< romiṇaḥ 3 >
1 aparañca yihūdinaḥ kiṁ śreṣṭhatvaṁ? tathā tvakchedasya vā kiṁ phalaṁ?
To, mece ce ribar zama mutumin Yahuda, ko kuwa mene ne amfanin kaciya?
2 sarvvathā bahūni phalāni santi, viśeṣata īśvarasya śāstraṁ tebhyo'dīyata|
Akwai riba ƙwarai ta kowace hanya! Da farko dai, su ne aka danƙa wa kalmomin nan na Allah.
3 kaiścid aviśvasane kṛte teṣām aviśvasanāt kim īśvarasya viśvāsyatāyā hānirutpatsyate?
Amma a ce waɗansu ba su da bangaskiya fa? Rashin bangaskiyarsu nan zai shafe amincin Allah?
4 kenāpi prakāreṇa nahi| yadyapi sarvve manuṣyā mithyāvādinastathāpīśvaraḥ satyavādī| śāstre yathā likhitamāste, atastvantu svavākyena nirddoṣo hi bhaviṣyasi| vicāre caiva niṣpāpo bhaviṣyasi na saṁśayaḥ|
Ko kaɗan! Bari Allah yă zama mai gaskiya, kowane mutum kuma yă zama maƙaryaci. Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Gama a tabbatar kana da gaskiya, sa’ad da ka yi magana, ka kuma yi nasara sa’ad da ka yi shari’a.”
5 asmākam anyāyena yadīśvarasya nyāyaḥ prakāśate tarhi kiṁ vadiṣyāmaḥ? ahaṁ mānuṣāṇāṁ kathāmiva kathāṁ kathayāmi, īśvaraḥ samucitaṁ daṇḍaṁ dattvā kim anyāyī bhaviṣyati?
Amma in rashin adalcinmu ya bayyana adalcin Allah a fili, me za mu ce ke nan? Za mu ce Allah ya yi rashin adalci ke nan da ya saukar da fushinsa a kanmu? (Ina magana kamar yadda mutum zai yi ne.)
6 itthaṁ na bhavatu, tathā satīśvaraḥ kathaṁ jagato vicārayitā bhaviṣyati?
Sam, ko kusa! Da a ce haka ne, ta yaya Allah zai shari’anta duniya?
7 mama mithyāvākyavadanād yadīśvarasya satyatvena tasya mahimā varddhate tarhi kasmādahaṁ vicāre'parādhitvena gaṇyo bhavāmi?
Wani zai iya ce, “In a dalilin ƙaryata, gaskiyar Allah ta ƙara bayyana, har aka ƙara ɗaukaka shi, to, ta yaya zan zama mai zunubi, in ƙaryata tana kawo ɗaukaka ga Allah?”
8 maṅgalārthaṁ pāpamapi karaṇīyamiti vākyaṁ tvayā kuto nocyate? kintu yairucyate te nitāntaṁ daṇḍasya pātrāṇi bhavanti; tathāpi tadvākyam asmābhirapyucyata ityasmākaṁ glāniṁ kurvvantaḥ kiyanto lokā vadanti|
In haka ne, “Ba sai mu yi ta yin mugunta don yă zama hanyar samun nagarta ba”? Kamar yadda masu baƙar magana game da mu suna cewa wai haka muke faɗa. Tabbatacce za a hukunta irin waɗannan da hukuncin da ya dace da su.
9 anyalokebhyo vayaṁ kiṁ śreṣṭhāḥ? kadācana nahi yato yihūdino 'nyadeśinaśca sarvvaeva pāpasyāyattā ityasya pramāṇaṁ vayaṁ pūrvvam adadāma|
To, me za mu ce ke nan? Mun fi su ke nan? Ina, ko kaɗan! Mun riga mun zartar cewa da Yahudawa da Al’ummai duk suna a ƙarƙarshin zunubi.
10 lipi ryathāste, naikopi dhārmmiko janaḥ|
Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Babu wani mai adalci, babu ko ɗaya;
11 tathā jñānīśvarajñānī mānavaḥ kopi nāsti hi|
babu wani mai fahimta, babu wani mai neman Allah.
12 vimārgagāminaḥ sarvve sarvve duṣkarmmakāriṇaḥ| eko janopi no teṣāṁ sādhukarmma karoti ca|
Duk sun kauce gaba ɗaya, sun zama marasa amfani; babu wani mai aikata nagarta, babu ko ɗaya.”
13 tathā teṣāntu vai kaṇṭhā anāvṛtaśmaśānavat| stutivādaṁ prakurvvanti jihvābhiste tu kevalaṁ| teṣāmoṣṭhasya nimne tu viṣaṁ tiṣṭhati sarppavat|
“Maƙogwaronsu kamar buɗaɗɗun kaburbura ne, harsunansu suna yin ƙarya.” “Dafin mugun maciji yana a leɓunansu.”
14 mukhaṁ teṣāṁ hi śāpena kapaṭena ca pūryyate|
“Bakunansu sun cike da la’ana da ɗacin rai.”
15 raktapātāya teṣāṁ tu padāni kṣipragāni ca|
“Ƙafafunsu suna saurin kai su zuwa ga zub da jini;
16 pathi teṣāṁ manuṣyāṇāṁ nāśaḥ kleśaśca kevalaḥ|
hallaka da baƙin ciki suna ko’ina a hanyoyinsu,
17 te janā nahi jānanti panthānaṁ sukhadāyinaṁ|
ba su kuma san hanyar salama ba.”
18 parameśād bhayaṁ yattat taccakṣuṣoragocaraṁ|
“Babu tsoron Allah a idanunsu.”
19 vyavasthāyāṁ yadyallikhati tad vyavasthādhīnān lokān uddiśya likhatīti vayaṁ jānīmaḥ| tato manuṣyamātro niruttaraḥ san īśvarasya sākṣād aparādhī bhavati|
Yanzu mun san cewa dukan abin da doka ta ce, tana magana ne ga waɗanda suke ƙarƙarshin doka, saboda a rufe kowane baki; dukan duniya kuma ta ba da lissafin kanta a gaban Allah.
20 ataeva vyavasthānurūpaiḥ karmmabhiḥ kaścidapi prāṇīśvarasya sākṣāt sapuṇyīkṛto bhavituṁ na śakṣyati yato vyavasthayā pāpajñānamātraṁ jāyate|
Saboda haka babu wanda Allah zai ce da shi mai adalci ta wurin kiyaye doka kawai; a maimako, ta wurin doka ne muke sane da zunubi.
21 kintu vyavasthāyāḥ pṛthag īśvareṇa deyaṁ yat puṇyaṁ tad vyavasthāyā bhaviṣyadvādigaṇasya ca vacanaiḥ pramāṇīkṛtaṁ sad idānīṁ prakāśate|
Amma yanzu an bayyana wani adalci daga Allah, wannan adalcin bai danganta ga doka ba, Doka da Annabawa suna ba da shaida game da wannan adalci.
22 yīśukhrīṣṭe viśvāsakaraṇād īśvareṇa dattaṁ tat puṇyaṁ sakaleṣu prakāśitaṁ sat sarvvān viśvāsinaḥ prati varttate|
Wannan adalcin Allah yana zuwa ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi ga dukan waɗanda suka ba da gaskiya ne. Ba bambanci,
23 teṣāṁ kopi prabhedo nāsti, yataḥ sarvvaeva pāpina īśvarīyatejohīnāśca jātāḥ|
gama duka sun yi zunubi suka kuma kāsa ga ɗaukakar Allah,
24 ta īśvarasyānugrahād mūlyaṁ vinā khrīṣṭakṛtena paritrāṇena sapuṇyīkṛtā bhavanti|
an kuma kuɓutar da su kyauta ta wurin alherinsa bisa ga aikin fansar da ya zo ta wurin Yesu Kiristi.
25 yasmāt svaśoṇitena viśvāsāt pāpanāśako balī bhavituṁ sa eva pūrvvam īśvareṇa niścitaḥ, ittham īśvarīyasahiṣṇutvāt purākṛtapāpānāṁ mārjjanakaraṇe svīyayāthārthyaṁ tena prakāśyate,
Allah ya miƙa Yesu Kiristi a matsayin hadayar kafara, ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya yi haka domin yă nuna adalcinsa, domin a cikin haƙurinsa bai hukunta zunuban da aka aikata a dā ba
26 varttamānakālīyamapi svayāthārthyaṁ tena prakāśyate, aparaṁ yīśau viśvāsinaṁ sapuṇyīkurvvannapi sa yāthārthikastiṣṭhati|
ya yi haka domin yă nuna adalcinsa a wannan lokaci, saboda yă zama mai adalci da mai kuɓutar da waɗanda suke ba da gaskiya a cikin Yesu.
27 tarhi kutrātmaślāghā? sā dūrīkṛtā; kayā vyavasthayā? kiṁ kriyārūpavyavasthayā? itthaṁ nahi kintu tat kevalaviśvāsarūpayā vyavasthayaiva bhavati|
To, me za mu yi taƙama a kai? Babu wani abin da zamu yi taƙama a kai. A kan wace ƙa’ida ce za mu yi taƙama? Ta hanyar bin doka ne? A’a, sai dai ta wurin bangaskiya.
28 ataeva vyavasthānurūpāḥ kriyā vinā kevalena viśvāsena mānavaḥ sapuṇyīkṛto bhavituṁ śaknotītyasya rāddhāntaṁ darśayāmaḥ|
Gama mun tsaya a kan cewa ta wurin bangaskiya ne ake kuɓutar da mutum, ba ta wurin kiyaye doka ba.
29 sa kiṁ kevalayihūdinām īśvaro bhavati? bhinnadeśinām īśvaro na bhavati? bhinnadeśināmapi bhavati;
Allah ɗin, Allahn Yahudawa ne kaɗai? Shi ba Allahn Al’ummai ba ne? I, shi Allahn Al’ummai ne ma,
30 yasmād eka īśvaro viśvāsāt tvakchedino viśvāsenātvakchedinaśca sapuṇyīkariṣyati|
da yake Allah ɗaya ne kaɗai, shi kuma zai kuɓutar da masu kaciya bisa ga bangaskiya da kuma marasa kaciya ta wurin wannan bangaskiya ɗin.
31 tarhi viśvāsena vayaṁ kiṁ vyavasthāṁ lumpāma? itthaṁ na bhavatu vayaṁ vyavasthāṁ saṁsthāpayāma eva|
To, za mu soke dokar saboda wannan bangaskiyar ne? Ko kaɗan! A maimako, sai ma tabbatar da ita muke yi.