< 1 Korinæanima 7 >

1 A za ono što mi pisaste: dobro je èovjeku da se ne dohvata do žene:
To, game da zancen da kuka rubuto. Yana da kyau mutum yă zauna ba aure.
2 Ali zbog kurvarstva svaki da ima svoju ženu, i svaka žena da ima svojega muža;
Amma da yake fasikanci ya yi yawa, ya kamata kowane mutum yă kasance da matarsa, kowace mace kuma da mijinta.
3 Muž da èini ženi dužnu ljubav, tako i žena mužu.
Ya kamata miji yă cika hakkinsa na aure ga matarsa. Haka kuma matar ta yi ga mijinta.
4 Žena nije gospodar od svojega tijela, nego muž; tako i muž nije gospodar od svojega tijela, nego žena.
Jikin matar ba nata ne kaɗai ba, amma na mijinta ne ma. Haka ma jikin mijin, ba na shi ne kaɗai ba, amma na matarsa ne ma.
5 Ne zabranjujte se jedno od drugoga, veæ ako u dogovoru za vrijeme, da se postite i molite Bogu; i opet da se sastanete, da vas sotona ne iskuša vašijem neuzdržanjem.
Kada ku ƙi kwana da juna sai ko kun yarda a junanku kuma na ɗan lokaci, don ku himmantu ga addu’a. Sa’an nan ku sāke haɗuwa don kada Shaiɗan yă jarrabce ku saboda rashin ƙamewarku.
6 Ali ovo govorim po svjetu a ne po zapovijesti;
Wannan fa shawara ce nake ba ku, ba umarni ba.
7 Jer hoæu da svi ljudi budu kao i ja; ali svaki ima svoj dar od Boga: ovaj dakle ovako a onaj onako.
Da ma a ce dukan maza kamar ni suke mana. Sai dai kowa da irin baiwar da Allah ya yi masa; wani yana da wannan baiwa, wani kuwa wancan.
8 A neoženjenijem i udovicama velim: dobro im je ako ostanu kao i ja što sam.
To, ga marasa aure da gwauraye kuwa ina cewa yana da kyau su zauna haka ba aure, yadda nake.
9 Ako li se ne uzdrže, neka se žene i udaju; jer je bolje ženiti se negoli upaljivati se.
Sai dai in ba za su iya ƙame kansu ba, to, su yi aure, don yă fi kyau a yi aure, da sha’awa ta sha kan mutum.
10 A oženjenijem zapovijedam, ne ja nego Gospod, da se žena od muža ne razdvaja
Ga waɗanda suke da aure kuwa ina ba da wannan umarni (ba ni ba, amma Ubangiji) cewa kada mace ta rabu da mijinta.
11 Ako li se pak i razdvoji, da se više ne udaje, ili da se pomiri sa svojijem mužem i muž da ne pušæa žene.
In kuwa ta rabu da shi, sai ta kasance ba aure, ko kuma ta sāke shiryawa da mijinta. Kada miji kuma yă saki matarsa.
12 A ostalima govorim ja a ne Gospod: ako koji brat ima ženu nekrštenu i ona se privoli življeti s njim, da je ne ostavlja.
Ga sauran kuwa (ni ne fa na ce ba Ubangiji ba), in wani ɗan’uwa yana da mata wadda ba mai bi ba ce, kuma tana so ta zauna tare da shi, kada yă sake ta.
13 I žena ako ima muža nekrštena i on se privoli življeti s njom, da ga ne ostavlja.
In kuma mace tana da miji wanda ba mai bi ba ne, kuma yana so yă zauna tare da ita, kada tă kashe auren.
14 Jer se posveti muž nekršten ženom krštenom, i posveti se žena nekrštena od muža krštenoga; jer inaèe djeca vaša bila bi neèista, a sad su sveta.
Don miji marar ba da gaskiya an tsarkake shi ta wurin matarsa. Mace marar ba da gaskiya kuma an tsarkake ta ta wurin mijinta. In ba haka ba’ya’yanku ba za su zama da tsarki ba, amma kamar yadda yake, su masu tsarki ne.
15 Ako li se nekršteni razdvaja, neka se razdvoji; jer se brat ili sestra u takovom dogaðaju ne zarobi; jer nas na mir dozva Gospod Bog.
Amma in marar bi ɗin ya raba auren, a ƙyale shi. A irin wannan hali, babu tilas a kan wani, ko wata mai bi. Allah ya kira mu ga zaman lafiya ne.
16 Jer šta znaš, ženo, da ako muža spaseš? ili šta znaš, mužu, da ako ženu spaseš?
Ke mace, kin sani ne, ko ke ce za ki ceci mijinki? Kai miji, ka sani ne, ko kai ne za ka ceci matarka?
17 Samo kao što je Bog razdijelio svakome, i kao što je svakoga pozvao Gospod onako neka živi. I tako zapovijedam po svijem crkvama.
Duk da haka, sai kowa yă kasance a rayuwar da Ubangiji ya sa shi da kuma wanda Allah ya kira shi. Umarnin da na kafa a dukan ikkilisiyoyi ke nan.
18 Je li ko pozvat obrezan, neka se ne gradi neobrezan; ako li je ko pozvat neobrezan, neka se ne obrezuje.
In an riga an yi wa mutum kaciya sa’ad da aka kira shi, to, kada yă zama marar kaciya. In an kira mutum sa’ad da yake marar kaciya, to, kada a yi masa kaciya.
19 Obrezanje je ništa, i neobrezanje je ništa; nego držanje zapovijesti Božijeh.
Kaciya ba wani abu ba ne, rashin kaciya kuma ba wani abu ba ne. Kiyaye umarnin Allah shi ne muhimmin abu.
20 Svaki neka ostane u onome zvanju u kome je pozvan.
Ya kamata kowa yă kasance a matsayin da yake ciki sa’ad da Allah ya kira shi.
21 Jesi li pozvan rob, ne brini se; nego ako i možeš svoj biti, još radije budi.
Kai bawa ne sa’ad da aka kira ka? Kada wannan yă dame ka, sai dai in kana iya samun’yanci, sai ka yi amfani da wannan dama.
22 Jer koji je pozvan u Gospodu rob, slobodnjak je Gospodnji, tako i koji je pozvan slobodnjak, rob je Hristov.
Gama wanda yake bawa sa’ad da Ubangiji ya kira shi,’yantacce ne na Ubangiji; haka ma, wanda yake’yantacce sa’ad da aka kira shi, bawa ne na Kiristi.
23 Kupljeni ste skupo, ne budite robovi ljudima.
Da tsada fa aka saye ku, kada ku zama bayin mutane.
24 Svaki, braæo, u èemu je ko pozvan u onome neka ostane pred Gospodom.
’Yan’uwa, a duk matsayin da mutum yake sa’ad da aka kira shi, sai yă kasance haka a sabuwar dangantakarsa da Allah.
25 A za djevojke nemam zapovijesti Gospodnje, nego dajem svjet, kao koji sam pomilovan od Gospoda, da budem vjeran.
To, game da budurwai. Ba ni da wani umarni daga Ubangiji, sai dai na yanke hukunci a matsayi wanda yake amintacce ta wurin jinƙan Ubangiji.
26 Mislim dakle ovo da æe biti dobro za sadašnju nevolju da je èovjeku dobro tako biti.
Saboda ƙuncin rayuwar da ake ciki, ina gani ya fi kyau ku kasance yadda kuke.
27 Jesi li se privezao za ženu, ne traži da se razdriješiš; jesi li se odriješio od žene, ne traži žene.
In kuna da aure, kada ku nemi kashe auren. In ba ku da aure, kada ku nemi yin aure.
28 A ako li se i oženiš, nijesi sagriješio; i djevojka ako se uda, nije sagriješila: ali æe imati takovi nevolje tjelesne; a ja vas žalim.
Amma idan ka riga ka yi aure, to, ba laifi, ba zunubi ba ne, kuma idan yarinya ta yi aure, ba tă yi laifi ba. Sai dai waɗanda suka yi aure za su fuskanci damuwoyi masu yawa a cikin rayuwa, ni kuwa ina so in fisshe su daga wannan.
29 A ovo govorim, braæo, jer je ostalo vrijeme prekraæeno, da æe i oni koji imaju žene biti kao oni koji nemaju;
’Yan’uwa, abin da nake nufi shi ne, lokaci ya rage kaɗan. Daga yanzu, waɗanda suke da mata ya kamata su yi rayuwa kamar ba su da su;
30 I koji plaèu kao koji ne plaèu; i koji se raduju kao koji se ne raduju; i koji kupuju kao koji nemaju;
waɗanda suke kuka kuma kamar ba kuka suke yi ba, waɗanda suke farin ciki kuwa kamar ba farin ciki suke yi ba. Waɗanda suka sayi abu su yi kamar ba nasu ba ne;
31 I koji ovaj svijet upotrebljavaju kao da ga ne upotrebljavaju: jer prolazi oblièje ovoga svijeta.
masu amfani da kayan duniya kuwa, kada su duƙufa a cikinsu. Gama duniyan nan a yadda take mai shuɗewa ce.
32 A ja hoæu da ste vi bezbrižni. Ko je neoženjen brine se za Gospodnje, kako æe ugoditi Gospodu;
Zan so ku’yantu daga damuwa. Mutum marar aure ya damu ne da al’amuran Ubangiji, yadda zai gamshi Ubangiji.
33 A koji je oženjen brine se za svjetsko, kako æe ugoditi ženi. Drugo je žena, a drugo je djevojka.
Amma mutumin da yake da aure yakan damu ne da al’amuran wannan duniya, yadda zai gamshi matarsa
34 Koja je neudata brine se za Gospodnje, kako æe ugoditi Gospodu, da bude sveta i tijelom i duhom; a koja je udata brine se za svjetsko, kako æe ugoditi mužu.
hankalinsa a rabe yake. Mace marar aure ko kuwa budurwa ta damu ne da al’amuran Ubangiji. Nufinta shi ne ta ba da kanta ga Ubangiji cikin jiki da ruhu. Amma mace da take da aure ta damu ne da al’amuran wannan duniya, yadda za tă gamshi mijinta.
35 A ovo govorim na korist vama samijem, ne da vam nametnem zamku na vrat, nego za lijepu i pristojnu službu Gospodu bez smetnje.
Na faɗa haka don amfaninku ne, ba don in ƙuntata muku ba. Sai dai don ku yi rayuwa a hanyar da ta dace da nufin ku himmantu ga bautar Ubangiji ba da raba hankali ba.
36 Ako li pak ko misli da je sramota za njegovu djevojku kad ostane usidjelica, i ne može drukèije biti, neka èini šta hoæe, ne griješi ako se uda.
In mutum ya ga cewa ba ya nuna halin da ya kamata ga budurwar da ya yi alkawarin aure da ita, in kuma shekarunta suna wucewa, shi kuma ya ga ya kamata yă yi aure, to, sai yă yi. Ba zunubi ba ne. Ya kamata su yi aure.
37 A koji stoji tvrdo u srcu, i nema nevolje, a ima vlast nad svojom voljom, i ovo je rasudio u srcu svojemu da zadrži djevojku, dobro èini.
Amma mutumin da ya riga ya yanke shawara a ransa, wanda kuma ba lalle ba ne amma yana iya shan kan nufinsa, kuma ya riga ya zartar a zuciyarsa ba zai auri budurwar ba, wannan mutum ma ya yi abin da ya dace.
38 Tako i onaj koji udaje svoju djevojku dobro èini; ali koji ne udaje bolje èini.
Don haka, wanda ya auri budurwar ya yi daidai, amma wanda bai aure ta ba ya ma fi.
39 Žena je privezana zakonom dokle joj god živi muž; a ako joj umre muž, slobodna je za koga hoæe da se uda, samo u Gospodu.
Mace tana haɗe da mijinta muddin yana da rai. Amma in mijinta ya mutu, tana da’yanci ta auri wanda take so. Amma fa, sai mai bin Ubangiji.
40 Ali je blaženija ako ostane tako po mojemu svjetu; jer mislim da i ja imam Duha Božijega.
A nawa ra’ayi, za tă fi jin daɗi in ta zauna haka, a ganina kuwa ina ba ku shawara ce daga Ruhun Allah da na ce haka.

< 1 Korinæanima 7 >