< romiṇaḥ 7 >
1 he bhrātṛgaṇa vyavasthāvidaḥ prati mamedaṁ nivedanaṁ| vidhiḥ kevalaṁ yāvajjīvaṁ mānavoparyyadhipatitvaṁ karotīti yūyaṁ kiṁ na jānītha?
Ba ku sani ba,’yan’uwa, ina magana ne fa da mutanen da suka san doka, cewa dokar tana da iko a kan mutum muddin yana a raye ne kawai.
2 yāvatkālaṁ pati rjīvati tāvatkālam ūḍhā bhāryyā vyavasthayā tasmin baddhā tiṣṭhati kintu yadi pati rmriyate tarhi sā nārī patyu rvyavasthāto mucyate|
Misali, bisa ga doka mace mai aure tana daure ga mijinta muddin mijin yana da rai, amma in mijinta ya mutu, an sake ta ke nan daga dokar aure.
3 etatkāraṇāt patyurjīvanakāle nārī yadyanyaṁ puruṣaṁ vivahati tarhi sā vyabhicāriṇī bhavati kintu yadi sa pati rmriyate tarhi sā tasyā vyavasthāyā muktā satī puruṣāntareṇa vyūḍhāpi vyabhicāriṇī na bhavati|
Saboda haka fa, in ta auri wani yayinda mijinta yana raye, za a ce da ita mazinaciya. Amma in mijinta ya mutu, an sake ta ke nan daga wannan doka, ita kuwa ba mazinaciya ba ce, ko da yake ta auri wani.
4 he mama bhrātṛgaṇa, īśvaranimittaṁ yadasmākaṁ phalaṁ jāyate tadarthaṁ śmaśānād utthāpitena puruṣeṇa saha yuṣmākaṁ vivāho yad bhavet tadarthaṁ khrīṣṭasya śarīreṇa yūyaṁ vyavasthāṁ prati mṛtavantaḥ|
Saboda haka’yan’uwana, ku ma kun mutu ga dokar ta wurin jikin Kiristi, domin ku zama na wani, gare shi wanda aka tashe shi daga matattu, don mu ba da amfani ga Allah.
5 yato'smākaṁ śārīrikācaraṇasamaye maraṇanimittaṁ phalam utpādayituṁ vyavasthayā dūṣitaḥ pāpābhilāṣo'smākam aṅgeṣu jīvan āsīt|
Gama sa’ad da halin mutuntaka yake mulkinmu, sha’awace-sha’awacen zunubi waɗanda dokar ta zuga sun yi ta aiki a jikunanmu, don mu ba da amfani wa mutuwa.
6 kintu tadā yasyā vyavasthāyā vaśe āsmahi sāmprataṁ tāṁ prati mṛtatvād vayaṁ tasyā adhīnatvāt muktā iti hetorīśvaro'smābhiḥ purātanalikhitānusārāt na sevitavyaḥ kintu navīnasvabhāvenaiva sevitavyaḥ
Amma yanzu, ta wurin mutuwa ga abin da dā ya daure mu, an sake mu daga dokar saboda mu yi hidima a sabuwar hanyar Ruhu, ba a tsohuwar hanyar rubutaccen ƙa’ida ba.
7 tarhi vayaṁ kiṁ brūmaḥ? vyavasthā kiṁ pāpajanikā bhavati? netthaṁ bhavatu| vyavasthām avidyamānāyāṁ pāpaṁ kim ityahaṁ nāvedaṁ; kiñca lobhaṁ mā kārṣīriti ced vyavasthāgranthe likhitaṁ nābhaviṣyat tarhi lobhaḥ kimbhūtastadahaṁ nājñāsyaṁ|
Me za mu ce ke nan? Dokar zunubi ce? Sam, ko kaɗan! Tabbatacce ai, da ban san mene ne zunubi ba in ba ta wurin doka ba. Gama da ban san mene ne ƙyashi yake ba tabbatacce in ba don doka ta ce, “Kada ka yi ƙyashi ba.”
8 kintu vyavasthayā pāpaṁ chidraṁ prāpyāsmākam antaḥ sarvvavidhaṁ kutsitābhilāṣam ajanayat; yato vyavasthāyām avidyamānāyāṁ pāpaṁ mṛtaṁ|
Amma zunubi, da ya sami dama ta wurin umarnin nan, ya haifar a cikina kowane halin ƙyashi iri-iri. Gama in babu doka, zunubi matacce ne.
9 aparaṁ pūrvvaṁ vyavasthāyām avidyamānāyām aham ajīvaṁ tataḥ param ājñāyām upasthitāyām pāpam ajīvat tadāham amriye|
Dā kam ina da rai sa’ad da ban san doka ba; amma da umarni ya zo, sai zunubi ya zaburo da rai na kuma mutu.
10 itthaṁ sati jīvananimittā yājñā sā mama mṛtyujanikābhavat|
Na gane cewa wannan umarnin da aka nufa ya kawo rai, a gaskiya ya jawo mutuwa ce.
11 yataḥ pāpaṁ chidraṁ prāpya vyavasthitādeśena māṁ vañcayitvā tena mām ahan|
Gama zunubi, da ya sami dama ta wurin umarni, sai ya ruɗe ni, kuma ta wurin umarnin kuwa ya kashe ni.
12 ataeva vyavasthā pavitrā, ādeśaśca pavitro nyāyyo hitakārī ca bhavati|
Saboda haka fa, dokar tana da tsarki, umarnin kuma yana da tsarki, su duka suna da adalci da kuma kyau.
13 tarhi yat svayaṁ hitakṛt tat kiṁ mama mṛtyujanakam abhavat? netthaṁ bhavatu; kintu pāpaṁ yat pātakamiva prakāśate tathā nideśena pāpaṁ yadatīva pātakamiva prakāśate tadarthaṁ hitopāyena mama maraṇam ajanayat|
Abin nan da yana mai kyau, zai kawo mini mutuwa? Ko kaɗan! Amma domin zunubi ya bayyana kansa a matsayin zunubi, sai ya haifar da mutuwa a cikina ta wurin abin da yake mai kyau, domin ta wurin umarnin nan zunubi ya fito da matuƙar muninsa.
14 vyavasthātmabodhiketi vayaṁ jānīmaḥ kintvahaṁ śārīratācārī pāpasya krītakiṅkaro vidye|
Mun san cewa doka aba ce ta ruhu; amma ni ba na ruhu ba ne, an sayar da ni a matsayin bawa ga zunubi.
15 yato yat karmma karomi tat mama mano'bhimataṁ nahi; aparaṁ yan mama mano'bhimataṁ tanna karomi kintu yad ṛtīye tat karomi|
Ban gane abin da nake yi ba. Don abin da nakan so yi, ba shi nakan yi ba, sai dai abin da nake ƙi, shi nake yi.
16 tathātve yan mamānabhimataṁ tad yadi karomi tarhi vyavasthā sūttameti svīkaromi|
In kuma na yi abin da ba na son yi, na yarda da cewa dokar aba ce mai kyau.
17 ataeva samprati tat karmma mayā kriyata iti nahi kintu mama śarīrasthena pāpenaiva kriyate|
Kamar dai yadda yake, ba ni kaina nake yinsa ba, sai dai zunubin da yake zaune a cikina ne.
18 yato mayi, arthato mama śarīre, kimapyuttamaṁ na vasati, etad ahaṁ jānāmi; mamecchukatāyāṁ tiṣṭhantyāmapyaham uttamakarmmasādhane samartho na bhavāmi|
Gama na san cewa babu wani abin kirkin da yake zaune a cikina, wato, a mutuntakata. Gama sha’awar yin abu mai kyau kam ina da ita, sai dai ikon yin ne fa babu.
19 yato yāmuttamāṁ kriyāṁ karttumahaṁ vāñchāmi tāṁ na karomi kintu yat kutsitaṁ karmma karttum anicchuko'smi tadeva karomi|
Gama abin da nake yi ba shi ne abu mai kyau da nake so in yi ba; a’a, mugun da ba na so in yi, shi ne nake ci gaba da yi.
20 ataeva yadyat karmma karttuṁ mamecchā na bhavati tad yadi karomi tarhi tat mayā na kriyate, mamāntarvarttinā pāpenaiva kriyate|
To, in na yi abin da ba na so in yi, ba ni ba ne nake yinsa, sai dai zunubin nan da yake zaune a cikina.
21 bhadraṁ karttum icchukaṁ māṁ yo 'bhadraṁ karttuṁ pravarttayati tādṛśaṁ svabhāvamekaṁ mayi paśyāmi|
Saboda haka na gane wannan ƙa’ida ce take aiki a cikina. Sa’ad da nake so in yi abu mai kyau, sai in ga cewa mugun nan ne nake yi.
22 aham āntarikapuruṣeṇeśvaravyavasthāyāṁ santuṣṭa āse;
Gama a ciki-cikina ina farin cikin da dokar Allah;
23 kintu tadviparītaṁ yudhyantaṁ tadanyamekaṁ svabhāvaṁ madīyāṅgasthitaṁ prapaśyāmi, sa madīyāṅgasthitapāpasvabhāvasyāyattaṁ māṁ karttuṁ ceṣṭate|
amma ina ganin wata doka tana aiki a gaɓoɓin jikina, tana yaƙi da dokar hankalina, tana kuma sa in zama ɗaurarren dokar zunubin da take aiki a gaɓoɓin jikina.
24 hā hā yo'haṁ durbhāgyo manujastaṁ mām etasmān mṛtāccharīrāt ko nistārayiṣyati?
Kaitona! Wane ne zai cece ni daga wannan jiki mai mutuwa?
25 asmākaṁ prabhuṇā yīśukhrīṣṭena nistārayitāram īśvaraṁ dhanyaṁ vadāmi| ataeva śarīreṇa pāpavyavasthāyā manasā tu īśvaravyavasthāyāḥ sevanaṁ karomi|
Godiya ga Allah ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu! Saboda haka fa, ni kaina a cikin hankalina, ni bawa ne ga dokar Allah, amma a mutuntaka, ni bawa ne ga dokar zunubi.