< 1 Dnevnika 21 >

1 Ali usta sotona na Izrailja i navrati Davida da izbroji Izrailja.
Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
2 I reèe David Joavu i knezovima narodnijem: idite, izbrojte sinove Izrailjeve od Virsaveje dori do Dana, pa mi javite da znam koliko ih ima.
Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
3 Ali Joav reèe: neka doda Gospod narodu svojemu koliko ga je sada još sto puta toliko; nijesu li, care gospodaru moj, svi sluge gospodaru mojemu? zašto traži to gospodar moj? zašto da bude na grijeh Izrailju?
Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
4 Ali rijeè careva nadjaèa Joava. I tako otide Joav i obide svega Izrailja, pa se vrati u Jerusalim.
Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
5 I dade Joav broj prepisanoga naroda Davidu; i bijaše svega naroda Izrailjeva tisuæa tisuæa i sto tisuæa ljudi koji mahahu maèem, a naroda Judina èetiri stotine i sedamdeset tisuæa ljudi koji mahahu maèem.
Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
6 A plemena Levijeva i Venijaminova ne izbroji s njima, jer mrska bješe Joavu zapovijest careva.
Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
7 A ne bješe mila Bogu ta stvar; zato udari Izrailja.
Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
8 I David reèe Bogu: sagriješih veoma što to uradih; ali uzmi bezakonje sluge svojega, jer veoma ludo radih.
Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
9 A Gospod reèe Gadu vidiocu Davidovu govoreæi:
Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
10 Idi kaži Davidu i reci: ovako veli Gospod: troje ti dajem, izberi jedno da ti uèinim.
“Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’”
11 I doðe Gad k Davidu i reèe mu: tako veli Gospod, biraj:
Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
12 Ili glad za tri godine, ili tri mjeseca da bježiš od neprijatelja svojih i maè neprijatelja tvojih da te stiže, ili tri dana maè Gospodnji i pomor da bude u zemlji i anðeo Gospodnji da ubija po svijem krajevima Izrailjevijem. Sada dakle gledaj što æu odgovoriti onomu koji me je poslao.
shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
13 A David reèe Gadu: u tjeskobi sam ljutoj; ali neka zapadnem Gospodu u ruke, jer je veoma velika milost njegova; a ljudima da ne zapadnem u ruke.
Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
14 I tako pusti Gospod pomor na Izrailja, te pade Izrailja sedamdeset tisuæa ljudi.
Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
15 I posla Gospod anðela u Jerusalim da ga ubija; i kad ubijaše, pogleda Gospod i sažali mu se sa zla; i reèe anðelu koji ubijaše: dosta, spusti ruku svoju. A anðeo Gospodnji stajaše kod gumna Ornana Jevusejina,
Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
16 A David podiže oèi svoje i vidje anðela Gospodnjega gdje stoji izmeðu zemlje i neba a u ruci mu go maè, kojim bješe zamahnuo na Jerusalim; i pade David i starješine nièice, obuèeni u kostrijet.
Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
17 I reèe David Bogu: nijesam li ja zapovjedio da se izbroji narod? ja sam dakle zgriješio i zlo uèinio; a te ovce šta su uèinile? Gospode Bože moj, neka se ruka tvoja obrati na me i na dom oca mojega; ali ne na taj narod da ga potre.
Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
18 Tada anðeo Gospodnji reèe Gadu da kaže Davidu da izide gore i naèini oltar Gospodu na gumnu Ornana Jevusejina.
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
19 I izide David po rijeèi Gadovoj, koju mu reèe u ime Gospodnje.
Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
20 A Ornan okrenuv se ugleda anðela, i sakri se sa èetiri sina svoja. Jer Ornan vrsijaše pšenicu.
Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika;’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
21 Utom doðe David do Ornana; i pogledav Ornan kad vidje Davida izide iz gumna i pokloni se Davidu licem do zemlje.
Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
22 Tada reèe David Ornanu: daj mi to gumno da naèinim na njemu oltar Gospodu; za novce koliko vrijedi daj mi ga, da bi prestao pomor u narodu.
Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
23 A Ornan reèe Davidu: uzmi i neka èini gospodar moj car što mu je drago; evo dajem i volove za žrtve paljenice, i kola za drva, i pšenicu za dar; sve to dajem.
Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
24 A car David reèe Ornanu: ne, nego æu kupiti za novce šta vrijedi, jer neæu da prinesem Gospodu što je tvoje ni da prinesem žrtve paljenice poklonjene.
Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
25 I dade David Ornanu za ono mjesto na mjeru šest stotina sikala zlata.
Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
26 I ondje naèini David oltar Gospodu, i prinese žrtve paljenice i žrtve zahvalne; i prizva Gospoda, i usliši ga spustivši oganj s neba na oltar žrtve paljenice.
Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
27 I zapovjedi Gospod anðelu, te vrati maè svoj u korice.
Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
28 U ono vrijeme vidjev David da ga Gospod usliši na gumnu Ornana Jevusejina prinošaše žrtve ondje.
A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
29 A šator Gospodnji, koji naèini Mojsije u pustinji, i oltar za žrtve paljenice bijaše u to vrijeme na visini u Gavaonu.
Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
30 I David ne može iæi k njemu da traži Boga, jer se uplaši od maèa anðela Gospodnjega.
Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.

< 1 Dnevnika 21 >