< པྲེརིཏཱཿ 9 >

1 ཏཏྐཱལཔཪྻྱནཏཾ ཤཽལཿ པྲབྷོཿ ཤིཥྱཱཎཱཾ པྲཱཏིཀཱུལྱེན ཏཱཌནཱབདྷཡོཿ ཀཐཱཾ ནིཿསཱརཡན྄ མཧཱཡཱཛཀསྱ སནྣིདྷིཾ གཏྭཱ
Ana cikin haka, Shawulu ya ɗage yana barazana yin kisa da tsananta wa almajiran Ubangiji. Sai ya je wurin babban firist
2 སྟྲིཡཾ པུརུཥཉྩ ཏནྨཏགྲཱཧིཎཾ ཡཾ ཀཉྩིཏ྄ པཤྱཏི ཏཱན྄ དྷྲྀཏྭཱ བདྡྷྭཱ ཡིརཱུཤཱལམམ྄ ཨཱནཡཏཱིཏྱཱཤཡེན དམྨེཥཀྣགརཱིཡཾ དྷརྨྨསམཱཛཱན྄ པྲཏི པཏྲཾ ཡཱཙིཏཝཱན྄།
ya roƙe shi ya ba shi wasiƙu zuwa majami’un Damaskus, don in ya sami wani a wurin wanda yake bin wannan Hanya, ko maza ko mata, yă kama su a matsayin’yan kurkuku yă kai Urushalima.
3 གཙྪན྄ ཏུ དམྨེཥཀྣགརནིཀཊ ཨུཔསྠིཏཝཱན྄; ཏཏོ྅ཀསྨཱད྄ ཨཱཀཱཤཱཏ྄ ཏསྱ ཙཏུརྡིཀྵུ ཏེཛསཿ པྲཀཱཤནཱཏ྄ ས བྷཱུམཱཝཔཏཏ྄།
Da ya yi kusa da Damaskus a kan hanyarsa, ba zato ba tsammani sai wani haske daga sama ya haskaka kewaye da shi.
4 པཤྩཱཏ྄ ཧེ ཤཽལ ཧེ ཤཽལ ཀུཏོ མཱཾ ཏཱཌཡསི? སྭཾ པྲཏི པྲོཀྟམ྄ ཨེཏཾ ཤབྡཾ ཤྲུཏྭཱ
Sai ya fāɗi a ƙasa ya kuma ji wata murya ta ce masa, “Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini?”
5 ས པྲྀཥྚཝཱན྄, ཧེ པྲབྷོ བྷཝཱན྄ ཀཿ? ཏདཱ པྲབྷུརཀཐཡཏ྄ ཡཾ ཡཱིཤུཾ ཏྭཾ ཏཱཌཡསི ས ཨེཝཱཧཾ; ཀཎྚཀསྱ མུཁེ པདཱགྷཱཏཀརཎཾ ཏཝ ཀཥྚམ྄།
Shawulu ya yi tambaya ya ce, “Wane ne kai, ya Ubangiji?” Ya amsa ya ce, “Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
6 ཏདཱ ཀམྤམཱནོ ཝིསྨཡཱཔནྣཤྩ སོཝདཏ྄ ཧེ པྲབྷོ མཡཱ ཀིཾ ཀརྟྟཝྱཾ? བྷཝཏ ཨིཙྪཱ ཀཱ? ཏཏཿ པྲབྷུརཱཛྙཱཔཡད྄ ཨུཏྠཱཡ ནགརཾ གཙྪ ཏཏྲ ཏྭཡཱ ཡཏ྄ ཀརྟྟཝྱཾ ཏད྄ ཝདིཥྱཏེ།
Yanzu ka tashi ka shiga cikin birnin, za a kuma gaya maka abin da dole za ka yi.”
7 ཏསྱ སངྒིནོ ལོཀཱ ཨཔི ཏཾ ཤབྡཾ ཤྲུཏཝནྟཿ ཀིནྟུ ཀམཔི ན དྲྀཥྚྭཱ སྟབྡྷཱཿ སནྟཿ སྠིཏཝནྟཿ།
Mutanen da suke tafiya tare da Shawulu suka rasa bakin magana; sun ji muryar amma ba su ga kowa ba.
8 ཨནནྟརཾ ཤཽལོ བྷཱུམིཏ ཨུཏྠཱཡ ཙཀྵུཥཱི ཨུནྨཱིལྱ ཀམཔི ན དྲྀཥྚཝཱན྄། ཏདཱ ལོཀཱསྟསྱ ཧསྟཽ དྷྲྀཏྭཱ དམྨེཥཀྣགརམ྄ ཨཱནཡན྄།
Shawulu ya tashi daga ƙasa, amma sa’ad da ya buɗe idanunsa bai iya ganin wani abu ba. Saboda haka aka kama hannunsa aka yi masa jagora zuwa cikin Damaskus.
9 ཏཏཿ ས དིནཏྲཡཾ ཡཱཝད྄ ཨནྡྷོ བྷཱུཏྭཱ ན བྷུཀྟཝཱན྄ པཱིཏཝཱཾཤྩ།
Kwana uku yana a makance, bai ci ba bai kuma sha kome ba.
10 ཏདནནྟརཾ པྲབྷུསྟདྡམྨེཥཀྣགརཝཱསིན ཨེཀསྨཻ ཤིཥྱཱཡ དརྴནཾ དཏྭཱ ཨཱཧཱུཏཝཱན྄ ཧེ ཨནནིཡ། ཏཏཿ ས པྲཏྱཝཱདཱིཏ྄, ཧེ པྲབྷོ པཤྱ ཤྲྀཎོམི།
A Damaskus kuwa akwai wani almajiri mai suna Ananiyas. Ubangiji ya kira shi a cikin wahayi ya ce, “Ananiyas!” Ananiyas ya amsa, “Ga ni, ya Ubangiji.”
11 ཏདཱ པྲབྷུསྟམཱཛྙཱཔཡཏ྄ ཏྭམུཏྠཱཡ སརལནཱམཱནཾ མཱརྒཾ གཏྭཱ ཡིཧཱུདཱནིཝེཤནེ ཏཱརྵནགརཱིཡཾ ཤཽལནཱམཱནཾ ཛནཾ གཝེཥཡན྄ པྲྀཙྪ;
Ubangiji ya ce masa, “Je gidan Yahuda da yake a Miƙaƙƙen Titi ka yi tambaya ko akwai wani mutum daga Tarshish mai suna Shawulu, gama ga shi yana addu’a.
12 པཤྱ ས པྲཱརྠཡཏེ, ཏཐཱ ཨནནིཡནཱམཀ ཨེཀོ ཛནསྟསྱ སམཱིཔམ྄ ཨཱགཏྱ ཏསྱ གཱཏྲེ ཧསྟཱརྤཎཾ ཀྲྀཏྭཱ དྲྀཥྚིཾ དདཱཏཱིཏྠཾ སྭཔྣེ དྲྀཥྚཝཱན྄།
Cikin wahayi ya ga wani mutum mai suna Ananiyas ya zo ya sa hannuwansa a kansa don yă sāke samun ganin gari.”
13 ཏསྨཱད྄ ཨནནིཡཿ པྲཏྱཝདཏ྄ ཧེ པྲབྷོ ཡིརཱུཤཱལམི པཝིཏྲལོཀཱན྄ པྲཏི སོ྅ནེཀཧིཾསཱཾ ཀྲྀཏཝཱན྄;
Ananiyas ya amsa ya ce, “Ubangiji, na ji labarin mutumin nan sosai da kuma duk lahanin da ya yi wa tsarkakanka a Urushalima.
14 ཨཏྲ སྠཱནེ ཙ ཡེ ལོཀཱསྟཝ ནཱམྣི པྲཱརྠཡནྟི ཏཱནཔི བདྡྷུཾ ས པྲདྷཱནཡཱཛཀེབྷྱཿ ཤཀྟིཾ པྲཱཔྟཝཱན྄, ཨིམཱཾ ཀཐཱམ྄ ཨཧམ྄ ཨནེཀེཥཱཾ མུཁེབྷྱཿ ཤྲུཏཝཱན྄།
Ga shi kuma ya zo nan da izinin manyan firistoci, don yă kama duk wanda yake kiran bisa sunanka.”
15 ཀིནྟུ པྲབྷུརཀཐཡཏ྄, ཡཱཧི བྷིནྣདེཤཱིཡལོཀཱནཱཾ བྷཱུཔཏཱིནཱམ྄ ཨིསྲཱཡེལློཀཱནཱཉྩ ནིཀཊེ མམ ནཱམ པྲཙཱརཡིཏུཾ ས ཛནོ མམ མནོནཱིཏཔཱཏྲམཱསྟེ།
Amma Ubangiji ya ce wa Ananiyas, “Je ka! Wannan mutum zaɓaɓɓen kayan aikina ne don yă kai sunana a gaban Al’ummai da sarakunansu da kuma a gaban mutanen Isra’ila.
16 མམ ནཱམནིམིཏྟཉྩ ཏེན ཀིཡཱན྄ མཧཱན྄ ཀླེཤོ བྷོཀྟཝྱ ཨེཏཏ྄ ཏཾ དརྴཡིཥྱཱམི།
Zan nuna masa wahalar da dole zai sha saboda sunana.”
17 ཏཏོ ྅ནནིཡོ གཏྭཱ གྲྀཧཾ པྲཝིཤྱ ཏསྱ གཱཏྲེ ཧསྟཱརྤྲཎཾ ཀྲྀཏྭཱ ཀཐིཏཝཱན྄, ཧེ བྷྲཱཏཿ ཤཽལ ཏྭཾ ཡཐཱ དྲྀཥྚིཾ པྲཱཔྣོཥི པཝིཏྲེཎཱཏྨནཱ པརིཔཱུརྞོ བྷཝསི ཙ, ཏདརྠཾ ཏཝཱགམནཀཱལེ ཡཿ པྲབྷུཡཱིཤུསྟུབྷྱཾ དརྴནམ྄ ཨདདཱཏ྄ ས མཱཾ པྲེཥིཏཝཱན྄།
Sa’an nan Ananiyas ya tafi gidan ya kuma shiga ciki. Da ya sa hannuwansa a kan Shawulu, sai ya ce, “Ɗan’uwana Shawulu, Ubangiji, Yesu, wanda ya bayyana gare ka a kan hanya yayinda kake zuwa nan, ya aiko ni domin ka sāke gani a kuma cika ka da Ruhu Mai Tsarki.”
18 ཨིཏྱུཀྟམཱཏྲེ ཏསྱ ཙཀྵུརྦྷྱཱམ྄ མཱིནཤལྐཝད྄ ཝསྟུནི ནིརྒཏེ ཏཏྐྵཎཱཏ྄ ས པྲསནྣཙཀྵུ རྦྷཱུཏྭཱ པྲོཏྠཱཡ མཛྫིཏོ྅བྷཝཏ྄ བྷུཀྟྭཱ པཱིཏྭཱ སབལོབྷཝཙྩ།
Nan da nan, sai wani abu kamar ɓawo ya fāɗo daga idanun Shawulu, ya kuma sāke iya ganin gari. Sai ya tashi aka kuma yi masa baftisma,
19 ཏཏཿ པརཾ ཤཽལཿ ཤིཥྱཻཿ སཧ ཀཏིཔཡདིཝསཱན྄ ཏསྨིན྄ དམྨེཥཀནགརེ སྠིཏྭཱ྅ཝིལམྦཾ
bayan ya ci abinci, sai sāke samun ƙarfi. Shawulu ya yi kwanaki masu yawa tare da almajiran da suke a Damaskus.
20 སཪྻྭབྷཛནབྷཝནཱནི གཏྭཱ ཡཱིཤུརཱིཤྭརསྱ པུཏྲ ཨིམཱཾ ཀཐཱཾ པྲཱཙཱརཡཏ྄།
Nan take ya fara wa’azi cikin majami’u cewa Yesu Ɗan Allah ne.
21 ཏསྨཱཏ྄ སཪྻྭེ ཤྲོཏཱརཤྩམཏྐྲྀཏྱ ཀཐིཏཝནྟོ ཡོ ཡིརཱུཤཱལམྣགར ཨེཏནྣཱམྣཱ པྲཱརྠཡིཏྲྀལོཀཱན྄ ཝིནཱཤིཏཝཱན྄ ཨེཝམ྄ ཨེཏཱདྲྀཤལོཀཱན྄ བདྡྷྭཱ པྲདྷཱནཡཱཛཀནིཀཊཾ ནཡཏཱིཏྱཱཤཡཱ ཨེཏཏྶྠཱནམཔྱཱགཙྪཏ྄ སཨེཝ ཀིམཡཾ ན བྷཝཏི?
Dukan waɗanda suka ji shi suka yi mamaki suka ce, “Ba shi ne mutumin da ya tā-da-na-zaune-tsaye a kan masu kira bisa ga wannan sunan a Urushalima ba? Ba ya zo nan ne don yă kai su a matsayin’yan kurkuku ga manyan firistoci ba?”
22 ཀིནྟུ ཤཽལཿ ཀྲམཤ ཨུཏྶཱཧཝཱན྄ བྷཱུཏྭཱ ཡཱིཤུརཱིཤྭརེཎཱབྷིཥིཀྟོ ཛན ཨེཏསྨིན྄ པྲམཱཎཾ དཏྭཱ དམྨེཥཀ྄-ནིཝཱསིཡིཧཱུདཱིཡལོཀཱན྄ ནིརུཏྟརཱན྄ ཨཀརོཏ྄།
Duk da haka Shawulu ya yi ta ƙara ƙarfi, ya kuma rikitar da Yahudawan da suke zaune a Damaskus, ta wurin tabbatar musu cewa, Yesu shi ne Kiristi.
23 ཨིཏྠཾ བཧུཏིཐེ ཀཱལེ གཏེ ཡིཧཱུདཱིཡལོཀཱསྟཾ ཧནྟུཾ མནྟྲཡཱམཱསུཿ
Bayan kwanaki masu yawa, sai Yahudawa suka haɗa baki su kashe shi,
24 ཀིནྟུ ཤཽལསྟེཥཱམེཏསྱཱ མནྟྲཎཱཡཱ ཝཱརྟྟཱཾ པྲཱཔྟཝཱན྄། ཏེ ཏཾ ཧནྟུཾ ཏུ དིཝཱནིཤཾ གུཔྟཱཿ སནྟོ ནགརསྱ དྭཱརེ྅ཏིཥྛན྄;
amma Shawulu ya sami labarin shirinsu. Dare da rana suka yi fakonsa a ƙofofin birnin don su kashe shi.
25 ཏསྨཱཏ྄ ཤིཥྱཱསྟཾ ནཱིཏྭཱ རཱཏྲཽ པིཊཀེ ནིདྷཱཡ པྲཱཙཱིརེཎཱཝཱརོཧཡན྄།
Amma almajiransa suka ɗauke shi da dare suka saukar da shi a cikin kwando ta taga a katanga.
26 ཏཏཿ པརཾ ཤཽལོ ཡིརཱུཤཱལམཾ གཏྭཱ ཤིཥྱགཎེན སཱརྡྡྷཾ སྠཱཏུམ྄ ཨཻཧཏ྄, ཀིནྟུ སཪྻྭེ ཏསྨཱདབིབྷཡུཿ ས ཤིཥྱ ཨིཏི ཙ ན པྲཏྱཡན྄།
Da ya zo Urushalima, ya yi ƙoƙarin shiga cikin almajiran amma dukansu suka ji tsoronsa, ba su gaskata cewa tabbatacce shi almajiri ba ne.
27 ཨེཏསྨཱད྄ བརྞབྦཱསྟཾ གྲྀཧཱིཏྭཱ པྲེརིཏཱནཱཾ སམཱིཔམཱནཱིཡ མཱརྒམདྷྱེ པྲབྷུཿ ཀཐཾ ཏསྨཻ དརྴནཾ དཏྟཝཱན྄ ཡཱཿ ཀཐཱཤྩ ཀཐིཏཝཱན྄ ས ཙ ཡཐཱཀྵོབྷཿ སན྄ དམྨེཥཀྣགརེ ཡཱིཤོ རྣཱམ པྲཱཙཱརཡཏ྄ ཨེཏཱན྄ སཪྻྭཝྲྀཏྟཱནྟཱན྄ ཏཱན྄ ཛྙཱཔིཏཝཱན྄།
Amma Barnabas ya ɗauke shi ya kawo shi wurin manzanni. Ya gaya musu yadda Shawulu a kan hanyarsa ya ga Ubangiji kuma cewa Ubangiji ya yi magana da shi, da yadda a Damaskus ya yi wa’azi ba tsoro a cikin sunan Yesu.
28 ཏཏཿ ཤཽལསྟཻཿ སཧ ཡིརཱུཤཱལམི ཀཱལཾ ཡཱཔཡན྄ ནིརྦྷཡཾ པྲབྷོ ཪྻཱིཤོ རྣཱམ པྲཱཙཱརཡཏ྄།
Saboda haka Shawulu ya zauna tare da su yana kai da kawowa a sake a cikin Urushalima, yana magana gabagadi a cikin sunan Ubangiji.
29 ཏསྨཱད྄ ཨནྱདེཤཱིཡལོཀཻཿ སཱརྡྡྷཾ ཝིཝཱདསྱོཔསྠིཏཏྭཱཏ྄ ཏེ ཏཾ ཧནྟུམ྄ ཨཙེཥྚནྟ།
Ya yi magana ya kuma yi muhawwara da Yahudawa masu jin Hellenanci, amma suka yi ƙoƙarin kashe shi.
30 ཀིནྟུ བྷྲཱཏྲྀགཎསྟཛྫྙཱཏྭཱ ཏཾ ཀཻསརིཡཱནགརཾ ནཱིཏྭཱ ཏཱརྵནགརཾ པྲེཥིཏཝཱན྄།
Sa’ad da’yan’uwa suka sami labarin wannan, sai suka ɗauke shi zuwa Kaisariya suka aika da shi Tarshish.
31 ཨིཏྠཾ སཏི ཡིཧཱུདིཡཱགཱལཱིལྴོམིརོཎདེཤཱིཡཱཿ སཪྻྭཱ མཎྜལྱོ ཝིཤྲཱམཾ པྲཱཔྟཱསྟཏསྟཱསཱཾ ནིཥྛཱབྷཝཏ྄ པྲབྷོ རྦྷིཡཱ པཝིཏྲསྱཱཏྨནཿ སཱནྟྭནཡཱ ཙ ཀཱལཾ ཀྵེཔཡིཏྭཱ བཧུསཾཁྱཱ ཨབྷཝན྄།
Sa’an nan ikkilisiya ko’ina a Yahudiya, Galili da kuma Samariya ta sami salama. Ta yi ƙarfi; ta kuma ƙarfafa ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ta ƙaru sosai tana rayuwa cikin tsoron Ubangiji.
32 ཏཏཿ པརཾ པིཏརཿ སྠཱནེ སྠཱནེ བྷྲམིཏྭཱ ཤེཥེ ལོདྣགརནིཝཱསིཔཝིཏྲལོཀཱནཱཾ སམཱིཔེ སྠིཏཝཱན྄།
Da Bitrus yake zazzaga ƙasar, sai ya je ya ziyarci tsarkakan da suke a Lidda.
33 ཏདཱ ཏཏྲ པཀྵཱགྷཱཏཝྱཱདྷིནཱཥྚཽ ཝཏྶརཱན྄ ཤཡྻཱགཏམ྄ ཨཻནེཡནཱམཱནཾ མནུཥྱཾ སཱཀྵཏ྄ པྲཱཔྱ ཏམཝདཏ྄,
A can ya tarar da wani mutum mai suna Eniyas, shanyayye wanda yake kwance kan gado shekara takwas.
34 ཧེ ཨཻནེཡ ཡཱིཤུཁྲཱིཥྚསྟྭཱཾ སྭསྠམ྄ ཨཀཱརྵཱིཏ྄, ཏྭམུཏྠཱཡ སྭཤཡྻཱཾ ནིཀྵིཔ, ཨིཏྱུཀྟམཱཏྲེ ས ཨུདཏིཥྛཏ྄།
Sai Bitrus ya ce masa, “Eniyas, Yesu Kiristi ya warkar da kai. Tashi ka naɗe tabarmarka.” Nan da nan Eniyas ya tashi.
35 ཨེཏཱདྲྀཤཾ དྲྀཥྚྭཱ ལོདྴཱརོཎནིཝཱསིནོ ལོཀཱཿ པྲབྷུཾ པྲཏི པརཱཝརྟྟནྟ།
Duk waɗanda suke zama a Lidda da Sharon suka gan shi suka kuma juyo ga Ubangiji.
36 ཨཔརཉྩ བྷིཀྵཱདཱནཱདིཥུ ནཱནཀྲིཡཱསུ ནིཏྱཾ པྲཝྲྀཏྟཱ ཡཱ ཡཱཕོནགརནིཝཱསིནཱི ཊཱབིཐཱནཱམཱ ཤིཥྱཱ ཡཱཾ དརྐྐཱཾ ཨརྠཱད྄ ཧརིཎཱིམཡུཀྟྭཱ ཨཱཧྭཡན྄ སཱ ནཱརཱི
A Yoffa akwai wata almajira mai suna Tabita (a harshen Girik sunanta shi ne Dokas); ita mai aikin alheri ce kullum, tana kuma taimakon matalauta.
37 ཏསྨིན྄ སམཡེ རུགྣཱ སཏཱི པྲཱཎཱན྄ ཨཏྱཛཏ྄, ཏཏོ ལོཀཱསྟཱཾ པྲཀྵཱལྱོཔརིསྠཔྲཀོཥྛེ ཤཱཡཡིཏྭཱསྠཱཔཡན྄།
A lokacin nan ta yi rashin lafiya ta mutu, aka kuma yi wa gawarta wanka aka ajiye a wani ɗaki a gidan sama.
38 ལོདྣགརཾ ཡཱཕོནགརསྱ སམཱིཔསྠཾ ཏསྨཱཏྟཏྲ པིཏར ཨཱསྟེ, ཨིཏི ཝཱརྟྟཱཾ ཤྲུཏྭཱ ཏཱུརྞཾ ཏསྱཱགམནཱརྠཾ ཏསྨིན྄ ཝིནཡམུཀྟྭཱ ཤིཥྱགཎོ དྭཽ མནུཛཽ པྲེཥིཏཝཱན྄།
Lidda yana kusa da Yoffa; saboda haka sa’ad da almajirai suka ji cewa Bitrus yana a Lidda, sai suka aiki mutum biyu wurinsa su roƙe shi cewa, “In ka yarda ka zo nan da nan!”
39 ཏསྨཱཏ྄ པིཏར ཨུཏྠཱཡ ཏཱབྷྱཱཾ སཱརྡྡྷམ྄ ཨཱགཙྪཏ྄, ཏཏྲ ཏསྨིན྄ ཨུཔསྠིཏ ཨུཔརིསྠཔྲཀོཥྛཾ སམཱནཱིཏེ ཙ ཝིདྷཝཱཿ སྭཱབྷིཿ སཧ སྠིཏིཀཱལེ དརྐྐཡཱ ཀྲྀཏཱནི ཡཱནྱུཏྟརཱིཡཱཎི པརིདྷེཡཱནི ཙ ཏཱནི སཪྻྭཱཎི ཏཾ དརྴཡིཏྭཱ རུདཏྱཤྩཏསྲྀཥུ དིཀྵྭཏིཥྛན྄།
Sai Bitrus ya tafi tare da su, sa’ad da ya iso sai aka kai shi ɗakin saman. Duka gwauraye suka tsaya kewaye da shi, suna kuka suna nunnuna masa riguna da kuma waɗansu tufafin da Dokas ta yi yayinda take tare da su.
40 ཀིནྟུ པིཏརསྟཱཿ སཪྻྭཱ བཧིཿ ཀྲྀཏྭཱ ཛཱནུནཱི པཱཏཡིཏྭཱ པྲཱརྠིཏཝཱན྄; པཤྩཱཏ྄ ཤཝཾ པྲཏི དྲྀཥྚིཾ ཀྲྀཏྭཱ ཀཐིཏཝཱན྄, ཧེ ཊཱབཱིཐེ ཏྭམུཏྟིཥྛ, ཨིཏི ཝཱཀྱ ཨུཀྟེ སཱ སྟྲཱི ཙཀྵུཥཱི པྲོནྨཱིལྱ པིཏརམ྄ ཨཝལོཀྱོཏྠཱཡོཔཱཝིཤཏ྄།
Bitrus ya fitar da su duka daga ɗakin; sa’an nan ya durƙusa ya yi addu’a. Da ya juya wajen matacciyar, sai ya ce, “Tabita, tashi.” Ta buɗe idanunta, ta ga Bitrus sai ta tashi zaune.
41 ཏཏཿ པིཏརསྟསྱཱཿ ཀརཽ དྷྲྀཏྭཱ ཨུཏྟོལྱ པཝིཏྲལོཀཱན྄ ཝིདྷཝཱཤྩཱཧཱུཡ ཏེཥཱཾ ནིཀཊེ སཛཱིཝཱཾ ཏཱཾ སམཱརྤཡཏ྄།
Ya kama ta a hannu ya taimake ta ta tsaya a ƙafafunta. Sa’an nan ya kira masu bi da kuma gwaurayen ya miƙa musu ita da rai.
42 ཨེཥཱ ཀཐཱ སམསྟཡཱཕོནགརཾ ཝྱཱཔྟཱ ཏསྨཱད྄ ཨནེཀེ ལོཀཱཿ པྲབྷཽ ཝྱཤྭསན྄།
Wannan ya zama sananne ko’ina a Yoffa, mutane da yawa kuma suka gaskata da Ubangiji.
43 ཨཔརཉྩ པིཏརསྟདྱཱཕོནགརཱིཡསྱ ཀསྱཙིཏ྄ ཤིམོནྣཱམྣཤྩརྨྨཀཱརསྱ གྲྀཧེ བཧུདིནཱནི ནྱཝསཏ྄།
Bitrus ya zauna a Yoffa na ɗan lokaci tare da wani mai aikin fatu mai suna Siman.

< པྲེརིཏཱཿ 9 >