< 1 Kraljevima 9 >
1 A kad Solomun svrši dom Gospodnji i dom carski i sve što željaše Solomun i rad bijaše naèiniti,
Sa’ad da Solomon ya gama ginin haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki, ya kuma yi dukan abin da yake so yă yi,
2 Javi se Gospod Solomunu drugi put, kao što mu se bješe javio u Gavaonu;
sai Ubangiji ya bayyana gare shi sau na biyu, kamar yadda ya bayyana masa a Gibeyon.
3 I reèe mu Gospod: uslišio sam molbu tvoju i molitvu tvoju, kojom si mi se molio; posvetio sam taj dom koji si sazidao da tu namjestim ime svoje dovijeka; i oèi æe moje i srce moje biti ondje vazda.
Ubangiji ya ce masa, “Na ji addu’arka da kuma roƙon da ka yi a gabana; na tsarkake wannan haikali wanda ka gina, ta wurinsa Sunana zai kasance a can har abada. Idanuna da zuciyata kullum za su kasance a can.
4 A ti ako uzideš preda mnom kako je išao David otac tvoj s cijelijem i pravijem srcem tvoreæi sve što sam ti zapovjedio i držeæi uredbe moje i zakone moje,
“Kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana da mutunci a zuci da kuma gaskiya, kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka yi dukan abin da na umarta, ka kuma yi biyayya da ƙa’idodina da kuma dokokina,
5 Utvrdiæu prijesto carstva tvojega nad Izrailjem navijek, kao što sam kazao Davidu ocu tvojemu govoreæi: neæe ti nestati èovjeka na prijestolu Izrailjevu.
zan kafa kujerar sarautarka a bisa Isra’ila har abada, kamar yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani a kan kujerar sarautar Isra’ila ba.’
6 Ali ako se vi i sinovi vaši odvratite od mene i ne uzdržite zapovijesti mojih i uredaba mojih koje sam vam dao, i otidete i stanete služiti drugim bogovima i klanjati im se,
“Amma in kai, ko’ya’yanka maza, suka juye daga gare ni, ba ku kuma kiyaye umarnai da ƙa’idodin da na ba ku ba, kuka yi gaba, kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka kuma yi musu sujada,
7 Tada æu istrijebiti Izrailja sa zemlje, koju sam vam dao, i ovaj dom, koji sam posvetio imenu svojemu, odbaciæu od sebe, i Izrailj æe postati prièa i potsmijeh meðu svijem narodima;
sai in yanke mutanen Isra’ila daga ƙasar da na ba su, in kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Isra’ila kuwa za tă zama abin gori da abin dariya a cikin dukan mutane.
8 A dom ovaj koliko je slavan, ko god proðe mimo nj, zaèudiæe se i zapištaæe, i reæi æe: zašto uèini Gospod ovo od ove zemlje i od ovoga doma?
Wannan haikali zai zama tarin juji. Duk wanda ya wuce ta hanyan nan kuwa zai ji tausayi, yă kuma yi tsaki yana cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka ga wannan ƙasa da kuma wannan haikali?’
9 I odgovaraæe se: jer odustaše Gospoda Boga svojega, koji izvede oce njihove iz zemlje Misirske, i uzeše druge bogove, i klanjaše im se i služiše im; zato pusti na njih Gospod sve ovo zlo.
Mutane za su amsa su ce, ‘Saboda sun yashe Ubangiji Allahnsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna yin musu sujada, suna bauta musu ne, ya sa Ubangiji ya kawo dukan masifan nan a kansu.’”
10 A kad proðe dvadeset godina, u koje sazida Solomun ova dva doma, dom Gospodnji i dom carski,
A ƙarshen shekaru ashirin da Solomon ya ɗauka yana gina haikalin Ubangiji da fadan sarki,
11 A Hiram car Tirski dade Solomunu drva kedrovijeh i drva jelovijeh i zlata koliko mu god volja bješe, tada car Solomun dade Hiramu dvadeset gradova u zemlji Galilejskoj.
sai Sarki Solomon ya ba wa Hiram sarkin Taya garuruwa ashirin a yankin Galili, gama Hiram ya tanada masa da dukan katakai al’ul da na fir, da kuma zinariyar da ya bukaci domin aiki.
12 I doðe Hiram iz Tira da vidi gradove koje mu dade Solomun, ali ne biše mu po volji.
Amma sa’ad da Hiram ya zo daga Taya don yă ga garuruwan da Solomon ya ba shi, sai bai ji daɗi ba.
13 Pa reèe: kakvi su to gradovi što si mi ih dao, brate? I nazva ih: zemlja Kavul; i osta im to ime do danas.
Sai ya ce, “Wanda irin garuruwa ke nan ka ba ni, ɗan’uwana?” Saboda haka ya kira su Ƙasar Kabul, sunan da suke da shi har wa yau.
14 A Hiram bješe poslao caru sto i dvadeset talanata zlata.
Hiram kuwa ya aika wa sarki talenti 120 na zinariya.
15 I tako car Solomun odredi ljude, te sazida dom Gospodnji i dom svoj i Milon, i zidove oko Jerusalima, i Asor i Megidon i Gezer.
Ga lissafin ma’aikatan gandun da Sarki Solomon ya ɗauka don ginin haikalin Ubangiji, da fadarsa, da madogaran gini, da katangar Urushalima, da kuma Hazor Megiddo da Gezer.
16 Jer Faraon car Misirski izide i uze Gezer, i spali ga ognjem, i pobi Hananeje koji življahu u gradu, i dade ga u præiju kæeri svojoj, ženi Solomunovoj.
(Fir’auna sarkin Masar ya kai wa Gezer hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Ya sa mata wuta, ya kashe Kan’aniyawanta mazaunan wurin, ya kuma ba da ita a matsayin kyautar aure ga’yarsa, matar Solomon.
17 A Solomun sazida Gezer i Vet-Oron donji.
Solomon kuwa ya sāke gina Gezer.) Ya gina Bet-Horon ta Kwari,
18 I Valat i Tadmor u pustinji u zemlji,
da Ba’alat, da Tadmor a hamada, na cikin ƙasarsa.
19 I sve gradove u kojima Solomun imaše žitnice, i gradove u kojima mu bijahu kola, i gradove u kojima mu bijahu konjici, i što god Solomunu bi volja zidati u Jerusalimu i na Livanu i u svoj zemlji carstva svojega.
Haka kuma ya gina dukan biranen ajiyarsa, da garuruwa domin kekunan yaƙinsa, da garuruwa domin dawakansa. Ya gina duk abin da ya so yă ginawa a Urushalima, da Lebanon, da kuma ko’ina a dukan yankin da ya yi mulki.
20 I sav narod koji bješe ostao od Amoreja, Heteja, Ferezeja, Jeveja i Jevuseja, koji ne bijahu od sinova Izrailjevijeh,
Dukan Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa da Yebusiyawan da suka ragu a ƙasar (waɗanda ba Isra’ilawa ba ne),
21 Sinove njihove, koji bjehu ostali iza njih u zemlji, kojih ne mogoše sinovi Izrailjevi istrijebiti, njih Solomun nagna da plaæaju danak i robuju do današnjega dana.
wato, waɗanda suka ragu a ƙasar, waɗanda Isra’ilawa ba su iya hallakawa ba, su ne Solomon ya ɗauka su zama bayinsa don aikin gandu, kamar yadda yake har wa yau.
22 A od sinova Izrailjevijeh ne uèini nijednoga robom, nego bijahu vojnici i sluge njegove i knezovi, vojvode njegove, i zapovjednici nad kolima njegovijem i nad konjicima njegovijem.
Amma Solomon bai mai da Isra’ilawa bayi ba; su ne mayaƙansa, shugabannin gwamnatinsa, dogarawansa, shugabannin sojojinsa, da shugabanninsa na kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙinsa.
23 I bješe glavnijeh nastojnika nad poslom Solomunovijem pet stotina i pedeset, koji upravljahu narodom koji raðaše posao.
Su ne kuma manyan shugabanni masu lura da ayyukan Solomon, su ne shugabanni 550 masu lura da mutanen da suke aiki.
24 A kæi Faraonova preseli se iz grada Davidova u dom svoj, koji joj sazida. Tada sazida i Milon.
Bayan’yar Fir’auna ta haura daga Birnin Dawuda zuwa fadan da Solomon ya gina mata, sai ya gina madogaran gini.
25 I Solomun prinošaše tri puta na godinu žrtve paljenice i žrtve zahvalne na oltaru koji naèini Gospodu, i kaðaše na oltaru koji bješe pred Gospodom, kad svrši dom.
Sau uku a shekara Solomon kan miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama a kan bagaden da ya gina wa Ubangiji, yana ƙone turare a gaban Ubangiji haɗe da su, ta haka ya cika abin da ake bukata na haikali.
26 I laðe naèini car Solomun u Esion-Gaveru, koji je kod Elota na brijegu Crvenoga Mora u zemlji Edomskoj.
Sarki Solomon ya kuma gina jiragen ruwa a Eziyon Geber, wadda take kusa da Elot a Edom, a bakin Jan Teku.
27 I posla Hiram na tijem laðama sluge svoje, laðare vješte moru, sa slugama Solomunovijem;
Hiram kuwa ya aiki mutanensa, masu tuƙan jirgin ruwa waɗanda suka san teku, don su yi hidima a jerin jiragen ruwa tare da mutanen Solomon.
28 I doðoše u Ofir, i uzeše odande zlata èetiri stotine i dvadeset talanata, i donesoše caru Solomunu.
Suka tafi Ofir suka kuma dawo da talenti 420 na zinariya, wanda suka ba wa Sarki Solomon.