< 2 tImathiyaH 3 >
1 charamadineShu kleshajanakAH samayA upasthAsyantIti jAnIhi|
Amma fa ka san wannan, za a yi lokutan shan wahala a kwanakin ƙarshe.
2 yatastAtkAlikA lokA AtmapremiNo. arthapremiNa AtmashlAghino. abhimAnino nindakAH pitroranAj nAgrAhiNaH kR^itaghnA apavitrAH
Mutane za su zama masu son kansu, masu son kuɗi, masu taƙama, masu girman kai, masu zage-zage, marasa biyayya ga iyayensu, marasa godiya, marasa tsarki,
3 prItivarjitA asandheyA mR^iShApavAdino. ajitendriyAH prachaNDA bhadradveShiNo
marasa ƙauna, marasa gafartawa, masu ɓata sunayen waɗansu, marasa kamunkai, masu ƙeta, marasa ƙaunar nagarta,
4 vishvAsaghAtakA duHsAhasino darpadhmAtA IshvarApremiNaH kintu sukhapremiNo
masu cin amana, marasa hankali, waɗanda sun cika da ɗaga kai, masu son jin daɗi a maimakon ƙaunar Allah
5 bhaktaveshAH kintvasvIkR^itabhaktiguNA bhaviShyanti; etAdR^ishAnAM lokAnAM saMmargaM parityaja|
suna riƙe da siffofin ibada, amma suna mūsun ikonta. Kada wani abu yă haɗa ka da su.
6 yato ye janAH prachChannaM gehAn pravishanti pApai rbhAragrastA nAnAvidhAbhilAShaishchAlitA yAH kAminyo
Irin su ne suke saɗaɗawa su shiga gidaje suna rinjayar mata marasa ƙarfin hali, waɗanda zunubai suka sha kansu, mugayen sha’awace-sha’awace kuma sun ɗauke hankulansu,
7 nityaM shikShante kintu satyamatasya tattvaj nAnaM prAptuM kadAchit na shaknuvanti tA dAsIvad vashIkurvvate cha te tAdR^ishA lokAH|
kullum suna koyo amma ba sa taɓa iya yarda da gaskiya.
8 yAnni ryAmbrishcha yathA mUsamaM prati vipakShatvam akurutAM tathaiva bhraShTamanaso vishvAsaviShaye. agrAhyAshchaite lokA api satyamataM prati vipakShatAM kurvvanti|
Kamar dai yadda Yannes da Yamberes suka tayar wa Musa, haka waɗannan mutane ma suke tayar wa gaskiya, mutane masu ɓataccen hankali, waɗanda, in ana zancen bangaskiya ne, to, fa ba sa ciki.
9 kintu te bahudUram agrasarA na bhaviShyanti yatastayo rmUDhatA yadvat tadvad eteShAmapi mUDhatA sarvvadR^ishyA bhaviShyati|
Sai dai ba za su yi nisa ba, don rashin hankalinsu zai bayyana ga kowa, kamar na mutanen nan biyu.
10 mamopadeshaH shiShTatAbhiprAyo vishvAso rdharyyaM prema sahiShNutopadravaH kleshA
Kai kam, ka san kome game da koyarwata, da halina, da niyyata, bangaskiya, haƙuri, ƙauna, jimiri,
11 AntiyakhiyAyAm ikaniye lUstrAyA ncha mAM prati yadyad aghaTata yAMshchopadravAn aham asahe sarvvametat tvam avagato. asi kintu tatsarvvataH prabhu rmAm uddhR^itavAn|
tsanani, shan wahala, irin abubuwan da suka faru da ni a Antiyok, Ikoniyum da kuma Listira, tsananin da na jure. Duk da haka Ubangiji ya cece ni daga dukansu.
12 parantu yAvanto lokAH khrIShTena yIshuneshvarabhaktim Acharitum ichChanti teShAM sarvveShAm upadravo bhaviShyati|
Labudda, duk masu niyyar zaman tsarkaka, suna na Kiristi Yesu, za su sha tsanani.
13 aparaM pApiShThAH khalAshcha lokA bhrAmyanto bhramayantashchottarottaraM duShTatvena varddhiShyante|
Mugayen mutane da masu ruɗi kuwa, ƙara muni za su riƙa yi, suna yaudara, ana kuma yaudararsu.
14 kintu tvaM yad yad ashikShathAH, yachcha tvayi samarpitam abhUt tasmin avatiShTha, yataH kasmAt shikShAM prApto. asi tad vetsi;
Amma kai kam, ka ci gaba da abin da ka koya ka kuma tabbatar, gama ka san waɗanda ka koye su daga gare su,
15 yAni cha dharmmashAstrANi khrIShTe yIshau vishvAsena paritrANaprAptaye tvAM j nAninaM karttuM shaknuvanti tAni tvaM shaishavakAlAd avagato. asi|
da kuma yadda tun kana ɗan jinjiri ka san Nassosi masu tsarki, waɗanda suke iya sa ka zama mai hikima zuwa ceto ta wurin bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
16 tat sarvvaM shAstram IshvarasyAtmanA dattaM shikShAyai doShabodhAya shodhanAya dharmmavinayAya cha phalayUktaM bhavati
Dukan Nassi numfashin Allah ne yana kuma da amfani don koyarwa, tsawatarwa, gyara da kuma horarwa cikin adalci,
17 tena cheshvarasya loko nipuNaH sarvvasmai satkarmmaNe susajjashcha bhavati|
domin mutumin Allah yă zama shiryayye sosai saboda kowane kyakkyawan aiki.