< mArkaH 1 >

1 Ishvaraputrasya yIshukhrIShTasya susaMvAdArambhaH|
Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah.
2 bhaviShyadvAdinAM grantheShu lipiritthamAste, pashya svakIyadUtantu tavAgre preShayAmyaham| gatvA tvadIyapanthAnaM sa hi pariShkariShyati|
kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya.
3 "parameshasya panthAnaM pariShkuruta sarvvataH| tasya rAjapatha nchaiva samAnaM kurutAdhunA|" ityetat prAntare vAkyaM vadataH kasyachidravaH||
Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.
4 saeva yohan prAntare majjitavAn tathA pApamArjananimittaM manovyAvarttakamajjanasya kathA ncha prachAritavAn|
Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai.
5 tato yihUdAdeshayirUshAlamnagaranivAsinaH sarvve lokA bahi rbhUtvA tasya samIpamAgatya svAni svAni pApAnya NgIkR^itya yarddananadyAM tena majjitA babhUvuH|
Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu.
6 asya yohanaH paridheyAni kramelakalomajAni, tasya kaTibandhanaM charmmajAtam, tasya bhakShyANi cha shUkakITA vanyamadhUni chAsan|
Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.
7 sa prachArayan kathayA nchakre, ahaM namrIbhUya yasya pAdukAbandhanaM mochayitumapi na yogyosmi, tAdR^isho matto gurutara ekaH puruSho matpashchAdAgachChati|
Yana wa'azi, ya ce “akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba.
8 ahaM yuShmAn jale majjitavAn kintu sa pavitra AtmAni saMmajjayiShyati|
Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki''.
9 apara ncha tasminneva kAle gAlIlpradeshasya nAsaradgrAmAd yIshurAgatya yohanA yarddananadyAM majjito. abhUt|
Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun.
10 sa jalAdutthitamAtro meghadvAraM muktaM kapotavat svasyopari avarohantamAtmAna ncha dR^iShTavAn|
Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya.
11 tvaM mama priyaH putrastvayyeva mamamahAsantoSha iyamAkAshIyA vANI babhUva|
Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, “Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai''.
12 tasmin kAle AtmA taM prAntaramadhyaM ninAya|
Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji.
13 atha sa chatvAriMshaddinAni tasmin sthAne vanyapashubhiH saha tiShThan shaitAnA parIkShitaH; pashchAt svargIyadUtAstaM siShevire|
Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.
14 anantaraM yohani bandhanAlaye baddhe sati yIshu rgAlIlpradeshamAgatya IshvararAjyasya susaMvAdaM prachArayan kathayAmAsa,
Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah.
15 kAlaH sampUrNa IshvararAjya ncha samIpamAgataM; atoheto ryUyaM manAMsi vyAvarttayadhvaM susaMvAde cha vishvAsita|
Yana cewa, “Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara”.
16 tadanantaraM sa gAlIlIyasamudrasya tIre gachChan shimon tasya bhrAtA andriyanAmA cha imau dvau janau matsyadhAriNau sAgaramadhye jAlaM prakShipantau dR^iShTvA tAvavadat,
Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
17 yuvAM mama pashchAdAgachChataM, yuvAmahaM manuShyadhAriNau kariShyAmi|
Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane”.
18 tatastau tatkShaNameva jAlAni parityajya tasya pashchAt jagmatuH|
Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.
19 tataH paraM tatsthAnAt ki nchid dUraM gatvA sa sivadIputrayAkUb tadbhrAtR^iyohan cha imau naukAyAM jAlAnAM jIrNamuddhArayantau dR^iShTvA tAvAhUyat|
Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa.
20 tatastau naukAyAM vetanabhugbhiH sahitaM svapitaraM vihAya tatpashchAdIyatuH|
Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.
21 tataH paraM kapharnAhUmnAmakaM nagaramupasthAya sa vishrAmadivase bhajanagrahaM pravishya samupadidesha|
Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu.
22 tasyopadeshAllokA AshcharyyaM menire yataH sodhyApakAiva nopadishan prabhAvavAniva propadidesha|
Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.
23 apara ncha tasmin bhajanagR^ihe apavitrabhUtena grasta eko mAnuSha AsIt| sa chItshabdaM kR^itvA kathayA nchake
A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi.
24 bho nAsaratIya yIsho tvamasmAn tyaja, tvayA sahAsmAkaM kaH sambandhaH? tvaM kimasmAn nAshayituM samAgataH? tvamIshvarasya pavitraloka ityahaM jAnAmi|
Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah”.
25 tadA yIshustaM tarjayitvA jagAda tUShNIM bhava ito bahirbhava cha|
Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, “Ka yi shiru ka fita daga cikinsa”.
26 tataH so. apavitrabhUtastaM sampIDya atyuchaishchItkR^itya nirjagAma|
Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.
27 tenaiva sarvve chamatkR^itya parasparaM kathayA nchakrire, aho kimidaM? kIdR^isho. ayaM navya upadeshaH? anena prabhAvenApavitrabhUteShvAj nApiteShu te tadAj nAnuvarttino bhavanti|
Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!”
28 tadA tasya yasho gAlIlashchaturdiksthasarvvadeshAn vyApnot|
Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.
29 apara ncha te bhajanagR^ihAd bahi rbhUtvA yAkUbyohanbhyAM saha shimona Andriyasya cha niveshanaM pravivishuH|
Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya.
30 tadA pitarasya shvashrUrjvarapIDitA shayyAyAmAsta iti te taM jhaTiti vij nApayA nchakruH|
Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 tataH sa Agatya tasyA hastaM dhR^itvA tAmudasthApayat; tadaiva tAM jvaro. atyAkShIt tataH paraM sA tAn siSheve|
Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.
32 athAstaM gate ravau sandhyAkAle sati lokAstatsamIpaM sarvvAn rogiNo bhUtadhR^itAMshcha samAninyuH|
Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu.
33 sarvve nAgarikA lokA dvAri saMmilitAshcha|
Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa.
34 tataH sa nAnAvidharogiNo bahUn manujAnarogiNashchakAra tathA bahUn bhUtAn tyAjayA nchakAra tAn bhUtAn kimapi vAkyaM vaktuM niShiShedha cha yatohetoste tamajAnan|
ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.
35 apara ncha so. atipratyUShe vastutastu rAtrisheShe samutthAya bahirbhUya nirjanaM sthAnaM gatvA tatra prArthayA nchakre|
Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua.
36 anantaraM shimon tatsa Nginashcha tasya pashchAd gatavantaH|
Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi.
37 taduddeshaM prApya tamavadan sarvve lokAstvAM mR^igayante|
Suka sa me shi, sai su ka ce masa, “kowa yana nemanka”.
38 tadA so. akathayat AgachChata vayaM samIpasthAni nagarANi yAmaH, yato. ahaM tatra kathAM prachArayituM bahirAgamam|
Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan''.
39 atha sa teShAM gAlIlpradeshasya sarvveShu bhajanagR^iheShu kathAH prachArayA nchakre bhUtAnatyAjaya ncha|
Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.
40 anantaramekaH kuShThI samAgatya tatsammukhe jAnupAtaM vinaya ncha kR^itvA kathitavAn yadi bhavAn ichChati tarhi mAM pariShkarttuM shaknoti|
Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, “in ka yarda kana iya warkar da ni.
41 tataH kR^ipAlu ryIshuH karau prasAryya taM spaShTvA kathayAmAsa
Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa “Na yarda. Ka sarkaka”.
42 mamechChA vidyate tvaM pariShkR^ito bhava| etatkathAyAH kathanamAtrAt sa kuShThI rogAnmuktaH pariShkR^ito. abhavat|
Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.
43 tadA sa taM visR^ijan gADhamAdishya jagAda
Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi.
44 sAvadhAno bhava kathAmimAM kamapi mA vada; svAtmAnaM yAjakaM darshaya, lokebhyaH svapariShkR^iteH pramANadAnAya mUsAnirNItaM yaddAnaM tadutsR^ijasva cha|
Ya ce masa “ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.
45 kintu sa gatvA tat karmma itthaM vistAryya prachArayituM prArebhe tenaiva yIshuH punaH saprakAshaM nagaraM praveShTuM nAshaknot tatohetorbahiH kAnanasthAne tasyau; tathApi chaturddigbhyo lokAstasya samIpamAyayuH|
Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.

< mArkaH 1 >