< مَتھِح 26 >

یِیشُریتانْ پْرَسْتاوانْ سَماپْیَ شِشْیانُوچے، 1
Yayin da Yesu ya gama fadi masu wadannan maganganu, sai ya cewa almajiransa,
یُشْمابھِ رْجْناتَں دِنَدْوَیاتْ پَرَں نِسْتارَمَہَ اُپَسْتھاسْیَتِ، تَتْرَ مَنُجَسُتَح کْرُشینَ ہَنْتُں پَرَکَریشُ سَمَرْپِشْیَتے۔ 2
“Kun sani sauran kwana biyu idin ketarewa ya zo, kuma za'a bada Dan mutum domin a gicciye shi.
تَتَح پَرَں پْرَدھانَیاجَکادھْیاپَکَپْرانْچَح کِیَپھانامْنو مَہایاجَکَسْیاٹّالِکایاں مِلِتْوا 3
Sa'annan manyan firistoci da dattawan jama'a suka taru a fadar babban firist, mai suna Kayafa.
کینوپایینَ یِیشُں دھرِتْوا ہَنْتُں شَکْنُیُرِتِ مَنْتْرَیانْچَکْرُح۔ 4
Suka shirya yadda zasu kama Yesu a boye su kuma kashe shi.
کِنْتُ تَیرُکْتَں مَہَکالے نَ دھَرْتَّوْیَح، دھرِتے پْرَجاناں کَلَہینَ بھَوِتُں شَکْیَتے۔ 5
Amma suna cewa, “Ba a lokacin idin ba, domin kada tarzoma ta tashi daga cikin mutane.”
تَتو بَیتھَنِیاپُرے شِموناکھْیَسْیَ کُشْٹھِنو ویشْمَنِ یِیشَو تِشْٹھَتِ 6
Sa'adda Yesu yake Baita'anya a gidan Saminu Kuturu,
کاچَنَ یوشا شْویتوپَلَبھاجَنینَ مَہارْگھْیَں سُگَنْدھِ تَیلَمانِییَ بھوجَنایوپَوِشَتَسْتَسْیَ شِروبھْیَشیچَتْ۔ 7
daidai lokacin da ya zauna a gefen teburin cin abinci, sai wata mata ta shigo da kwalbar mai, mai tsada, ta zuba wa Yesu a kansa.
کِنْتُ تَدالوکْیَ تَچّھِشْیَیح کُپِتَیرُکْتَں، کُتَ اِتّھَمَپَوْیَیَتے؟ 8
Amma da almajiransa suka ga haka, sai suka ji haushi suka ce, “Ina dalilin yin irin wannan asara?
چیدِدَں وْیَکْریشْیَتَ، تَرْہِ بھُورِمُولْیَں پْراپْیَ دَرِدْریبھْیو وْیَتارِشْیَتَ۔ 9
Ai da an sayar da wannan mai da kudi mai yawa a rabawa talakawa.”
یِیشُنا تَدَوَگَتْیَ تے سَمُدِتاح، یوشامیناں کُتو دُحکھِنِیں کُرُتھَ، سا ماں پْرَتِ سادھُ کَرْمّاکارْشِیتْ۔ 10
Amma da yake Yesu ya san tunaninsu, sai yace masu, “Don me kuke damun matar nan? Ta yi abu mai kyau domina.
یُشْماکَمَں سَمِیپے دَرِدْراح سَتَتَمیواسَتے، کِنْتُ یُشْماکَمَنْتِکیہَں ناسے سَتَتَں۔ 11
Kuna da talakawa tare da ku koyaushe, amma ni ba zan kasance da ku ba koyaushe.
سا مَمَ کایوپَرِ سُگَنْدھِتَیلَں سِکْتْوا مَمَ شْمَشانَدانَکَرْمّاکارْشِیتْ۔ 12
Don a sa'adda ta zuba man nan a jikina, ta yi haka ne don jana'iza ta.
اَتوہَں یُشْمانْ تَتھْیَں وَدامِ سَرْوَّسْمِنْ جَگَتِ یَتْرَ یَتْرَیشَ سُسَماچارَح پْرَچارِشْیَتے، تَتْرَ تَتْرَیتَسْیا نارْیّاح سْمَرَنارْتھَمْ کَرْمّیدَں پْرَچارِشْیَتے۔ 13
Hakika Ina gaya maku, duk inda za ayi wannan bishara a dukan duniya, abin da matar nan tayi za'a rika ambatar da shi don tunawa da ita.”
تَتو دْوادَشَشِشْیانامْ اِیشْکَرِیوتِییَیِہُودانامَکَ ایکَح شِشْیَح پْرَدھانَیاجَکانامَنْتِکَں گَتْوا کَتھِتَوانْ، 14
Sai daya daga cikin sha biyun, mai suna Yahuza Iskariyoti, ya tafi wurin manyan firistocin,
یَدِ یُشْماکَں کَریشُ یِیشُں سَمَرْپَیامِ، تَرْہِ کِں داسْیَتھَ؟ تَدانِیں تے تَسْمَے تْرِںشَنْمُدْرا داتُں سْتھِرِیکرِتَوَنْتَح۔ 15
yace, ''Me kuke da niyyar bani idan na mika maku shi?” Suka auna masa azurfa talatin.
سَ تَدارَبھْیَ تَں پَرَکَریشُ سَمَرْپَیِتُں سُیوگَں چیشْٹِتَوانْ۔ 16
Daga wannan lokacin yayi ta neman zarafi da zai bada shi a wurinsu.
اَنَنْتَرَں کِنْوَشُونْیَپُوپَپَرْوَّنَح پْرَتھَمیہْنِ شِشْیا یِیشُمْ اُپَگَتْیَ پَپْرَچّھُح بھَوَتْکرِتے کُتْرَ وَیَں نِسْتارَمَہَبھوجْیَمْ آیوجَیِشْیامَح؟ بھَوَتَح کیچّھا؟ 17
To a rana ta fari na idin ketarewa almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, ''Ina kake so mu shirya maka da zaka ci abincin idin ketarewa?”
تَدا سَ گَدِتَوانْ، مَدھْیینَگَرَمَمُکَپُںسَح سَمِیپَں وْرَجِتْوا وَدَتَ، گُرُ رْگَدِتَوانْ، مَتْکالَح سَوِدھَح، سَہَ شِشْیَیسْتْوَدالَیے نِسْتارَمَہَبھوجْیَں بھوکْشْیے۔ 18
Yace, “Ku shiga cikin birnin zaku sami wani mutum sai kuce masa, 'Mallam yace, “lokaci na ya kusa. Zan ci idin ketarewa a gidanka, da almajiraina.”'''
تَدا شِشْیا یِیشوسْتادرِشَنِدیشانُرُوپَکَرْمَّ وِدھایَ تَتْرَ نِسْتارَمَہَبھوجْیَماسادَیاماسُح۔ 19
Almajiran suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su, suka shirya abincin idin ketarewar.
تَتَح سَنْدھْیایاں سَتْیاں دْوادَشَبھِح شِشْیَیح ساکَں سَ نْیَوِشَتْ۔ 20
Da yamma ta yi, sai ya zauna domin ya ci tare da almajiransa goma sha biyu.
اَپَرَں بھُنْجانَ اُکْتَوانْ یُشْمانْ تَتھْیَں وَدامِ، یُشْماکَمیکو ماں پَرَکَریشُ سَمَرْپَیِشْیَتِ۔ 21
Sa'adda suke ci, yace, “Hakika ina gaya maku, daya daga cikin ku zai bada ni.”
تَدا تےتِیوَ دُحکھِتا ایکَیکَشو وَکْتُماریبھِرے، ہے پْرَبھو، سَ کِمَہَں؟ 22
Suka yi bakin ciki, suka fara tambayarsa daya bayan daya, ''Na tabbata ba ni bane ko, Ubangiji?”
تَتَح سَ جَگادَ، مَیا ساکَں یو جَنو بھوجَنَپاتْرے کَرَں سَںکْشِپَتِ، سَ ایوَ ماں پَرَکَریشُ سَمَرْپَیِشْیَتِ۔ 23
Sai ya amsa, “Wanda ke sa hannu tare da ni cikin kwano daya shi ne zai bada ni.
مَنُجَسُتَمَدھِ یادرِشَں لِکھِتَماسْتے، تَدَنُرُوپا تَدْگَتِ رْبھَوِشْیَتِ؛ کِنْتُ یینَ پُںسا سَ پَرَکَریشُ سَمَرْپَیِشْیَتے، ہا ہا چیتْ سَ ناجَنِشْیَتَ، تَدا تَسْیَ کْشیمَمَبھَوِشْیَتْ۔ 24
Dan mutum zai tafi, kamar yadda aka rubuta akan sa. Amma kaiton mutumin da ta wurin sa za'a bada Dan mutum! Gwamma da ba'a haifi mutumin nan ba.”
تَدا یِہُوداناما یو جَنَسْتَں پَرَکَریشُ سَمَرْپَیِشْیَتِ، سَ اُکْتَوانْ، ہے گُرو، سَ کِمَہَں؟ تَتَح سَ پْرَتْیُکْتَوانْ، تْوَیا سَتْیَں گَدِتَمْ۔ 25
Yahuza da zai bada shi yace, “Mallam ko ni ne?” Yace masa, “Ka fada da kanka.”
اَنَنْتَرَں تیشامَشَنَکالے یِیشُح پُوپَماداییشْوَرِییَگُنانَنُودْیَ بھَںکْتْوا شِشْییبھْیَح پْرَدایَ جَگادَ، مَدْوَپُحسْوَرُوپَمِمَں گرِہِیتْوا کھادَتَ۔ 26
Yayin da suke ci, sai Yesu ya dauki gurasa, ya sa albarka, ya karya. Ya ba almajiran yace, “Ku karba, ku ci, wannan jiki nane.”
پَشْچاتْ سَ کَںسَں گرِہْلَنْ اِیشْوَرِییَگُنانَنُودْیَ تیبھْیَح پْرَدایَ کَتھِتَوانْ، سَرْوَّے رْیُشْمابھِرَنینَ پاتَوْیَں، 27
Sai ya dauki kokon yayi godiya, Ya ba su yace, “Ku sha, dukanku.
یَسْمادَنیکیشاں پاپَمَرْشَنایَ پاتِتَں یَنْمَنُّوتْنَنِیَمَرُوپَشونِتَں تَدیتَتْ۔ 28
“Gama wannan jinina ne na alkawari wanda aka zubar domin gafarar zunuban mutane da yawa.
اَپَرَمَہَں نُوتْنَگوسْتَنِیرَسَں نَ پاسْیامِ، تاوَتْ گوسْتَنِیپھَلَرَسَں پُنَح کَداپِ نَ پاسْیامِ۔ 29
Amma ina gaya maku, ba zan kara shan ruwan inabin nan ba, sai ranar da zan sha shi sabo tare da ku a cikin mulkin Ubana.”
پَشْچاتْ تے گِیتَمیکَں سَںگِییَ جَیتُناکھْیَگِرِں گَتَوَنْتَح۔ 30
Da suka raira waka, sai suka ka tafi dutsen zaitun.
تَدانِیں یِیشُسْتانَووچَتْ، اَسْیاں رَجَنْیامَہَں یُشْماکَں سَرْوّیشاں وِگھْنَرُوپو بھَوِشْیامِ، یَتو لِکھِتَماسْتے، "میشاناں رَکْشَکو یَسْتَں پْرَہَرِشْیامْیَہَں تَتَح۔ میشاناں نِوَہو نُونَں پْرَوِکِیرْنو بھَوِشْیَتِ"۔۔ 31
Sai Yesu yace masu, “Dukan ku zaku yi tuntube a wannan dare sabili da ni, gama a rubuce yake, ''Zan bugi makiyayin, garken tumakin kuma za su watse.'
کِنْتُ شْمَشاناتْ سَمُتّھایَ یُشْماکَمَگْرےہَں گالِیلَں گَمِشْیامِ۔ 32
Amma bayan an tashe ni, zan riga ku zuwa Galili.”
پِتَرَسْتَں پْروواچَ، بھَواںشْچیتْ سَرْوّیشاں وِگھْنَرُوپو بھَوَتِ، تَتھاپِ مَمَ نَ بھَوِشْیَتِ۔ 33
Amma Bitrus yace masa, “Ko dama duka zasu fadi sabili da kai, ni kam bazan fadi ba.”
تَتو یِیشُنا سَ اُکْتَح، تُبھْیَمَہَں تَتھْیَں کَتھَیامِ، یامِنْیامَسْیاں چَرَنایُدھَسْیَ رَواتْ پُورْوَّں تْوَں ماں تْرِ رْنانْگِیکَرِشْیَسِ۔ 34
Yesu yace masa, ''Hakika ina gaya maka, a wannan daren kafin carar zakara, za ka yi musun sani na sau uku.”
تَتَح پِتَرَ اُدِتَوانْ، یَدْیَپِ تْوَیا سَمَں مَرْتَّوْیَں، تَتھاپِ کَداپِ تْواں نَ نانْگِیکَرِشْیامِ؛ تَتھَیوَ سَرْوّے شِشْیاشْچوچُح۔ 35
Bitrus yace masa, koda zan mutu tare da kai, bazan yi musunka ba.” Sai sauran almajiran suma suka fadi haka.
اَنَنْتَرَں یِیشُح شِشْیَیح ساکَں گیتْشِمانِینامَکَں سْتھانَں پْرَسْتھایَ تیبھْیَح کَتھِتَوانْ، اَدَح سْتھانَں گَتْوا یاوَدَہَں پْرارْتھَیِشْیے تاوَدْ یُویَمَتْروپَوِشَتَ۔ 36
Sa'anna Yesu ya tafi tare da su, wurin da ake kira Getsaimani sai yace wa almajiransa, ''Ku zauna a nan ni kuma zan je gaba in yi addu'a.”
پَشْچاتْ سَ پِتَرَں سِوَدِیَسُتَو چَ سَنْگِنَح کرِتْوا گَتَوانْ، شوکاکُلوتِیوَ وْیَتھِتَشْچَ بَبھُووَ۔ 37
Ya dauki Bitrus da kuma 'ya'ya biyu na Zabadi tare da shi, sai ya fara damuwa da juyayi.
تانَوادِیچَّ مرِتِیاتَنیوَ مَتْپْراناناں یاتَنا جایَتے، یُویَمَتْرَ مَیا سارْدّھَں جاگرِتَ۔ 38
Sai yace masu, “Raina na cikin damuwa sosai har ga mutuwa. Ku kasance anan kuna tsaro tare da ni.”
تَتَح سَ کِنْچِدُّورَں گَتْوادھومُکھَح پَتَنْ پْرارْتھَیانْچَکْرے، ہے مَتْپِتَرْیَدِ بھَوِتُں شَکْنوتِ، تَرْہِ کَںسویَں مَتّو دُورَں یاتُ؛ کِنْتُ مَدِچّھاوَتْ نَ بھَوَتُ، تْوَدِچّھاوَدْ بھَوَتُ۔ 39
Ya dan taka zuwa gaba kadan, sai ya fadi a fuskarsa, yayi addu'a. Yace, “Ya Ubana, in zai yiwu, bari kokon nan ya wuce ni. Duk da haka, ba nufina za'a bi ba, amma naka nufin.”
تَتَح سَ شِشْیانُپیتْیَ تانْ نِدْرَتو نِرِیکْشْیَ پِتَرایَ کَتھَیاماسَ، یُویَں مَیا ساکَں دَنْڈَمیکَمَپِ جاگَرِتُں ناشَنْکُتَ؟ 40
Ya koma wurin almajiran ya same su suna barci, sai ya cewa Bitrus, “Kai, ba zaku yi tsaro tare da ni ba koda sa'a daya?
پَرِیکْشایاں نَ پَتِتُں جاگرِتَ پْرارْتھَیَدھْوَنْچَ؛ آتْما سَمُدْیَتوسْتِ، کِنْتُ وَپُ رْدُرْبَّلَں۔ 41
Ku yi tsaro kuma, kuyi addu'a domin kada ku fada cikin jaraba. Ruhu dai ya yarda amma, jiki ba karfi.”
سَ دْوِتِییَوارَں پْرارْتھَیانْچَکْرے، ہے مَتّاتَ، نَ پِیتے یَدِ کَںسَمِدَں مَتّو دُورَں یاتُں نَ شَکْنوتِ، تَرْہِ تْوَدِچّھاوَدْ بھَوَتُ۔ 42
Sai ya koma karo na biyu yayi addu'a, Yace, “Ya Ubana, in wannan kokon ba zai wuce ba sai na sha shi, bari nufinka ya kasance.”
سَ پُنَریتْیَ تانْ نِدْرَتو دَدَرْشَ، یَتَسْتیشاں نیتْرانِ نِدْرَیا پُورْنانْیاسَنْ۔ 43
Ya sake dawowa, ya same su suna barci, domin idanunsu sun yi nauyi.
پَشْچاتْ سَ تانْ وِہایَ وْرَجِتْوا ترِتِییَوارَں پُورْوَّوَتْ کَتھَیَنْ پْرارْتھِتَوانْ۔ 44
Sai ya sake barinsu ya tafi. Ya koma karo na uku yana addu'a yana fadin kalmomi iri daya.
تَتَح شِشْیانُپاگَتْیَ گَدِتَوانْ، سامْپْرَتَں شَیاناح کِں وِشْرامْیَتھَ؟ پَشْیَتَ، سَمَیَ اُپاسْتھاتْ، مَنُجَسُتَح پاپِناں کَریشُ سَمَرْپْیَتے۔ 45
Sai Yesu ya koma wurin almajiran yace masu, “Har yanzu barci kuke kuna hutawa? Duba, lokaci ya kusato, kuma an bada Dan mutum ga hannun masu zunubi.
اُتِّشْٹھَتَ، وَیَں یامَح، یو ماں پَرَکَریشُ مَسَرْپَیِشْیَتِ، پَشْیَتَ، سَ سَمِیپَمایاتِ۔ 46
Ku tashi mu tafi. Duba, wanda zai badani ya kusato.”
ایتَتْکَتھاکَتھَنَکالے دْوادَشَشِشْیانامیکو یِہُودانامَکو مُکھْیَیاجَکَلوکَپْراچِینَیح پْرَہِتانْ اَسِدھارِیَشْٹِدھارِنو مَنُجانْ گرِہِیتْوا تَتْسَمِیپَمُپَتَسْتھَو۔ 47
Sa'adda yana cikin magana Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya zo. Babban taro ya zo tare da shi daga wurin manyan firistoci da dattawan jama'a. Suna rike da takubba da kulake.
اَسَو پَرَکَریشْوَرْپَیِتا پُورْوَّں تانْ اِتّھَں سَنْکیتَیاماسَ، یَمَہَں چُمْبِشْیے، سوسَو مَنُجَح،سَایوَ یُشْمابھِ رْدھارْیَّتاں۔ 48
To mutumin da zai bada Yesu ya rigaya ya basu alama, cewa, ''Duk wanda na sumbata, shine. Ku kama shi.''
تَدا سَ سَپَدِ یِیشُمُپاگَتْیَ ہے گُرو، پْرَنَمامِیتْیُکْتْوا تَں چُچُمْبے۔ 49
Nan da nan ya kaiga Yesu ya ce, “Gaisuwa, Mallam!” sai ya sumbace shi.
تَدا یِیشُسْتَمُواچَ، ہے مِتْرَں کِمَرْتھَماگَتوسِ؟ تَدا تَیراگَتْیَ یِیشُراکْرَمْیَ دَگھْرے۔ 50
Yesu kuwa yace masa, “Aboki, kayi abin da ya kawo ka.” Sai suka iso suka sa hannuwansu kan Yesu suka kama shi.
تَتو یِیشوح سَنْگِنامیکَح کَرَں پْرَسارْیَّ کوشادَسِں بَہِشْکرِتْیَ مَہایاجَکَسْیَ داسَمیکَماہَتْیَ تَسْیَ کَرْنَں چِچّھیدَ۔ 51
Nan take, daya daga cikin wadanda suke tare da Yesu ya mika hannunsa, ya zare takobinsa, ya sare wa bawan babban firist din kunne.
تَتو یِیشُسْتَں جَگادَ، کھَڈْگَں سْوَسْتھانے نِدھیہِ یَتو یے یے جَنا اَسِں دھارَیَنْتِ، تَایواسِنا وِنَشْیَنْتِ۔ 52
Sai Yesu yace, masa, “Ka maida takobinka cikin kubensa, domin duk wadanda suka dauki takobi su ma ta wurin takobi za su hallaka.
اَپَرَں پِتا یَتھا مَدَنْتِکَں سْوَرْگِییَدُوتاناں دْوادَشَواہِنِیتودھِکَں پْرَہِنُیاتْ مَیا تَمُدِّشْییدانِیمیوَ تَتھا پْرارْتھَیِتُں نَ شَکْیَتے، تْوَیا کِمِتّھَں جْنایَتے؟ 53
Ko kana tunanin ba zan iya kiran Ubana ba, ya kuma aiko da rundunar Mala'iku fiye da goma sha biyu?
تَتھا سَتِیتّھَں گھَٹِشْیَتے دھَرْمَّپُسْتَکَسْیَ یَدِدَں واکْیَں تَتْ کَتھَں سِدھْییتْ؟ 54
Amma to tayaya za'a cika nassi, cewa dole wannan ya faru?''
تَدانِیں یِیشُ رْجَنَنِوَہَں جَگادَ، یُویَں کھَڈْگَیَشْٹِینْ آدایَ ماں کِں چَورَں دھَرْتُّمایاتاح؟ اَہَں پْرَتْیَہَں یُشْمابھِح ساکَمُپَوِشْیَ سَمُپادِشَں، تَدا ماں نادھَرَتَ؛ 55
A wannan lokacin Yesu yace wa taron, “Kun zo da takubba da kulake ku kama ni kamar dan fashi? Ina zaune kowace rana a haikali ina koyarwa, amma baku kama ni ba.
کِنْتُ بھَوِشْیَدْوادِناں واکْیاناں سَںسِدّھَیے سَرْوَّمیتَدَبھُوتْ۔ تَدا سَرْوّے شِشْیاسْتَں وِہایَ پَلایَنْتَ۔ 56
Amma duk wannan ya faru ne don a cika abinda annabawa suka rubuta.” Bayan haka sai dukkan almajiran suka bar shi suka gudu.
اَنَنْتَرَں تے مَنُجا یِیشُں دھرِتْوا یَتْرادھْیاپَکَپْرانْچَح پَرِشَدَں کُرْوَّنْتَ اُپاوِشَنْ تَتْرَ کِیَپھانامَکَمَہایاجَکَسْیانْتِکَں نِنْیُح۔ 57
Wadanda suka kama Yesu, suka kai shi wurin Kayafa babban firist, inda marubuta da duttawan jama'a suka taru.
کِنْتُ شیشے کِں بھَوِشْیَتِیتِ ویتُّں پِتَرو دُورے تَتْپَشْچادْ وْرَجِتْوا مَہایاجَکَسْیاٹّالِکاں پْرَوِشْیَ داسَیح سَہِتَ اُپاوِشَتْ۔ 58
Amma Bitrus ya bi shi daga nesa, har zuwa farfajiyar babban firist din. Ya shiga ya zauna da masu tsaro domin ya ga abinda zai faru.
تَدانِیں پْرَدھانَیاجَکَپْراچِینَمَنْتْرِنَح سَرْوّے یِیشُں ہَنْتُں مرِشاساکْشْیَمْ اَلِپْسَنْتَ، 59
A wannan lokaci manyan firistoci da duk 'yan majalisar suka fara neman shaidar karya akan Yesu, domin su samu su kashe shi.
کِنْتُ نَ لیبھِرے۔ اَنیکیشُ مرِشاساکْشِشْواگَتیشْوَپِ تَنَّ پْراپُح۔ 60
Amma ba su samu ko daya ba, ko dayake an samu shaidun karya dayawa da suka gabata. Amma daga baya sai wasu su biyu suka fito
شیشے دْوَو مرِشاساکْشِناواگَتْیَ جَگَدَتُح، پُمانَیَمَکَتھَیَتْ، اَہَمِیشْوَرَمَنْدِرَں بھَںکْتْوا دِنَتْرَیَمَدھْیے تَنِّرْمّاتُں شَکْنومِ۔ 61
sukace ''Wannan mutum yace zan iya rushe haikalin Allah, in kuma gina shi cikin kwana uku.'''
تَدا مَہایاجَکَ اُتّھایَ یِیشُمْ اَوادِیتْ۔ تْوَں کِمَپِ نَ پْرَتِوَدَسِ؟ تْوامَدھِ کِمیتے ساکْشْیَں وَدَنْتِ؟ 62
Babban Firist din ya tashi tsaye yace masa, “Ba zaka ce komai ba? Wace irin shaida ce ake yi akanka?”
کِنْتُ یِیشُ رْمَونِیبھُویَ تَسْیَو۔ تَتو مَہایاجَکَ اُکْتَوانْ، تْوامْ اَمَریشْوَرَنامْنا شَپَیامِ، تْوَمِیشْوَرَسْیَ پُتْروبھِشِکْتو بھَوَسِ نَویتِ وَدَ۔ 63
Amma Yesu yayi shiru. Babban Firist ya ce, “Na umarce ka da sunan Allah mai rai, ka gaya mana ko kai Almasihu ne, Dan Allah.''
یِیشُح پْرَتْیَوَدَتْ، تْوَں سَتْیَمُکْتَوانْ؛ اَہَں یُشْمانْ تَتھْیَں وَدامِ، اِتَحپَرَں مَنُجَسُتَں سَرْوَّشَکْتِمَتو دَکْشِنَپارْشْوے سْتھاتُں گَگَنَسْتھَں جَلَدھَرانارُہْیایانْتَں وِیکْشَدھْوے۔ 64
Yesu ya amsa masa, “Ka fada da bakin ka. Amma ina gaya maka, daga yanzu zaka ga Dan mutun na zaune a hannun dama na iko, ya na zuwa akan gizagizai na sama.”
تَدا مَہایاجَکو نِجَوَسَنَں چھِتّوا جَگادَ، ایشَ اِیشْوَرَں نِنْدِتَوانْ، اَسْماکَمَپَرَساکْشْیینَ کِں پْرَیوجَنَں؟ پَشْیَتَ، یُویَمیواسْیاسْیادْ اِیشْوَرَنِنْداں شْرُتَوَنْتَح، 65
Sai babban firist din ya yayyaga rigarsa, yana cewa, “Yayi sabo! don me ku ke neman wata shaida kuma? Duba, yanzu kun ji sabon.
یُشْمابھِح کِں وِوِچْیَتے؟ تے پْرَتْیُوچُح، وَدھارْہویَں۔ 66
Menene tunaninku?” Suka amsa sukace, “Ya cancanci mutuwa.”
تَتو لوکَیسْتَداسْیے نِشْٹھِیوِتَں کیچِتْ پْرَتَلَماہَتْیَ کیچِچَّ چَپیٹَماہَتْیَ بَبھاشِرے، 67
Sai suka tofa masa yawu a fuska, suka kuma yi masa duka, suka kuma mammare shi da tafin hannuwansu,
ہے کھْرِیشْٹَ تْواں کَشْچَپیٹَماہَتَوانْ؟ اِتِ گَنَیِتْوا وَداسْمانْ۔ 68
sukace, ''Ka yi mana anabci, kai Almasihu. Wanene wanda ya dokeka.
پِتَرو بَہِرَنْگَنَ اُپَوِشَتِ، تَدانِیمیکا داسِی تَمُپاگَتْیَ بَبھاشے، تْوَں گالِیلِییَیِیشوح سَہَچَرَایکَح۔ 69
To Bitrus kuwa na zaune a farfajiyar, sai wata yarinya baiwa ta zo wurinsa tana cewa, “Kaima kana tare da Yesu na Galili.”
کِنْتُ سَ سَرْوّیشاں سَمَکْشَمْ اَنَنْگِیکرِتْیاوادِیتْ، تْوَیا یَدُچْیَتے، تَدَرْتھَمَہَں نَ ویدْمِ۔ 70
Amma ya yi musun haka a gaban su duka, yace, “Ban ma san abinda kike magana akai ba.”
تَدا تَسْمِنْ بَہِرْدْوارَں گَتے نْیا داسِی تَں نِرِیکْشْیَ تَتْرَتْیَجَنانَوَدَتْ، اَیَمَپِ ناسَرَتِییَیِیشُنا سارْدّھَمْ آسِیتْ۔ 71
Da ya fita zuwa bakin kofa, nan ma wata yarinyar baiwa ta gan shi tace wa wadanda suke wurin, “Wannan mutumin ma yana tare da Yesu Banazare.”
تَتَح سَ شَپَتھینَ پُنَرَنَنْگِیکرِتْیَ کَتھِتَوانْ، تَں نَرَں نَ پَرِچِنومِ۔ 72
Sai yayi musun haka kuma, har da rantsuwa, yace, “Ban san mutumin nan ba.”
کْشَناتْ پَرَں تِشْٹھَنْتو جَنا ایتْیَ پِتَرَمْ اَوَدَنْ، تْوَمَوَشْیَں تیشامیکَ اِتِ تْوَدُچّارَنَمیوَ دْیوتَیَتِ۔ 73
Bayan dan lokaci kadan wadanda suke a tsaye suka zo wurin Bitrus suka ce masa, “Hakika kai daya daga cikin su ne, gama harshen ka ya tonaka.”
کِنْتُ سوبھِشَپْیَ کَتھِتَوانْ، تَں جَنَں ناہَں پَرِچِنومِ، تَدا سَپَدِ کُکُّٹو رُراوَ۔ 74
Sai ya fara rantsuwa irin ta la'ana, yana cewa, ''Ban san wannan mutumin ba,” nan da nan zakara yayi cara.
کُکُّٹَرَواتْ پْراکْ تْوَں ماں تْرِرَپاہْنوشْیَسے، یَیشا واگْ یِیشُناوادِ تاں پِتَرَح سَںسْمرِتْیَ بَہِرِتْوا کھیدادْ بھرِشَں چَکْرَنْدَ۔ 75
Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya fada, “Kafin carar zakara zaka yi musun sani na sau uku.” Sai ya fita waje yayi kuka mai zafi.''

< مَتھِح 26 >