa suka ja dāgā suna fuskantar junansu.
22 Tada ostavi David svoj prtljag kod èuvara, koji èuvaše prtljag, i otrèa u vojsku, i doðe i zapita braæu svoju za zdravlje.
Dawuda ya bar kayansa a wajen wani mai lura da kaya, sai ya ruga zuwa bakin dāgā yă gai da’yan’uwansa.
23 I dokle govoraše s njima, gle, onaj zatoènik po imenu Golijat Filistejin iz Gata, izide iz vojske Filistejske i govoraše kao prije, i David èu.
Da yana magana da su sai Goliyat, jarumin nan Bafilistin daga Gat ya fito daga rundunar Filistiyawa, ya tā da murya kamar yadda ya saba. Dawuda kuwa ya ji shi.
24 A svi Izrailjci kad vidješe toga èovjeka, uzbjegoše od njega, i bješe ih strah veoma.
Da Isra’ilawa suka ga mutumin, sai dukansu suka gudu saboda tsananin tsoro.
25 I govorahu Izrailjci: vidjeste li toga èovjeka što izide? Jer izide da sramoti Izrailja. A ko bi ga pogubio, car bi mu dao silno blago, i kæer svoju dao bi mu; i oslobodio bi dom oca njegova u Izrailju.
Isra’ilawa suka yi ta cewa, “Kun ga yadda wannan mutum yana ta fitowa? Yana fitowa ne don yă kalubalanci Isra’ila. Sarki zai sāka wa mutumin da ya kashe wannan da dukiya mai yawa. Zai kuma ba shi’yarsa yă aura, yă cire suna mahaifinsa daga biyan kuɗin haraji cikin Isra’ila.”
26 Tada reèe David ljudima koji stajahu oko njega govoreæi: šta æe se uèiniti èovjeku koji pogubi toga Filistejina i skine sramotu s Izrailja? Jer ko je taj Filistejin neobrezani da sramoti vojsku Boga živoga?
Dawuda ya tambayi mutanen da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Me za a yi wa wanda ya kashe Bafilistin nan, ya kuma cire wannan kunya daga Isra’ila? Wane ne wannan bafilistin marar kaciya da yake kalubalantar rundunar yaƙi na Allah mai rai?”
27 A narod mu odgovori iste rijeèi govoreæi: to æe se uèiniti onome ko ga pogubi.
Sai suka sāke gaya masa abin da suka faɗa cewa, “Ga abin da zai faru da wanda ya kashe shi.”
28 A kad èu Elijav brat njegov najstariji kako se razgovara s tijem ljudima, razljuti se Elijav na Davida, i reèe mu: što si došao? i na kom si ostavio ono malo ovaca u pustinji? znam ja obijest tvoju i zloæu srca tvojega; došao si da vidiš boj.
Da wansa Eliyab, ya ji yana magana da mutanen, sai ransa ya ɓace ƙwarai saboda fushi, sai ya ce wa Dawuda, “Me ka zo yi a nan? Wa kuma ka bar wa’yan tumakin a jeji? Na san ka da taurinkai, da kuma mugun hali. Ka zo nan ne don ka yi kallon yaƙi kawai.”
29 A David reèe: šta sam sad uèinio? zapovjeðeno mi je.
Dawuda ya ce, “To, yanzu me na yi? Ba zan ma yi magana ba?”
30 Potom okrenu se od njega k drugome i zapita kao prije; i narod mu odgovori kao prije.
Sai ya juya wajen wani kuma ya sāke kawo zancen, mutanen kuwa suka amsa masa kamar dā.
31 I kad se èuše rijeèi koje govoraše David, javiše ih Saulu, a on ga dozva k sebi.
Aka ji abin da Dawuda ya ce, aka kuwa gaya wa Shawulu, Shawulu kuma ya aika a kawo shi.
32 I David reèe Saulu: neka se niko ne plaši od onoga; sluga æe tvoj izaæi i biæe se s Filistejinom.
Da Shawulu ya tambayi Dawuda, sai Dawuda ya ce masa, “Kada kowa yă damu saboda wannan Bafilistin. Bawanka zai je yă yi faɗa da shi.”
33 A Saul reèe Davidu: ne možeš ti iæi na Filistejina da se biješ s njim, jer si ti dijete a on je vojnik od mladosti svoje.
Shawulu ya ce, “Ba za ka iya yin faɗa da wannan Bafilistin ba, ya daɗe yana yaƙi, ya yi yaƙi tun yana saurayi. Ga shi kuwa kai ɗan yaro ne kawai.”
34 A David reèe Saulu: sluga je tvoj pasao ovce oca svojega; pa kad doðe lav ili medvjed i odnese ovcu iz stada,
Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Bawanka yana kiwon tumakin mahaifinsa. Sa’ad da zaki ko beyar ta zo ta kama tunkiya, ta tafi da ita.
35 Ja potrèah za njim, i udarih ga i oteh mu iz èeljusti; i kad bi skoèio na me, uhvatih ga za grlo, te ga bih i ubih.
Nakan bi ta a baya in buga ta in kuma ƙwato tunkiyar daga bakinta. In kuma ta taso mini, nakan cafke ta a gashinta in buga ta in kashe.
36 I lava i medvjeda ubijao je tvoj sluga, pa æe i taj Filistejin neobrezani proæi kao oni; jer osramoti vojsku Boga živoga.
Bawanka ya kashe zaki da beyar, wannan Bafilistin marar kaciya zai zama kamar ɗaya daga cikinsu, domin ya rena rundunar Allah mai rai.
37 Još reèe David: Gospod koji me je saèuvao od lava i medvjeda, on æe me saèuvati i od ovoga Filistejina. Tada reèe Saul Davidu: idi, i Gospod neka bude s tobom.
Ubangiji wanda ya cece ni daga kumbar zaki da kuma kumbar beyar, zai cece ni daga hannun wannan Bafilistin.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Je ka, Ubangiji yă kasance tare da kai.”
38 I Saul dade Davidu svoje oružje, i metnu mu na glavu kapu svoju od mjedi i metnu oklop na nj.
Sai Shawulu ya kawo kayan yaƙinsa ya sa wa Dawuda. Ya sa masa hular kwanon da aka yi da tagulla a kansa, ya kuma sa masa rigar ƙarfensa.
39 I pripasa David maè njegov preko svojega odijela i poðe, ali ne bješe navikao, pa reèe David Saulu: ne mogu iæi s tijem, jer nijesam navikao. Pa skide David sa sebe.
Dawuda ya ɗaura māshin Shawulu a sulken, ya yi ƙoƙari yă zaga, sai ya ji ba zai iya ba saboda bai saba ba. Ya cewa Shawulu, “Ba zan iya tafiya da waɗannan ba, domin ban saba ba.” Don haka ya tuɓe su.
40 I uze štap svoj u ruku, i izabra na potoku pet glatkih kamena i metnu ih u torbu pastirsku, koju imaše, i uze praæu svoju u ruku, i tako poðe ka Filistejinu.
Sai ya ɗauki sandansa, ya zaɓi duwatsu guda biyar masu sulɓi daga cikin rafi, ya sa su a’yar jakarsa ta makiyaya; ya kuma ɗauki majajjawarsa, ya tafi, yă fuskanci Bafilistin.
41 A i Filistejin iðaše sve bliže k Davidu, a èovjek koji mu nošaše oružje, iðaše pred njim.
Ana ciki haka, sai Bafilistin nan shi ma ya fita yana gusowa zuwa wurin Dawuda. Mai riƙe masa garkuwar yaƙi kuwa yana tafe a gabansa.
42 A kad Filistejin pogleda i vidje Davida, potsmjehnu mu se, što bješe mlad i smeð i lijepa lica.
Bafilistin ya dubi Dawuda daga sama har ƙasa, ya gan dai ɗan yaro ne kawai, kyakkyawa kuma mai ƙoshin lafiya, sai ya rena shi.
43 I reèe Filistejin Davidu: eda li sam pseto, te ideš na me sa štapom? I proklinjaše Filistejin Davida bogovima svojim.
Ya ce masa, “Kana tsammani ni kare ne da za ka zo mini da sanda?” Sai ya la’anci Dawuda da sunayen allolin Filistiyawa.
44 I reèe Filistejin Davidu: hodi k meni da dam tijelo tvoje pticama nebeskim i zvijerima zemaljskim.
Ya ce, “Zo nan, ni kuwa zan ba da naman jikinka ga tsuntsayen sama da namun jeji su ci.”
45 A David reèe Filistejinu: ti ideš na me s maèem i s kopljem i sa štitom; a ja idem na te u ime Gospoda nad vojskama, Boga vojske Izrailjeve, kojega si ružio.
Dawuda ya ce wa Bafilistin, “Kana zuwa ka yaƙe ni da māshi da takobi da kere, amma ni ina zuwa in yaƙe ka a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki, Allah na rundunar Isra’ila, wanda ka rena.
46 Danas æe te Gospod dati meni u ruke, i ubiæu te, i skinuæu glavu s tebe, i daæu danas tjelesa vojske Filistejske pticama nebeskim i zvijerima zemaljskim, i poznaæe sva zemlja da je Bog u Izrailju.
Yau nan, Ubangiji zai bashe ka a hannuna, zan kuwa kashe ka, in datse kanka. Yau, zan ba da gawawwakin rundunar Filistiyawa ga tsuntsayen sama da namun jeji, da haka duniya za tă sani lalle akwai Allah a cikin Isra’ila.
47 I znaæe sav ovaj zbor da Gospod ne spasava maèem ni kopljem, jer je rat Gospodnji, zato æe vas dati nama u ruke.
Duk waɗanda suka taru a nan za su san cewa ba da māshi ko takobi ne Ubangiji yake ceto ba, gama yaƙin nan na Ubangiji ne, shi kuwa zai bashe ku duka a hannuwanmu.”
48 A kad se Filistejin podiže i doðe bliže k Davidu, David brže istrèa na bojište pred Filistejina.
Yayinda Bafilistin yana matsowa kusa domin yă fāɗa wa Dawuda, sai Dawuda ya ruga a guje zuwa bakin dāgā don yă same shi.
49 I David turi ruku svoju u torbu svoju, i izvadi iz nje kamen, i baci ga iz praæe, i pogodi Filistejina u èelo i uðe mu kamen u èelo, te pade nièice na zemlju.
Ya sa hannu a jakarsa ya ɗauki dutse, ya sa cikin majajjawa ya wurga, dutsen kuwa ya bugi Bafilistin a goshi, dutsen ya shiga cikin goshinsa, sai Bafilistin ya fāɗi rubda ciki.
50 Tako David praæom i kamenom nadjaèa Filistejina, i udari Filistejina i ubi ga; a nemaše David maèa u ruci.
Da majajjawa da dutse kawai Dawuda ya ci nasara a kan Bafilistin. Ya buge shi, ya kashe shi ba tare da takobi a hannunsa ba.
51 I pritrèav David stade na Filistejina, i zgrabi maè njegov i izvuèe ga iz korica i pogubi ga i otsijeèe mu glavu. A Filisteji kad vidješe gdje pogibe junak njihov pobjegoše.
Dawuda ya ruga ya tsaya a bisan Bafilistin, ya zare takobin Bafilistin daga kubensa, ya datse masa kai da shi. Da Filistiyawa suka ga jaruminsu ya mutu, sai suka juya suka gudu.
52 A Izrailjci i Judejci ustaše i povikaše i potjeraše Filisteje do doline i do vrata Akaronskih; i padaše pobijeni Filisteji po putu Sarajimskom do Gata i do Akarona.
Mutanen Isra’ila da na Yahuda suka rugo gaba da babbar murya, suka fafari Filistiyawa har zuwa mashigin Gat da kuma ƙofofin Ekron. Gawawwakin Filistiyawa suka bazu a hanyar Sha’arayim zuwa Gat da kuma Ekron.
53 Potom se vratiše sinovi Izrailjevi tjeravši Filisteje, i oplijeniše oko njihov.
Da Isra’ilawa suka komo daga bin Filistiyawa sai suka washe sansanin Filistiyawa.
54 A David uze glavu Filistejinovu, i odnese je u Jerusalim, a oružje njegovo ostavi u svojoj kolibi.
Dawuda ya ɗauki kan Bafilistin zuwa Urushalima. Sai Dawuda ya ajiye kayan yaƙin Bafilistin a tentinsa.
55 A kad Saul vidje Davida gdje ide pred Filistejina, reèe Aveniru vojvodi: èiji je sin taj mladiæ, Avenire? A Avenir reèe: kako je živa duša tvoja, care, ne znam.
Yayinda Shawulu yake kallon Dawuda sa’ad da za shi yă yaƙi Bafilistin, sai ya tambayi Abner, komandan rundunarsa ya ce, “Abner, ɗan wane ne wannan saurayi?” Abner ya ce ran sarki yă daɗe, “Ban sani ba.”
56 A car reèe: pitaj èiji je sin taj mladiæ.
Sarki ya ce, “Ka tambaya mini ko yaron wane ne wannan saurayi.”
57 A kad se vrati David pogubivši Filistejina, uze ga Avenir i izvede ga pred Saula, a u ruci mu bješe glava Filistejinova.
Dawuda yana dawowa daga karkashe Filistiyawa ke nan, sai Abner ya kai shi gaban Shawulu, riƙe da kan Bafilistin.
58 I Saul reèe mu: èiji si sin, dijete? A David reèe: ja sam sin sluge tvojega Jeseja Vitlejemca.
Sai Shawulu ya ce, “Kai ɗan wane ne, saurayi?” Dawuda ya ce, “Ni ɗan bawanka Yesse ne, na Betlehem.”